< Ƙidaya 25 >
1 Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
Israël resta à Shittim, et le peuple commença à se prostituer avec les filles de Moab;
2 waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
car elles appelaient le peuple aux sacrifices de leurs dieux. Le peuple mangeait et se prosternait devant leurs dieux.
3 Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
Israël s'attacha à Baal Péor, et la colère de Yahvé s'enflamma contre Israël.
4 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
L'Éternel dit à Moïse: « Prends tous les chefs du peuple et suspends-les à l'Éternel devant le soleil, afin que l'ardente colère de l'Éternel se détourne d'Israël. »
5 Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
Moïse dit aux juges d'Israël: « Que chacun tue ses hommes qui se sont attachés à Baal Peor. »
6 Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
Voici, un des enfants d'Israël vint et amena à ses frères une femme madianite, sous les yeux de Moïse et de toute l'assemblée des enfants d'Israël, pendant qu'ils pleuraient à l'entrée de la tente d'assignation.
7 Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
Lorsque Phinées, fils d'Éléazar, fils du sacrificateur Aaron, vit cela, il se leva du milieu de l'assemblée et prit une lance dans sa main.
8 ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
Il poursuivit l'homme d'Israël dans le pavillon, et les transperça tous les deux, l'homme d'Israël et la femme par le corps. Et la peste s'arrêta parmi les enfants d'Israël.
9 Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
Ceux qui moururent de la peste furent vingt-quatre mille.
10 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahvé parla à Moïse, et dit:
11 “Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
« Phinées, fils d'Eléazar, fils du prêtre Aaron, a détourné ma colère des enfants d'Israël, en ce qu'il était jaloux de ma jalousie au milieu d'eux, afin que je ne consume pas les enfants d'Israël dans ma jalousie.
12 Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
C'est pourquoi tu diras: « Voici, je lui donne mon alliance de paix.
13 Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
Ce sera pour lui, et pour sa postérité après lui, l'alliance d'un sacerdoce éternel, parce qu'il a été jaloux de son Dieu et qu'il a fait l'expiation pour les enfants d'Israël.'"
14 Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
Or le nom de l'homme d'Israël qui fut tué avec la femme madianite était Zimri, fils de Salu, prince d'une maison paternelle parmi les Siméonites.
15 Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
Le nom de la femme madianite qui fut tuée était Cozbi, fille de Tsur. Il était chef du peuple d'une maison paternelle en Madian.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahvé parla à Moïse, et dit:
17 “Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
« Poursuis les Madianites, et frappe-les;
18 gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”
car ils t'ont poursuivi par leurs ruses, et ils t'ont trompé dans l'affaire de Péor, et dans l'affaire de Cozbi, fille du prince de Madian, leur sœur, qui fut tuée le jour de la peste dans l'affaire de Péor. »