< Ƙidaya 25 >

1 Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
While the Israelis were camped at a place called Acacia [Grove], some of the men caused themselves to become unacceptable to God by having sex with some of the women of the Moab [people-group who lived in that area].
2 waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
Then those women invited the men to come when the sacrifices were being offered to their gods. The Israeli men [accepted]. They went to the feasts with the women and worshiped the gods of the Moab people-group.
3 Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
By doing that, those Israeli people joined the women in worshiping the god Baal [add] the Moab people-group thought lived on Peor Mountain. That caused Yahweh to become very angry with his people.
4 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
Yahweh said this to Moses/me: “Seize all the leaders of those men who are doing this and execute them while I am watching. Do that in the daytime. After you do that, I will no longer be angry with the Israeli people.”
5 Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
So Moses/I said to the other Israeli leaders, “Each of you must execute your men who have joined [others] in worshiping Baal.”
6 Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
[But later], while Moses/I and many [HYP] other people were crying at the entrance of the Sacred Tent, while they/we were watching, one of the Israeli men brought a woman from the Midian people-group into his tent [and started to have sex with her].
7 Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
When Phinehas, who was the grandson of Aaron, saw that, he grabbed a spear
8 ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
and rushed into the man’s tent. He thrust the spear completely through the man’s body and into the woman’s belly [and killed both of them]. When he did that, the (plague/serious illness) [that had started to strike the Israelis] stopped.
9 Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
But 24,000 people had already died [from that plague].
10 Ubangiji ya ce wa Musa,
Then Yahweh said to Moses/me,
11 “Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
“Phinehas has caused me to stop being angry with the Israeli people, by being as eager as I am [to stop this sinful behavior]. I was ready to get rid of all the Israeli people because I was extremely angry, but Phinehas has prevented me from doing that.
12 Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
Now tell him that I am making a special peace agreement with him.
13 Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
In this agreement, I am promising to give to him and to his descendants the right/authority to be priests. I am doing this because [he showed that] he was very eager to honor me, his God, by stopping this sinful behavior. He has caused the Israeli people to become acceptable to me again by causing them to be forgiven for their sin.”
14 Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
The Israeli man who was killed with the woman of the Moab people-group was named Zimri. He was the son of Salu, who was the leader of a family from the tribe of Simeon.
15 Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
The woman’s name was Cozbi. She was the daughter of Zur, who was the leader of one of the clans of the Midian people-group.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
Then Yahweh said to Moses/me,
17 “Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
“[Take your men and] attack the Midian people-group and kill them.
18 gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”
They have become your enemies, because they tricked you Israeli people and induced/persuaded many of you to worship Baal, and because [one of your men had sex with] Cozbi, who was the daughter of a leader of the Midian people-group. She was killed at the time the plague [started because the people sinned] at Peor [Mountain].”

< Ƙidaya 25 >