< Ƙidaya 25 >
1 Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
And it remained Israel in Shittim and it began the people to commit fornication into [the] daughters of Moab.
2 waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
And they invited the people to [the] sacrifices of gods their and it ate the people and they bowed down to gods their.
3 Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
And it joined itself Israel to Baal Peor and it burned [the] anger of Yahweh on Israel.
4 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
And he said Yahweh to Moses take all [the] leaders of the people and impale them to Yahweh before the sun so may it turn away [the] burning of [the] anger of Yahweh from Israel.
5 Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
And he said Moses to [the] judges of Israel kill everyone men his who have joined themselves to Baal Peor.
6 Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
And there! a man from [the] people of Israel [was] coming and he brought near to brothers his the Midianite [woman] to [the] eyes of Moses and to [the] eyes of all [the] congregation of [the] people of Israel and they [were] weeping [the] entrance of [the] tent of meeting.
7 Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
And he saw [it] Phinehas [the] son of Eleazar [the] son of Aaron the priest and he arose from among the congregation and he took a spear in hand his.
8 ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
And he went after [the] man of Israel into the tent and he pierced through both of them [the] man of Israel and the woman into belly her and it was restrained the plague from on [the] people of Israel.
9 Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
And they were those [who] died by the plague four and twenty thousand.
10 Ubangiji ya ce wa Musa,
And he spoke Yahweh to Moses saying.
11 “Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
Phinehas [the] son of Eleazar [the] son of Aaron the priest he has turned back rage my from against [the] people of Israel because was zealous he zeal my in midst of them and not I made an end of [the] people of Israel in zeal my.
12 Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
Therefore say here I [am] about to give to him covenant my peace.
13 Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
And it will belong to him and to offspring his after him a covenant of priesthood of perpetuity because that he was zealous for God his and he made atonement on [the] people of Israel.
14 Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
And [the] name of [the] man of Israel who was struck down who he was struck down with the Midianite [woman] [was] Zimri [the] son of Salu a leader of a house of a father of the Simeonite[s].
15 Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
And [the] name of the woman who was struck down the Midianite [woman] [was] Cozbi [the] daughter of Zur [was] a leader of tribes a house of a father in Midian he.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
And he spoke Yahweh to Moses say.
17 “Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
oppose The Midianites and you will strike down them.
18 gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”
For [are] opposers they you by deceitfulness their which they have dealt deceptively to you on [the] matter of Peor and on [the] matter of Cozbi [the] daughter of [the] leader of Midian sister their who was struck down on [the] day of the plague on [the] matter of Peor.