< Ƙidaya 25 >

1 Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
Now when Israel was living in Shittim the people became false to the Lord, doing evil with the daughters of Moab:
2 waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
For they sent for the people to be present at the offerings made to their gods; and the people took part in their feasts and gave honour to their gods.
3 Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
So Israel had relations with the women of Moab in honour of the Baal of Peor: and the Lord was moved to wrath against Israel.
4 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
Then the Lord said to Moses, Take all the chiefs of the people, hanging them up in the sun before the Lord, so that the wrath of the Lord may be turned from Israel.
5 Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
So Moses said to the judges of Israel, Let everyone put to death those of his men who have had relations with the women of Moab in honour of the Baal of Peor.
6 Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
Then one of the children of Israel came to his brothers, taking with him a woman of Midian, before the eyes of Moses and all the meeting of the people, while they were weeping at the door of the Tent of meeting.
7 Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
And Phinehas, the son of Eleazar, the son of Aaron the priest, seeing it, got up from among the people and took a spear in his hand,
8 ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
And went after the man of Israel into the tent, driving the spear through the two of them, through the man of Israel and through the stomach of the woman. So the disease was stopped among the children of Israel.
9 Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
But twenty-four thousand of them had come to their death by the disease.
10 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord said to Moses,
11 “Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
Through Phinehas, and because of his passion for my honour, my wrath has been turned away from the children of Israel, so that I have not sent destruction on them all in my wrath.
12 Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
So say to them that I will make with him an agreement of peace:
13 Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
And by this agreement, he and his sons after him have the right to be priests for ever; because, by his care for the honour of his God, he took away the sin of the children of Israel.
14 Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
Now the man of Israel who was put to death with the woman of Midian was Zimri, the son of Salu, a chief of one of the families of the Simeonites.
15 Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
And the woman of Midian who was put to death was Cozbi, the daughter of Zur; he was the head of a family in Midian.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
Then the Lord said to Moses,
17 “Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
Take up arms against the Midianites and overcome them;
18 gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”
For they are a danger to you with their false ways, causing sin to come on you in the question of Peor, and because of Cozbi, their sister, the daughter of the chief of Midian, who was put to death at the time of the disease which came on you because of Peor.

< Ƙidaya 25 >