< Ƙidaya 24 >

1 To, da Bala’am ya ga cewa Ubangiji yana jin daɗin sa wa Isra’ila albarka, bai koma wajen sihiri kamar dā ba, amma ya juya fuskarsa wajen hamada.
Cuando Balaam vio que era un placer del Señor dar su bendición a Israel, como en otras ocasiones, no usó las artes secretas, sino que volvió su rostro hacia él desierto.
2 Da Bala’am ya duba sai ya ga Isra’ila sun yi sansani kabila, kabila, Ruhun Allah kuwa ya sauko masa,
Y alzando sus ojos, vio a Israel allí, con sus tiendas en el orden de sus tribus; y el espíritu de Dios vino sobre él.
3 sai ya yi annabcinsa ya ce, “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
Y conmovido por el espíritu, dijo: Estas son las palabras de Balaam, hijo de Beor, las palabras del hombre cuyos ojos están abiertos:
4 maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, maganar wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, mutumin da ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
Él dice, cuyos oídos están abiertos a las palabras de Dios, que ha visto la visión del Gobernante de todos, cayendo, pero con los ojos abiertos.
5 “Ina misalin kyan tentunanka, ya Yaƙub, wuraren zamanka, ya Isra’ila!
¡Qué hermosas son tus tiendas, oh Jacob, tus habitaciones, oh Israel!
6 “Kamar kwaruruka suke a shimfiɗe, kamar lambu kusa da rafi, kamar itatuwan aloyes da Ubangiji ya dasa, kamar itatuwa al’ul kusa da ruwaye.
Se extienden como valles, como jardines a orillas del río, como árboles en flor plantados por el Señor, como árboles de cedro por las aguas.
7 Ruwa zai kwararo daga bokitinsu; irinsu za su sami ruwa a yalwace. “Sarkinsu zai fi sarkin Agag; mulkinsu zai ɗaukaka.
De sus manos brotara agua, su simiente será en muchas aguas; su rey será más alto que Agag, y su reino se hará grande en honor.
8 “Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfin kutunkun ɓauna. Sun cinye abokan gāban, suka kakkarya ƙasusuwansu; da kibiyoyinsu suka sossoke su.
Es Dios quien lo sacó de Egipto; tiene fuerzas como de búfalo las naciones que luchan contra él serán su alimento, sus huesos serán quebrantados, serán heridos con sus flechas.
9 Kamar zaki sun laɓe sun kwanta, kamar zakanya, wa zai yi ƙarfin hali yă tashe su? “Bari waɗanda suka albarkace ka, su sami albarka waɗanda kuma suka la’anta ka, su la’antu!”
Tomó su sueño extendido como un león, y como una leona: ¿por quién interrumpirá su descanso? Que una bendición sea para todos los que te dan la bendición, y una maldición para todos los que te maldijeron.
10 Fushin Balak ya ƙuna a kan Bala’am. Ya tafa hannunsa, ya ce masa, “Na kira ka don ka la’anta abokan gābana, amma sai ga shi ka sa musu albarka har sau uku.
Entonces Balac se llenó de ira contra Balaam, y agitando sus manos airadamente, le dijo a Balaam: “Yo envié por ti para que los que están en mi contra puedan ser maldecidos, pero ahora, mira, tres veces les has dado una bendición.
11 Yanzu ka bar nan ka tafi gida! Na ce zan sāka maka da lada mai kyau, amma Ubangiji ya hana ka samun ladan.”
Regresa rápidamente al lugar de donde viniste: era mi propósito darte un lugar de honor, pero ahora el Señor te ha alejado del honor.
12 Bala’am ya ce wa Balak, “Ban faɗa wa’yan aikan da ka aiko wurina ba cewa,
Entonces Balaam dijo a Balac: ¿No he dicho a los hombres que me enviaste, diciendo:
13 ‘Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba, kuma dole in faɗa abin da Ubangiji ya ce ne kawai’?
Aun si Balac me diera su casa llena de plata y oro, no me sería posible ir fuera de las órdenes del Señor, haciendo el bien o el mal por el impulso de mi mente; lo que diga el Señor, yo diré?
14 Yanzu zan koma wajen mutanena, amma bari in gargaɗe ka game da abin da mutanen nan za su yi wa mutanenka cikin kwanaki masu zuwa.”
Así que ahora volveré con mi gente; pero primero permítanme aclararles lo que esta gente hará a tu gente en los próximos días.
15 Sa’an nan ya furta saƙonsa. “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
Luego continuó con su historia y dijo: Estas son las palabras de Balaam, el hijo de Beor, las palabras de aquel cuyos ojos están abiertos:
16 maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, wanda yake da sani daga Mafi Ɗaukaka, wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, wanda ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
Dijo él que oyó las palabras de Dios, que tiene conocimiento del Altísimo, que ha visto la visión del omnipotente, cayendo en éxtasis y con sus ojos abiertos.
17 “Na gan shi, amma ba yanzu ba; na hange shi, amma ba kusa ba. Tauraro zai fito daga Yaƙub; sandan mulki zai fito daga Isra’ila. Zai ragargaje goshin Mowab, kawunan dukan’ya’yan Set.
Lo veo, pero no ahora: mirándolo, pero no cerca: saldrá una estrella de Jacob, y una vara de autoridad de Israel, enviando destrucción a los límites más lejanos de Moab y sobre la cabeza de todos los hijos de Set.
18 Za a ci Edom da yaƙi; za a ci Seyir, abokiyar gābanta, amma Isra’ila zai ƙara ƙarfi.
Edom será su herencia, y pondrá fin al último de los habitantes de Seir.
19 Mai mulki zai fito daga Yaƙub yă hallaka waɗanda suka ragu a birnin.”
E Israel continuará con fuerza, y Jacob tendrá dominio sobre sus enemigos.
20 Sai Bala’am ya ga Amalek, ya kuma furta maganarsa. “Amalek yana cikin al’ummai na fari, amma zai zama na ƙarshen da za a hallaka.”
Luego, volviendo sus ojos a Amalec, continuó con su historia y dijo: Amalec fue la primera de las naciones, pero su parte será destrucción para siempre.
21 Sai ya ga Keniyawa, ya kuma furta maganarsa. “Wurin zamanku lafiya yake, an kuma sa sheƙarku a cikin duwatsu;
Mirando al ceneo, continuó con su historia y dijo: Fuerte es tu lugar de vida, y tu lugar secreto está a salvo en la roca.
22 duk da haka, za a hallaka ku Keniyawa sa’ad da Asshur ya kame ku.”
Pero aún así, los descendientes de Caín serán destruidos con fuego, cuando Asiria les lleve prisionero.
23 Sai ya furta maganarsa ya ce, “Wayyo, wa zai rayu sa’ad da Allah ya yi haka?
Luego continuó con su historia y dijo: ¿Pero quién puede conservar su vida cuando Dios hace esto?
24 Jiragen ruwa za su zo daga Kittim; za su murƙushe Asshur da Eber, amma su ma za a hallaka su.”
Pero los barcos vendrán de la dirección de Chipre, a Asiria y a Heber, y al igual que a los demás, su destino será la destrucción.
25 Sa’an nan Bala’am ya tashi ya koma gidan, Balak kuma ya yi tafiyarsa.
Entonces Balaam se levantó y volvió a su lugar, y Balac se fue.

< Ƙidaya 24 >