< Ƙidaya 24 >

1 To, da Bala’am ya ga cewa Ubangiji yana jin daɗin sa wa Isra’ila albarka, bai koma wajen sihiri kamar dā ba, amma ya juya fuskarsa wajen hamada.
Da Bileam så at det var Herrens vilje at han skulde velsigne Israel, gikk han ikke bort for å søke tegn, som han hadde gjort de to første ganger, men vendte sig mot ørkenen.
2 Da Bala’am ya duba sai ya ga Isra’ila sun yi sansani kabila, kabila, Ruhun Allah kuwa ya sauko masa,
Og Bileam løftet sine øine og så Israel leiret efter sine stammer. Da kom Guds Ånd over ham,
3 sai ya yi annabcinsa ya ce, “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
og han tok til å kvede og sa: Så sier Bileam, Beors sønn, så sier mannen hvis øie er lukket,
4 maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, maganar wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, mutumin da ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
så sier han som hører ord fra Gud, som skuer syner fra den Allmektige, segnet til jorden med oplatt øie:
5 “Ina misalin kyan tentunanka, ya Yaƙub, wuraren zamanka, ya Isra’ila!
Hvor fagre er dine telt, Jakob, dine boliger, Israel!
6 “Kamar kwaruruka suke a shimfiɗe, kamar lambu kusa da rafi, kamar itatuwan aloyes da Ubangiji ya dasa, kamar itatuwa al’ul kusa da ruwaye.
Som vide bekkedaler, som haver ved en elv, som aloëtrær Herren har plantet, som sedrer ved vannet!
7 Ruwa zai kwararo daga bokitinsu; irinsu za su sami ruwa a yalwace. “Sarkinsu zai fi sarkin Agag; mulkinsu zai ɗaukaka.
Det strømmer vann av hans spann, og hans ætt bor ved store vann. Mektigere enn Agag skal hans konge være, ophøiet hans kongerike!
8 “Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfin kutunkun ɓauna. Sun cinye abokan gāban, suka kakkarya ƙasusuwansu; da kibiyoyinsu suka sossoke su.
Gud førte ham ut av Egypten; styrke har han som en villokse; han skal fortære hedningefolkene som står ham imot, og knuse deres ben og gjennembore dem med sine piler.
9 Kamar zaki sun laɓe sun kwanta, kamar zakanya, wa zai yi ƙarfin hali yă tashe su? “Bari waɗanda suka albarkace ka, su sami albarka waɗanda kuma suka la’anta ka, su la’antu!”
Han legger sig, han hviler som en løve, som en løvinne; hvem våger å vekke ham? Velsignet være den som velsigner dig, og forbannet den som forbanner dig!
10 Fushin Balak ya ƙuna a kan Bala’am. Ya tafa hannunsa, ya ce masa, “Na kira ka don ka la’anta abokan gābana, amma sai ga shi ka sa musu albarka har sau uku.
Da optendtes Balaks vrede mot Bileam, og han slo sine hender sammen. Og Balak sa til Bileam: Jeg kalte dig hit for å forbanne mine fiender, og nu har du velsignet tre ganger.
11 Yanzu ka bar nan ka tafi gida! Na ce zan sāka maka da lada mai kyau, amma Ubangiji ya hana ka samun ladan.”
Far nu hjem så fort du kan! Jeg hadde tenkt å vise dig ære, men du ser Herren har nektet dig den.
12 Bala’am ya ce wa Balak, “Ban faɗa wa’yan aikan da ka aiko wurina ba cewa,
Bileam svarte Balak: Sa jeg ikke allerede til de bud du sendte til mig:
13 ‘Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba, kuma dole in faɗa abin da Ubangiji ya ce ne kawai’?
Om Balak gav mig sitt hus fullt av sølv og gull, kunde jeg ikke overtrede Herrens ord og gjøre noget efter mitt eget tykke, enten godt eller ondt; jeg kan ikke tale annet enn hvad Herren sier.
14 Yanzu zan koma wajen mutanena, amma bari in gargaɗe ka game da abin da mutanen nan za su yi wa mutanenka cikin kwanaki masu zuwa.”
Se, jeg vender nu hjem til mitt folk; men la mig først varsle dig om hvad dette folk skal gjøre med ditt folk i de siste dager.
15 Sa’an nan ya furta saƙonsa. “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
Og han tok til å kvede og sa: Så sier Bileam, Beors sønn, så sier mannen hvis øie er lukket,
16 maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, wanda yake da sani daga Mafi Ɗaukaka, wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, wanda ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
så sier han som hører ord fra Gud og har fått kunnskap fra den Høieste, han som skuer syner fra den Allmektige, segnet til jorden med oplatt øie:
17 “Na gan shi, amma ba yanzu ba; na hange shi, amma ba kusa ba. Tauraro zai fito daga Yaƙub; sandan mulki zai fito daga Isra’ila. Zai ragargaje goshin Mowab, kawunan dukan’ya’yan Set.
Jeg ser ham, men ikke nu, jeg skuer ham, men ikke nær; en stjerne stiger op av Jakob, et spir løfter sig fra Israel; han knuser Moabs tinninger og utrydder ufreds-ætten.
18 Za a ci Edom da yaƙi; za a ci Seyir, abokiyar gābanta, amma Isra’ila zai ƙara ƙarfi.
Edom blir ham underlagt, og Se'ir, hans fiende, blir ham underlagt; stort velde vinner Israel.
19 Mai mulki zai fito daga Yaƙub yă hallaka waɗanda suka ragu a birnin.”
En hersker går ut fra Jakob, han utrydder av byene dem som har reddet sig dit.
20 Sai Bala’am ya ga Amalek, ya kuma furta maganarsa. “Amalek yana cikin al’ummai na fari, amma zai zama na ƙarshen da za a hallaka.”
Så fikk han se amalekittene; da tok han til å kvede og sa: Det første blandt hedningefolkene er Amalek; men til sist skal han gå til grunne.
21 Sai ya ga Keniyawa, ya kuma furta maganarsa. “Wurin zamanku lafiya yake, an kuma sa sheƙarku a cikin duwatsu;
Så fikk han se kenittene, og han tok til å kvede og sa: Fast er din bolig, og bygget på klippen ditt rede;
22 duk da haka, za a hallaka ku Keniyawa sa’ad da Asshur ya kame ku.”
men enda skal Kain bli ødelagt når Assur fører dig bort i fangenskap.
23 Sai ya furta maganarsa ya ce, “Wayyo, wa zai rayu sa’ad da Allah ya yi haka?
Så tok han igjen til å kvede og sa: Ve! Hvem skal bli i live når Gud lar dette skje?
24 Jiragen ruwa za su zo daga Kittim; za su murƙushe Asshur da Eber, amma su ma za a hallaka su.”
Skiber kommer fra Kittims kyst, de kuer Assur, og de kuer Eber; men også han skal gå til grunne.
25 Sa’an nan Bala’am ya tashi ya koma gidan, Balak kuma ya yi tafiyarsa.
Så gjorde Bileam sig rede og vendte hjem igjen; og Balak drog også sin vei.

< Ƙidaya 24 >