< Ƙidaya 23 >

1 Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
Bileám je rekel Baláku: »Tukaj mi zgradi sedem oltarjev in mi pripravi sedem volov ter sedem ovnov.«
2 Balak ya yi yadda Bala’am ya faɗa, sai su biyu suka miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
Balák je storil, kakor je Bileám govoril, in Balák in Bileám sta na vsakem oltarju darovala bikca in ovna.
3 Sa’an nan Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in koma wani wurin da yake a kaɗaice. Wataƙila Ubangiji zai sadu da ni. Duk abin da ya bayyana mini, zan faɗa maka.” Sai ya haura kan wani wurin da yake a kaɗaice a tudun.
Bileám je rekel Baláku: »Stoj pri svoji žgalni daritvi, jaz pa bom šel. Morda bo prišel Gospod, da me sreča in karkoli mi pokaže, ti bom povedal.« In odšel je na visok kraj.
4 Allah kuwa ya sadu da Bala’am. Bala’am ya ce, “Na shirya bagadai bakwai, na kuma miƙa bijimi guda da rago guda, a kan kowane bagade.”
Bog je srečal Bileáma in ta mu je rekel: »Pripravil sem sedem oltarjev in na vsakem oltarju sem daroval bikca in ovna.«
5 Ubangiji ya ba wa Bala’am saƙo ya ce, “Ka koma wurin Balak, ka faɗa masa wannan saƙo.”
Gospod je v Bileámova usta položil besedo ter rekel: »Vrni se k Baláku in tako boš govoril.«
6 Saboda haka, sai Bala’am ya koma wurin Balak ya same shi tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dukan dattawan Mowab.
Vrnil se je k njemu in glej, ta je stal poleg svoje žgalne daritve, on in vsi Moábovi princi.
7 Sai Bala’am ya furta abin da Allah ya faɗa masa ya ce, “Balak ya kawo ni daga Aram, sarkin Mowab ya kawo ni daga gabashin duwatsu. Ya ce, ‘Zo, ka la’anta mini Yaƙub; zo, ka tsine Isra’ila.’
Vzel je njegovo prispodobo ter rekel: »Moábski kralj Balák me je privedel iz Aráma, iz vzhodnih gora, rekoč: ›Pridi, prekolni mi Jakoba in pridi izzivat Izraela.‹
8 Yaya zan iya la’anta waɗanda Allah bai la’anta ba? Yaya zan tsine waɗanda Ubangiji bai tsine ba?
Kako naj prekolnem, kogar Bog ni preklel? Kako naj izzivam, kogar Gospod ni izzival?
9 Daga kan duwatsu na gan su, daga bisa kan tuddai na hange su. Na ga mutane da suke zaune su kaɗai ba sa ɗauki kansu ɗaya da al’ummai ba.
Kajti od vrha skal ga vidim in od hribov ga gledam. Glej, ljudstvo bo prebivalo samo in ne bo šteto med narode.
10 Wa zai iya ƙidaya ƙurar Yaƙub ko yă ƙidaya kashi ɗaya bisa huɗu na Isra’ila? Bari in mutu, mutuwar adali ƙarshena kuma yă zama kamar nasu!”
Kdo lahko prešteje Jakobov prah in število četrtine Izraela? Naj umrem smrt pravičnega in naj bo moj zadnji konec podoben njegovemu!«
11 Balak ya ce wa Bala’am, “Me ke nan ka yi mini? Na kawo ka, ka la’anta abokan gābana, sai ga shi albarka kake sa musu!”
Balák pa je rekel Bileámu: »Kaj si mi storil? Vzel sem te, da prekolneš moje sovražnike in glej, ti si jih vse skupaj blagoslovil.«
12 Bala’am ya ce, “Ba dole in faɗa abin da Ubangiji ya sa a bakina ba?”
Ta je odgovoril in rekel: »Mar ne morem paziti, da govorim to, kar je Gospod položil v moja usta?«
13 Sa’an nan Balak ya ce masa, “Zo, mu tafi wani wuri inda za ka gan su; a nan kana ganin sashe ne kawai, ba dukansu ba. Daga can kuwa, ka la’anta mini su.”
Balák mu je rekel: »Pridi, prosim te, z menoj na drug kraj, od koder jih lahko vidiš. Videl boš le njihov skrajni del, ne boš pa videl vseh, in od tam mi jih prekolni.«
14 Saboda haka ya ɗauke shi zuwa filin Zofim a ƙwanƙolin Fisga, a can ya gina bagadai bakwai, ya kuma miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
Privedel ga je na polje Zofim, k vrhu Pisge in zgradil sedem oltarjev in na vsakem oltarju daroval bikca in ovna.
15 Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in je in sadu da Ubangiji a can.”
Baláku je rekel: »Stoj tukaj pri svoji žgalni daritvi, medtem ko tam srečam Gospoda.«
16 Ubangiji ya sadu da Bala’am, ya kuma ba shi saƙo ya ce, “Koma wurin Balak ka ba shi wannan saƙo.”
Gospod je srečal Bileáma in v njegova usta položil besedo ter rekel: »Ponovno pojdi k Baláku in tako povej.«
17 Saboda haka ya tafi ya same Balak tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dattawan Mowab. Balak ya tambaye Bala’am ya ce, “Mene ne Ubangiji ya ce?”
Ko je prišel k njemu, glej, je ta stal pri svoji žgalni daritvi in princi Moába z njim. In Balák mu je rekel: »Kaj je Gospod govoril?«
18 Sai Bala’am ya furta saƙon da aka ba shi ya ce, “Tashi, Balak, ka saurara; ka kasa kunne gare ni, ɗan Ziffor.
Ta je vzel njegovo prispodobo ter rekel: »Vstani, Balák in poslušaj; prisluhni mi, ti, Cipórjev sin.
19 Allah ba mutum ba ne, da zai yi ƙarya, shi ba ɗan mutum ba ne, da zai canja tunaninsa. Yana maganar abin da ba zai iya aikata ba ne? Yakan kuma yi alkawarin da ba zai iya cikawa ba?
Bog ni človek, da bi lagal; niti človeški sin, da bi se moral kesati. Je rekel in tega ne bi storil? Je govoril in ali tega ne bi dobro naredil?
20 Na karɓi umarni in sa albarka; na kuwa sa albarka, ba zan iya janye ta ba.
Glej, prejel sem zapoved, da blagoslovim in on je blagoslovil in tega ne morem razveljaviti.
21 “Bai ga mugunta a cikin Yaƙub ba, bai kuma ga wahala a Isra’ila ba. Ubangiji Allahnsu yana tare da su; sowar Sarki yana cikinsu.
Ni zagledal krivičnosti v Jakobu niti ni videl perverznosti v Izraelu. Gospod, njegov Bog, je z njim in krik kralja je med njimi.
22 Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfi iri na kutunkun ɓauna.
Bog jih je privedel iz Egipta; moč ima, kakor bi bila moč od samoroga.
23 Ba wata maitar da za tă ci Yaƙub, ba sihiri da zai cuci Isra’ila. Yanzu za a ce game da Yaƙub da Isra’ila, ‘Duba abin da Allah ya yi!’
Zagotovo tam ni izrekanja uroka zoper Jakoba niti tam ni nobenega vedeževanja zoper Izraela. Glede na ta čas bo to rečeno o Jakobu in o Izraelu; ›Kaj je Bog storil!‹
24 Mutane sun tashi kamar ƙaƙƙarfar zakanya; sun tā da kansu kamar zaki wanda ba ya hutawa sai ya cinye naman abin da ya kama ya kuma sha jinin abin da ya kama.”
Glej, ljudstvo bo vstalo kakor velik lev in se dvignilo kakor mlad lev. On se ne bo ulegel, dokler ne jé od plena in ne pije krvi umorjenega.«
25 Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Kada ka la’anta su, kada kuma ka sa musu albarka!”
Balák je rekel Bileámu: »Niti jih sploh ne preklinjaj niti jih sploh ne blagoslavljaj.«
26 Bala’am amsa ya ce, “Ban faɗa maka zan yi kaɗai abin da Ubangiji ya ce ba?”
Toda Bileám je odgovoril in rekel Baláku: »Mar ti nisem rekel, rekoč: ›Vse, kar Gospod govori, to moram storiti?‹«
27 Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Zo in kai ka wani wuri. Wataƙila zai gamshi Allah, yă bari ka la’anta mini su daga can.”
Balák je rekel Bileámu: »Pridi, prosim te, privedel te bom na drug kraj. Morda bo to ugajalo Bogu, da mi jih boš od tam preklel.«
28 Balak kuwa ya ɗauki Bala’am zuwa ƙwanƙolin Feyor, wanda yake fuskantar hamada.
In Balák je privedel Bileáma na vrh Peórja, ki gleda proti Ješimonu.
29 Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka kuma shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
Bileám je rekel Baláku: »Tukaj mi zgradi sedem oltarjev in tukaj mi pripravi sedem bikcev in sedem ovnov.«
30 Balak ya yi yadda Bala’am ya ce, ya kuwa miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
Balák je storil kakor je Bileám rekel in na vsakem oltarju daroval bikca in ovna.

< Ƙidaya 23 >