< Ƙidaya 23 >
1 Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
Og Bileam sagde til Balak: Byg mig her syv Altere, og bered mig her syv Okser og syv Vædre.
2 Balak ya yi yadda Bala’am ya faɗa, sai su biyu suka miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
Og Balak gjorde, som Bileam sagde; og Balak og Bileam ofrede en Okse og en Væder paa hvert Alter.
3 Sa’an nan Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in koma wani wurin da yake a kaɗaice. Wataƙila Ubangiji zai sadu da ni. Duk abin da ya bayyana mini, zan faɗa maka.” Sai ya haura kan wani wurin da yake a kaɗaice a tudun.
Og Bileam sagde til Balak: Stil dig ved dit Brændoffer, og jeg vil gaa hen, maaske Herren møder mig, og det Ord, som han lader mig skue, vil jeg give dig til Kende; og han gik op paa et højt Sted.
4 Allah kuwa ya sadu da Bala’am. Bala’am ya ce, “Na shirya bagadai bakwai, na kuma miƙa bijimi guda da rago guda, a kan kowane bagade.”
Og Gud mødte Bileam, og denne sagde til ham: Jeg har oprejst syv Altere og ofret en Okse og en Væder paa hvert Alter.
5 Ubangiji ya ba wa Bala’am saƙo ya ce, “Ka koma wurin Balak, ka faɗa masa wannan saƙo.”
Da lagde Herren Ord i Bileams Mund og sagde: Vend tilbage til Balak, og saaledes skal du tale.
6 Saboda haka, sai Bala’am ya koma wurin Balak ya same shi tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dukan dattawan Mowab.
Og han vendte tilbage til ham, og se, han stod ved sit Brændoffer, han og alle Moabiternes Fyrster.
7 Sai Bala’am ya furta abin da Allah ya faɗa masa ya ce, “Balak ya kawo ni daga Aram, sarkin Mowab ya kawo ni daga gabashin duwatsu. Ya ce, ‘Zo, ka la’anta mini Yaƙub; zo, ka tsine Isra’ila.’
Da tog han til sit Sprog og sagde: Fra Syrien har Balak, Moabiternes Konge, ladet mig hente, fra Bjergene mod Østen: Gak hid, forband mig Jakob, og gak hid, øs Vrede paa Israel!
8 Yaya zan iya la’anta waɗanda Allah bai la’anta ba? Yaya zan tsine waɗanda Ubangiji bai tsine ba?
Hvorledes skal jeg forbande, da Gud ikke forbander ham? hvorledes skal jeg vredes, da Herren ikke vredes?
9 Daga kan duwatsu na gan su, daga bisa kan tuddai na hange su. Na ga mutane da suke zaune su kaɗai ba sa ɗauki kansu ɗaya da al’ummai ba.
Thi fra Klippernes Top ser jeg ham, og fra Højene skuer jeg ham; se, det Folk skal bo alene og skal ikke regne sig til Hedningerne.
10 Wa zai iya ƙidaya ƙurar Yaƙub ko yă ƙidaya kashi ɗaya bisa huɗu na Isra’ila? Bari in mutu, mutuwar adali ƙarshena kuma yă zama kamar nasu!”
Hvo har talt Jakobs Støv og Tallet paa den fjerde Part af Israel? Min Sjæl dø de oprigtiges Død, og mit Endeligt vorde som hans!
11 Balak ya ce wa Bala’am, “Me ke nan ka yi mini? Na kawo ka, ka la’anta abokan gābana, sai ga shi albarka kake sa musu!”
Da sagde Balak til Bileam: Hvad gør du imod mig? jeg tog dig hid til at forbande mine Fjender, og se, du har velsignet dem.
12 Bala’am ya ce, “Ba dole in faɗa abin da Ubangiji ya sa a bakina ba?”
Og han svarede og sagde: Skal jeg ikke tage Vare paa at tale det, som Herren lægger i min Mund?
13 Sa’an nan Balak ya ce masa, “Zo, mu tafi wani wuri inda za ka gan su; a nan kana ganin sashe ne kawai, ba dukansu ba. Daga can kuwa, ka la’anta mini su.”
Og Balak sagde til ham: Kære, kom med mig til et andet Sted, fra hvilket du kan se dem, dog skal du kun se det yderste af dem, men du skal ikke se dem alle; og forband mig dem derfra.
14 Saboda haka ya ɗauke shi zuwa filin Zofim a ƙwanƙolin Fisga, a can ya gina bagadai bakwai, ya kuma miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
Og han tog ham med sig paa Zofims Mark til Pisgas Top og byggede syv Altere og ofrede en Okse og en Væder paa hvert Alter.
15 Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in je in sadu da Ubangiji a can.”
Og han sagde til Balak: Stil dig her ved dit Brændoffer, og jeg vil saa søge et Møde.
16 Ubangiji ya sadu da Bala’am, ya kuma ba shi saƙo ya ce, “Koma wurin Balak ka ba shi wannan saƙo.”
Og Herren mødte Bileam og lagde Ord i hans Mund, og han sagde: Vend tilbage til Balak, og saaledes skal du tale.
17 Saboda haka ya tafi ya same Balak tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dattawan Mowab. Balak ya tambaye Bala’am ya ce, “Mene ne Ubangiji ya ce?”
Og han kom til ham, og se, han stod ved sit Brændoffer og Moabiternes Fyrster hos ham, og Balak sagde til ham: Hvad sagde Herren?
18 Sai Bala’am ya furta saƙon da aka ba shi ya ce, “Tashi, Balak, ka saurara; ka kasa kunne gare ni, ɗan Ziffor.
Og han tog til sit Sprog og sagde: Staa op, Balak, og hør, bøj dit Øre til mig, Zippors Søn!
19 Allah ba mutum ba ne, da zai yi ƙarya, shi ba ɗan mutum ba ne, da zai canja tunaninsa. Yana maganar abin da ba zai iya aikata ba ne? Yakan kuma yi alkawarin da ba zai iya cikawa ba?
Gud er ikke et Menneske, at han lyver, ej heller et Menneskes Barn, at han skulde angre; har han sagt det, og skulde ikke gøre det? og har han talet, og skulde ikke holde det?
20 Na karɓi umarni in sa albarka; na kuwa sa albarka, ba zan iya janye ta ba.
Se, at velsigne er mig overdraget; han velsignede, og jeg kan ikke forandre det.
21 “Bai ga mugunta a cikin Yaƙub ba, bai kuma ga wahala a Isra’ila ba. Ubangiji Allahnsu yana tare da su; sowar Sarki yana cikinsu.
Han skuede ikke Uret i Jakob og saa ikke Jammer i Israel; Herren, hans Gud, er med ham, og Kongejubel hos ham.
22 Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfi iri na kutunkun ɓauna.
Gud er den, som førte dem ud af Ægypten, de have megen Styrke som Enhjørningen.
23 Ba wata maitar da za tă ci Yaƙub, ba sihiri da zai cuci Isra’ila. Yanzu za a ce game da Yaƙub da Isra’ila, ‘Duba abin da Allah ya yi!’
Thi der er ingen Spaadomskunst i Jakob og ingen Sandsigerkunst i Israel; i sin Tid skal der siges til Jakob og til Israel, hvad Gud har gjort.
24 Mutane sun tashi kamar ƙaƙƙarfar zakanya; sun tā da kansu kamar zaki wanda ba ya hutawa sai ya cinye naman abin da ya kama ya kuma sha jinin abin da ya kama.”
Se, det Folk skal staa op som en Løvinde og ophøje sig som en Løve; det skal ikke lægge sig, før det æder Rovet og drikker de ihjelslagnes Blod.
25 Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Kada ka la’anta su, kada kuma ka sa musu albarka!”
Da sagde Balak til Bileam: Du skal hverken forbande det, ej heller skal du velsigne det.
26 Bala’am amsa ya ce, “Ban faɗa maka zan yi kaɗai abin da Ubangiji ya ce ba?”
Og Bileam svarede og sagde til Balak: Har jeg ej talet til dig og sagt: Alt det, som Herren vil tale, det vil jeg gøre?
27 Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Zo in kai ka wani wuri. Wataƙila zai gamshi Allah, yă bari ka la’anta mini su daga can.”
Og Balak sagde til Bileam: Kære, gaa med, jeg vil tage dig med hen til et andet Sted; maaske det maatte være Ret for Guds Øjne, at du derfra forbander mig det.
28 Balak kuwa ya ɗauki Bala’am zuwa ƙwanƙolin Feyor, wanda yake fuskantar hamada.
Og Balak tog Bileam med sig paa Peors Top, som skuer ud over Ørken.
29 Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka kuma shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
Og Bileam sagde til Balak: Byg mig her syv Altere, og bered mig her syv Okser og syv Vædre.
30 Balak ya yi yadda Bala’am ya ce, ya kuwa miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
Og Balak gjorde, som Bileam sagde, og ofrede en Okse og en Væder paa hvert Alter.