< Ƙidaya 22 >

1 Sai Isra’ilawa suka kama hanya, suka tafi filayen Mowab, a wajen Urdun, a ƙetare Yeriko, suka yi sansani a can.
Izraelovi otroci so se namerili naprej in se utaborili na moábskih ravninah, na tej strani Jordana, pri Jerihi.
2 To, fa, Balak ɗan Ziffor ya ga duk abin da Isra’ila suka yi da Amoriyawa.
Cipórjev sin Balák je videl vse, kar je Izrael storil Amoréjcem.
3 Sai Mowab ya firgita ƙwarai saboda yawan mutanen. Tsoron Isra’ilawa ya kama su.
Moáb je bil boleče prestrašen ljudstva, ker jih je bilo mnogo in Moáb je bil zaskrbljen zaradi Izraelovih otrok.
4 Sai Mowabawa suka ce wa dattawan Midiyawa, “Wannan taron zai lashe duk abin da ya kewaye mu kamar yadda saniya takan lashe ciyawa a fili.” Saboda haka Balak ɗan Ziffor, wanda yake sarkin Mowab a lokacin,
Moáb je rekel midjánskim starešinam: »Sedaj bo ta skupina polizala vse, ki so naokoli nas, kakor vol pomuli poljsko travo.« Cipórjev sin Balák je bil ob tistem času kralj Moábcev.
5 ya aika manzanni su zo da Bala’am ɗan Beyor, wanda yake a Fetor, kusa da Kogi, a ƙasar haihuwarsa. Balak ya ce, “Ga mutane sun fito daga Masar; sun mamaye ƙasar, suka kuma yi sansani kusa da ni.
Poslal je torej poslance k Beórjevemu sinu Bileámu v Petór, ki je poleg reke dežele otrok njegovega ljudstva, da ga pokliče, rekoč: »Glej, tam je ljudstvo prišlo iz Egipta. Glej, pokrivajo obličje zemlje in prebivajo nasproti meni.
6 Ka zo yanzu ka la’anta waɗannan mutane, domin sun fi ƙarfina. Wataƙila zan iya cin nasara a kansu, in kuma kore su daga ƙasar. Gama na sani duk waɗanda ka sa musu albarka, sun zama masu albarka ke nan, waɗanda kuma ka la’anta, sun la’antu ke nan.”
Pridi torej sedaj, prosim te, prekolni mi to ljudstvo, kajti oni so premogočni zame. Morda bom prevladal, da jih lahko udarimo in da jih lahko napodimo iz dežele, kajti vem, da kogar ti blagosloviš, je blagoslovljen in kogar ti prekolneš, je preklet.«
7 Sai dattawan Mowab da na Midiyawa suka tashi, suka ɗauki kuɗi don duba. Da suka zo wurin Bala’am sai suka faɗa masa abin da Balak ya ce.
Moábske starešine in midjánske starešine so odrinili z nagradami vedeževanja v svoji roki in prišli k Bileámu in mu spregovorili Balákove besede.
8 Bala’am ya ce musu, “Ku kwana a nan, ni kuwa zan faɗa muku abin da Ubangiji ya faɗa mini.” Saboda haka dattawan sarkin Mowab suka zauna da shi.
In ta jim je rekel: »To noč prenočite tukaj in ponovno vam bom prinesel besedo, kakor mi bo Gospod govoril, « in Moábovi princi so ostali z Bileámom.
9 Sai Allah ya zo wurin Bala’am ya ce, “Su wane ne waɗannan tare da kai?”
Bog je prišel k Bileámu in rekel: »Kakšni možje so tile s teboj?«
10 Bala’am ya ce wa Allah, “Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab ne, ya aiko mini wannan saƙo cewa,
Bileám je rekel Bogu: »Cipórjev sin Balák, moábski kralj, je poslal k meni, rekoč:
11 ‘Ga mutane sun fito daga Masar sun mamaye ƙasar. Ka zo yanzu ka la’anta mini su. Wataƙila ta haka zan yi nasara a kansu, in kuma kore su.’”
›Glej, tam je prišlo ljudstvo iz Egipta, ki pokriva obličje zemlje. Pridi sedaj, prekolni mi jih. Morda jih bom zmožen premagati in jih pognati ven.‹«
12 Amma Allah ya ce wa Bala’am, “Kada ka tafi tare da su. Kada ka la’anta mutanen nan, gama su masu albarka ne.”
Bog pa je rekel Bileámu: »Ne boš šel z njimi, ne boš preklel ljudstva, kajti blagoslovljeni so.«
13 Kashegari Bala’am ya tashi ya ce wa dattawan Balak, “Ku koma ƙasarku, domin Ubangiji ya hana ni in tafi tare da ku.”
Bileám je zjutraj vstal in Balákovim princem rekel: »Pojdite v svojo deželo, kajti Gospod mi odklanja dati dovoljenje, da grem z vami.«
14 Saboda haka dattawan Mowab suka koma wurin Balak suka ce, “Bala’am ya ƙi yă zo tare da mu.”
Moábski princi so vstali, odšli k Baláku in rekli: »Bileám odklanja, da pride z nami.«
15 Sai Balak ya aika waɗansu dattawa masu yawa, masu daraja kuma fiye da na dā.
Balák je ponovno poslal prince, več in častitljivejše od onih.
16 Suka zo wurin Bala’am suka ce, “Ga abin da Balak ɗan Ziffor ya ce, Kada ka bar wani abu yă hana ka zuwa wurina,
Prišli so k Bileámu in mu rekli: »Tako govori Cipórjev sin Balák: ›Naj te ničesar, prosim te, ne ovira, da bi prišel k meni,
17 gama zan ba ka lada mai yawa in kuma yi duk abin da ka ce. Ka zo ka la’anta mini waɗannan mutane.”
kajti povišal te bom v zelo veliko čast in storil bom kakorkoli mi rečeš. Pridi torej, prosim te, prekolni mi to ljudstvo.‹«
18 Amma Bala’am ya amsa musu ya ce, “Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba.
Bileám je odgovoril ter Balákovim služabnikom rekel: »Če bi mi Balák dal svojo hišo, polno srebra in zlata, ne morem iti preko besede od Gospoda, svojega Boga, da storim manj ali več.
19 To, fa, sai ku kwana a nan kamar yadda waɗancan suka yi, ni kuma in roƙi Ubangiji, in ji, wace magana zai ce mini.”
Zdaj torej, prosim vas, tudi vi ostanite tukaj to noč, da bom lahko vedel, kaj mi bo še povedal Gospod.«
20 A wannan dare, Allah ya zo wurin Bala’am ya ce, “Da yake waɗannan mutane sun zo su tafi da kai, to, ka tafi tare da su, sai dai ka yi abin da na ce ka yi ne kaɗai.”
Bog je ponoči prišel k Bileámu ter mu rekel: »Če pridejo možje, da te pokličejo, vstani in pojdi z njimi, toda reci jim samo besedo, ki ti jo bom jaz rekel, to boš storil.«
21 Bala’am ya tashi da safe, ya ɗaura wa jakarsa sirdi, ya tafi tare da dattawan Mowab.
Bileám je zjutraj vstal, osedlal svojo oslico in se odpravil k moábskim princem.
22 Amma Allah ya husata sa’ad da ya tafi, mala’ikan Ubangiji kuwa ya tsaya a hanya don yă hana shi. Bala’am kuwa yana kan jakarsa tare da bayinsa biyu.
Božja jeza je bila vžgana, ker je odšel in Gospodov angel je stal na poti za nasprotnika zoper njega. Torej jahal je na svoji oslici in dva njegova služabnika sta bila z njim.
23 Da jakar ta hangi mala’ikan Ubangiji tsaye a hanya da takobi a hannunsa, sai ta kauce daga hanya, ta shiga jeji. Bala’am kuwa ya buge ta don tă koma hanya.
In oslica je zagledala Gospodovega angela stati na poti in njegov meč je bil izvlečen v njegovi roki in oslica se je obrnila stran iz poti in odšla na polje. Bileám pa je udaril oslico, da jo obrne na pot.
24 Sai mala’ikan Ubangiji ya tsaya a wata matsattsiyar hanya tsakanin gonaki inabi biyu, da bango a kowane gefe.
Toda Gospodov angel je stal na stezi vinogradov, zid pa je bil na tej strani in zid na oni strani.
25 Sa’ad da jakar ta ga mala’ikan Ubangiji, sai ta matse a jikin bango, ta goge ƙafar Bala’am da bangon. Saboda haka sai Bala’am ya sāke bugunta.
Ko je oslica zagledala Gospodovega angela, se je pritisnila k zidu in Bileámovo stopalo zmečkala ob zid in ta jo je ponovno udaril.
26 Sai mala’ikan Ubangiji ya sha gabansa, ya tsaya a ƙunƙuntaccen wuri inda ba wurin juyawa dama ko hagu.
Gospodov angel je šel naprej in stal na ozkem kraju, kjer ni bilo nobene poti, da bi se obrnil k desni roki ali k levi.
27 Da jakar ta ga mala’ikan Ubangiji, sai ta kwanta a ƙasa, Bala’am kuwa ya husata, sai ya buge ta da sandansa.
Ko je oslica zagledala Gospodovega angela, je pod Bileámom padla dol in Bileámova jeza je bila vžgana in oslico je udaril s palico.
28 Ubangiji ya buɗe bakin jakar, sai jakar ta ce wa Bala’am, “Me na yi maka da ka buge ni har sau uku?”
Gospod pa je oslici odprl usta in ta je Bileámu rekla: »Kaj sem ti storila, da si me že trikrat udaril?«
29 Bala’am ya ce wa jakar “Domin kin wulaƙanta ni! Da a ce ina da takobi a hannuna da zan kashe ki nan take.”
Bileám je rekel oslici: »Ker si me zasmehovala. Če bi bil tukaj, v moji roki meč, bi te sedaj že ubil.«
30 Jakar ta ce wa Bala’am, “Ni ba jakarka ba ce wadda kake hawa kullum, har yă zuwa yau? Na taɓa yin maka haka?” Bala’am ya ce, “A’a.”
Oslica pa je Bileámu rekla: »Ali nisem tvoja oslica, na kateri si jahal, odkar sem bila tvoja, do današnjega dne? Sem imela kdaj navado, da ti tako storim?« Rekel je: »Ne.«
31 Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanun Bala’am, ya kuwa ga mala’ikan Ubangiji tsaye a hanya da takobi a zāre. Sai ya sunkuyar da kansa, ya fāɗi rubda ciki.
Potem je Gospod Bileámu odprl oči in zagledal je Gospodovega angela, stoječega na poti in njegov meč je bil izvlečen v njegovi roki. Sklonil je svojo glavo in padel plosko na svoj obraz.
32 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya tambaye shi, “Don me ka buge jakarka har sau uku? Na fito ne don in hana ka, gama hanyarka ba daidai ba ce a gabana.
Gospodov angel mu je rekel: »Zakaj si potem že trikrat udaril svojo oslico? Glej, odšel sem ven, da se ti zoperstavim, ker je tvoja pot sprevržena pred menoj,
33 Jakar ta gan ni, ta kauce mini har sau uku. Da a ce ba tă kauce ba, lalle da na kashe ka, in kuwa bar ta da rai.”
oslica pa me je zagledala in se že trikrat obrnila od mene. Razen če se ne bi obrnila od mene, bi te sedaj torej zagotovo ubil, njo pa rešil živo.«
34 Bala’am ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Na yi zunubi. Ban san ka tsaya a hanya don ka hana ni ba. Yanzu in ba ka ji daɗin tafiyata, sai in koma.”
Bileám je rekel Gospodovemu angelu: »Grešil sem, kajti nisem vedel, da zoper mene stojiš na poti. Sedaj torej, če te je to razžalilo, se bom ponovno vrnil nazaj.«
35 Mala’ikan Ubangiji ya ce wa Bala’am, “Ka tafi tare da mutanen, amma abin da na faɗa maka ne kaɗai za ka faɗa.” Saboda haka Bala’am ya tafi tare da dattawan Balak.
Gospodov angel je Bileámu rekel: »Pojdi z možmi, toda samo besedo, ki ti jo jaz govorim, to boš govoril.« Tako je Bileám odšel z Balákovimi princi.
36 Da Balak ya ji cewa Bala’am yana zuwa, sai ya fito, ya tarye shi a garin Mowabawa da suke a iyakar Arnon, a ƙarshen yankinsa.
Ko je Balák slišal, da je Bileám prišel, je odšel ven, da ga pospremi v mesto Moáb, ki je na meji Arnóna, ki je skrajna pokrajina.
37 Balak ya ce wa Bala’am, “Ban aika maka saƙo cikin gagawa ba? Me ya sa ba ka zo ba? Ko ban isa in sāka maka ba ne?”
Balák je rekel Bileámu: »Ali nisem iskreno poslal k tebi, da te pokličem? Čemu nisi prišel k meni? Mar te zares ne zmorem povišati k časti?«
38 Bala’am ya amsa ya ce, “To, ai, ga shi, na zo yanzu. Ina da wani ikon yin wata magana ne? Dole in faɗa abin da Allah ya ce in faɗa ne kawai.”
Bileám je rekel Baláku: »Glej, prišel sem k tebi. Imam zdaj sploh moč, da karkoli povem? Besedo, ki jo Bog polaga v moja usta, to bom govoril.«
39 Sa’an nan Bala’am ya tafi tare da Balak zuwa Kiriyat-Huzot,
Bileám je odšel z Balákom in prišla sta v Kirját Hucót.
40 a can ya yi hadaya da shanu da tumaki, ya kuwa aika wa Bala’am da dattawan da suke tare da shi.
Balák je daroval vola in ovco in poslal k Bileámu in k princem, ki so bili z njim.
41 Kashegari, Balak ya ɗauki Bala’am ya kai shi kan Bamot Ba’al, daga can ya iya ganin sassan sansanin Isra’ilawa.
Pripetilo se je naslednji dan, da je Balák vzel Bileáma in ga privedel gor na Báalov visok kraj, da bi od tam lahko videl skrajen del ljudstva.

< Ƙidaya 22 >