< Ƙidaya 22 >

1 Sai Isra’ilawa suka kama hanya, suka tafi filayen Mowab, a wajen Urdun, a ƙetare Yeriko, suka yi sansani a can.
And the children of Israel set forward, and encamped in the plains of Moab, on this side of the Jordan, opposite Jericho.
2 To, fa, Balak ɗan Ziffor ya ga duk abin da Isra’ila suka yi da Amoriyawa.
And Balak the son of Zippor saw all that Israel had done to the Emorites.
3 Sai Mowab ya firgita ƙwarai saboda yawan mutanen. Tsoron Isra’ilawa ya kama su.
And Moab was greatly afraid of the people, because it was numerous; and Moab was horrified because of the children of Israel.
4 Sai Mowabawa suka ce wa dattawan Midiyawa, “Wannan taron zai lashe duk abin da ya kewaye mu kamar yadda saniya takan lashe ciyawa a fili.” Saboda haka Balak ɗan Ziffor, wanda yake sarkin Mowab a lokacin,
And Moab said unto the elders of Midian, Now will this assemblage devour all that is round about us, as the ox devoureth the grass of the field; and Balak the son of Zippor was king of Moab at that time.
5 ya aika manzanni su zo da Bala’am ɗan Beyor, wanda yake a Fetor, kusa da Kogi, a ƙasar haihuwarsa. Balak ya ce, “Ga mutane sun fito daga Masar; sun mamaye ƙasar, suka kuma yi sansani kusa da ni.
And he sent messengers unto Bil'am the son of Beor to Pethor, which is by the river, in the land of the children of his people, to have him called; saying, Behold, there is a people come out from Egypt; behold, it covereth the surface of the earth, and it is abiding opposite to me:
6 Ka zo yanzu ka la’anta waɗannan mutane, domin sun fi ƙarfina. Wataƙila zan iya cin nasara a kansu, in kuma kore su daga ƙasar. Gama na sani duk waɗanda ka sa musu albarka, sun zama masu albarka ke nan, waɗanda kuma ka la’anta, sun la’antu ke nan.”
And now do but come, curse me this people; for it is too mighty for me; peradventure I may be able to smite it, that I may drive it out of the land; for I know that he whom thou blessest is blessed, and he whom thou cursest is cursed.
7 Sai dattawan Mowab da na Midiyawa suka tashi, suka ɗauki kuɗi don duba. Da suka zo wurin Bala’am sai suka faɗa masa abin da Balak ya ce.
And the elders of Moab and the elders of Midian departed with the rewards of divination in their hand; and they came unto Bil'am, and spoke unto him the words of Balak.
8 Bala’am ya ce musu, “Ku kwana a nan, ni kuwa zan faɗa muku abin da Ubangiji ya faɗa mini.” Saboda haka dattawan sarkin Mowab suka zauna da shi.
And he said unto them, Remain you here this night, and I will bring you word again, as the Lord may speak unto me; and the princes of Moab abode with Bil'am.
9 Sai Allah ya zo wurin Bala’am ya ce, “Su wane ne waɗannan tare da kai?”
And God came unto Bil'am, and said, Who are these men with thee?
10 Bala’am ya ce wa Allah, “Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab ne, ya aiko mini wannan saƙo cewa,
And Bil'am said unto God, Balak the son of Zippor, the king of Moab, hath sent unto me, [saying, ]
11 ‘Ga mutane sun fito daga Masar sun mamaye ƙasar. Ka zo yanzu ka la’anta mini su. Wataƙila ta haka zan yi nasara a kansu, in kuma kore su.’”
Behold, there is the people that is come out of Egypt, and covereth the face of the earth: now come, denounce it for me; peradventure I shall be able to fight against it, and drive it away.
12 Amma Allah ya ce wa Bala’am, “Kada ka tafi tare da su. Kada ka la’anta mutanen nan, gama su masu albarka ne.”
And God said unto Bil'am, Thou shalt not go with them: thou shalt not curse the people; for it is blessed.
13 Kashegari Bala’am ya tashi ya ce wa dattawan Balak, “Ku koma ƙasarku, domin Ubangiji ya hana ni in tafi tare da ku.”
And Bil'am rose up in the morning, and said unto the princes of Balak, Go back to your land; for the Lord refuseth to give me leave to go with you.
14 Saboda haka dattawan Mowab suka koma wurin Balak suka ce, “Bala’am ya ƙi yă zo tare da mu.”
And the princes of Moab rose up, and they went unto Balak, and said, Bil'am refuseth to come with us.
15 Sai Balak ya aika waɗansu dattawa masu yawa, masu daraja kuma fiye da na dā.
And Balak sent yet again princes, more in number, and more honorable than those.
16 Suka zo wurin Bala’am suka ce, “Ga abin da Balak ɗan Ziffor ya ce, Kada ka bar wani abu yă hana ka zuwa wurina,
And they came to Bil'am, and said to him, Thus hath said Balak the son of Zippor, Do not suffer thyself, I pray thee, to be prevented from coming unto me;
17 gama zan ba ka lada mai yawa in kuma yi duk abin da ka ce. Ka zo ka la’anta mini waɗannan mutane.”
For I will honor thee greatly, and whatsoever thou mayest say unto me will I do: and only come, I pray thee, denounce me this people.
18 Amma Bala’am ya amsa musu ya ce, “Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba.
And Bil'am answered and said unto the servants of Balak, If Balak would give me his house full of silver and gold, I could not transgress the order of the Lord my God, to do a small or a great thing.
19 To, fa, sai ku kwana a nan kamar yadda waɗancan suka yi, ni kuma in roƙi Ubangiji, in ji, wace magana zai ce mini.”
And now, I pray you, tarry ye also here this night, that I may know what the Lord will farther speak with me.
20 A wannan dare, Allah ya zo wurin Bala’am ya ce, “Da yake waɗannan mutane sun zo su tafi da kai, to, ka tafi tare da su, sai dai ka yi abin da na ce ka yi ne kaɗai.”
And God came unto Bil'am at night, and said unto him, If to call thee the men have come, rise up, go with them; but only the word which I shall speak unto thee, that shalt thou do.
21 Bala’am ya tashi da safe, ya ɗaura wa jakarsa sirdi, ya tafi tare da dattawan Mowab.
And Bil'am rose up in the morning, and saddled his ass, and went with the princes of Moab.
22 Amma Allah ya husata sa’ad da ya tafi, mala’ikan Ubangiji kuwa ya tsaya a hanya don yă hana shi. Bala’am kuwa yana kan jakarsa tare da bayinsa biyu.
And the anger of God was kindled, because he went; and an angel of the Lord placed himself in the way to be a hindrance to him; and he was riding upon his ass, and his two servants were with him.
23 Da jakar ta hangi mala’ikan Ubangiji tsaye a hanya da takobi a hannunsa, sai ta kauce daga hanya, ta shiga jeji. Bala’am kuwa ya buge ta don tă koma hanya.
And the ass saw the angel of the Lord standing in the way, with his sword drawn in his hand; and the ass turned aside out of the way, and went into the field: and Bil'am smote the ass, to make her turn into the way.
24 Sai mala’ikan Ubangiji ya tsaya a wata matsattsiyar hanya tsakanin gonaki inabi biyu, da bango a kowane gefe.
But the angel of the Lord stepped into a path between the vineyards, [with] a wall on this side, and a wall on that side.
25 Sa’ad da jakar ta ga mala’ikan Ubangiji, sai ta matse a jikin bango, ta goge ƙafar Bala’am da bangon. Saboda haka sai Bala’am ya sāke bugunta.
And when the ass saw the angel of the Lord, she forced herself against the wall, and pressed Bil'am's foot against the wall: and he smote her again.
26 Sai mala’ikan Ubangiji ya sha gabansa, ya tsaya a ƙunƙuntaccen wuri inda ba wurin juyawa dama ko hagu.
And the angel of the Lord went yet farther, and stood in a narrow place, where there was no way to turn either to the right or to the left.
27 Da jakar ta ga mala’ikan Ubangiji, sai ta kwanta a ƙasa, Bala’am kuwa ya husata, sai ya buge ta da sandansa.
And when the ass saw the angel of the Lord, she lay down under Bil'am: whereupon Bil'am's anger was kindled, and he smote the ass with a stick.
28 Ubangiji ya buɗe bakin jakar, sai jakar ta ce wa Bala’am, “Me na yi maka da ka buge ni har sau uku?”
And the Lord opened the mouth of the ass, and she said unto Bil'am, What have I done unto thee, that thou hast smitten me these three times?
29 Bala’am ya ce wa jakar “Domin kin wulaƙanta ni! Da a ce ina da takobi a hannuna da zan kashe ki nan take.”
And Bil'am said unto the ass, Because thou hast mocked me: had I but a sword in my hand, I would assuredly have now killed thee.
30 Jakar ta ce wa Bala’am, “Ni ba jakarka ba ce wadda kake hawa kullum, har yă zuwa yau? Na taɓa yin maka haka?” Bala’am ya ce, “A’a.”
And the ass said unto Bil'am, Am not I thy ass, upon which thou hast ridden from thy commencement unto this day? was I ever wont to do so unto thee? and he said, No.
31 Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanun Bala’am, ya kuwa ga mala’ikan Ubangiji tsaye a hanya da takobi a zāre. Sai ya sunkuyar da kansa, ya fāɗi rubda ciki.
Then the Lord opened the eyes of Bil'am, and he saw the angel of the Lord standing in the way, with his sword drawn in his hand: and he bowed down his head and prostrated himself on his face.
32 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya tambaye shi, “Don me ka buge jakarka har sau uku? Na fito ne don in hana ka, gama hanyarka ba daidai ba ce a gabana.
And the angel of the Lord said unto him, Wherefore hast thou smitten thy ass these three times? behold, I went out to be a hindrance; because the journey which is odious to me was too quickly begun.
33 Jakar ta gan ni, ta kauce mini har sau uku. Da a ce ba tă kauce ba, lalle da na kashe ka, in kuwa bar ta da rai.”
And the ass saw me, and turned aside before me these three times; if she had not turned aside from me, I would surely now not only have slain thee, but saved her alive.
34 Bala’am ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Na yi zunubi. Ban san ka tsaya a hanya don ka hana ni ba. Yanzu in ba ka ji daɗin tafiyata, sai in koma.”
And Bil'am said unto the angel of the Lord, I have sinned; for I knew not that thou wast standing against me in the way; but now, if it be evil in thy eyes, I will return home again.
35 Mala’ikan Ubangiji ya ce wa Bala’am, “Ka tafi tare da mutanen, amma abin da na faɗa maka ne kaɗai za ka faɗa.” Saboda haka Bala’am ya tafi tare da dattawan Balak.
And the angel of the Lord said unto Bil'am, Go with the men; however, only the word which I will speak unto thee, that shalt thou speak: and Bil'am went with the princes of Balak.
36 Da Balak ya ji cewa Bala’am yana zuwa, sai ya fito, ya tarye shi a garin Mowabawa da suke a iyakar Arnon, a ƙarshen yankinsa.
And when Balak heard that Bil'am was come, he went out to meet him unto 'Ir-Moab, which is on the border of Arnon, which is at the outmost end of the boundary.
37 Balak ya ce wa Bala’am, “Ban aika maka saƙo cikin gagawa ba? Me ya sa ba ka zo ba? Ko ban isa in sāka maka ba ne?”
And Balak said unto Bil'am, Did I not earnestly send unto thee to have thee called? wherefore camest thou not unto me? in truth, am I not able to honor thee?
38 Bala’am ya amsa ya ce, “To, ai, ga shi, na zo yanzu. Ina da wani ikon yin wata magana ne? Dole in faɗa abin da Allah ya ce in faɗa ne kawai.”
And Bil'am said unto Balak, Lo, I am come unto thee; have I now any power whatever to speak the least? the word that God may put in my mouth, that alone must I speak.
39 Sa’an nan Bala’am ya tafi tare da Balak zuwa Kiriyat-Huzot,
And Bil'am went with Balak, and they came unto Kiryath-chuzoth.
40 a can ya yi hadaya da shanu da tumaki, ya kuwa aika wa Bala’am da dattawan da suke tare da shi.
And Balak slew oxen and sheep, and sent to Bil'am and to the princes that were with him.
41 Kashegari, Balak ya ɗauki Bala’am ya kai shi kan Bamot Ba’al, daga can ya iya ganin sassan sansanin Isra’ilawa.
And it came to pass in the morning, that Balak took Bil'am, and brought him up into the high places of Baal, and he saw thence a portion of the people.

< Ƙidaya 22 >