< Ƙidaya 21 >
1 Sa’ad da sarkin Arad, mutumin Kan’ana, wanda yake zaune a Negeb, da ya ji cewa Isra’ila yana zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fito, yă yaƙi Isra’ilawa, yă kuma kama waɗansunsu.
Et le Cananéen, Roi de Arad, qui résidait dans le Midi, apprit qu'Israël s'avançait par la route d'Atharim; et il attaqua Israël et lui enleva des prisonniers.
2 Sai Isra’ila suka yi alkawari wa Ubangiji suka ce, “In ka ba da waɗannan mutane a hannunmu, za mu hallaka dukan garuruwansu ƙaf.”
Alors Israël fit un vœu à l'Éternel et dit: Si tu livres ce peuple entre mes mains, je dévouerai ses villes.
3 Ubangiji kuwa ya saurari kukan Isra’ila, ya kuma ba da Kan’aniyawa a gare su. Suka hallaka su da biranensu ƙaf; saboda haka aka sa wa wurin suna Horma.
Et l'Éternel écouta la voix d'Israël, et livra les Cananéens, et on les dévoua eux et leurs villes, et ce lieu reçut le nom de Horma [lieu dévoué].
4 Suka kama hanya daga Dutsen Hor ta hanya zuwa Jan Teku, don su kauce wa Edom. Amma mutane suka rasa haƙuri a hanya;
Et ils partirent du mont Hor prenant la route de la Mer aux algues pour tourner le pays d'Edom. Et le peuple perdit patience en chemin,
5 suka yi wa Allah da Musa gunaguni, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu mu mutu a wannan hamada? Babu abinci! Babu ruwa! Mu dai mun gaji da wannan abinci marar amfani!”
et le peuple tint des discours contre Dieu et contre Moïse: Pourquoi nous as-tu tirés de l'Egypte et exposés à mourir dans le désert? car il n'y a ici ni pain ni eau, et ce vil aliment nous dégoûte.
6 Sai Ubangiji ya aiko da macizai masu dafin a cikinsu, suka sassari mutane, Isra’ilawa masu yawa kuwa suka mutu.
Alors l'Éternel envoya parmi le peuple des serpents venimeux, et les morsures qu'ils firent dans le peuple, donnèrent la mort à beaucoup de gens en Israël.
7 Mutanen suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi, da muka yi wa Ubangiji da kai gunaguni. Ka yi addu’a don Ubangiji yă ɗauke mana macizan nan.” Saboda haka Musa ya yi addu’a domin mutane.
Alors le peuple vint à Moïse et dit: Nous avons péché, car nous avons tenu des discours contre l'Éternel et contre toi; intercède, auprès de l'Éternel pour qu'il éloigne de nous ces serpents. Et Moïse intercéda en faveur du peuple.
8 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera siffar maciji ka rataye shi a bisa doguwar sanda; kowa da maciji ya sare shi, idan ya dubi macijin nan da ka rataye, zai rayu.”
Et l'Éternel dit à Moïse: Fais-toi un serpent et place-le au haut d'une perche, et il arrivera que quiconque aura été mordu et le regardera, reprendra vie.
9 Saboda haka Musa ya ƙera macijin tagulla, ya kuma rataye shi bisa doguwar sanda. Sa’an nan duk wanda maciji ya sare shi, ya kuma dubi macijin tagullar, zai warke.
Alors Moïse fit un serpent d'airain, et il le plaça au haut d'une perche, et il arrivait que celui qui avait été mordu par un serpent et regardait vers le serpent d'airain, reprenait vie.
10 Isra’ilawa suka kama hanya, suka yi sansani a Obot.
Et les enfants d'Israël partirent et vinrent camper à Oboth.
11 Sai suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim a hamadar da take fuskantar Mowab, wajen fitowar rana.
Et ayant quitté Oboth, ils vinrent camper à Ijei-Abarim dans le désert situé à l'Orient de Moab du côté du soleil levant.
12 Daga nan kuma suka ci gaba, suka yi sansani a Kwarin Zered.
Étant partis de là ils vinrent camper dans la vallée de Zared.
13 Suka tashi daga nan, suka sauka kusa da Arnon wanda yake a hamadar da ta miƙe zuwa iyakar Amoriyawa. Arnon shi ne iyakar Mowab, wanda yake tsakanin Mowab da Amoriyawa.
Étant partis de là ils vinrent camper au delà de l'Arnon qui coule dans le désert après sa sortie du territoire des Amoréens; car l'Arnon est la limite de Moab, entre Moab et les Amoréens.
14 Shi ya sa Littafin Yaƙoƙin Ubangiji ya ce, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na tuddan Arnon,
C'est pourquoi il, est dit dans le Livre des Combats de l'Éternel: Vaheb en Sufa et les torrents d'Arnon
15 da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”
et l'épanchement des torrents, qui tourne vers la Résidence d'Ar, et s'appuie aux confins de Moab.
16 Daga can, suka gangara zuwa Beyer, wato, rijiyar da Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane duka, zan kuwa ba su ruwa.”
Et de là ils vinrent à Béer (puits). C'est le puits où l'Éternel dit à Moïse: Assemble le peuple, et je leur donnerai de l'eau.
17 Sai Isra’ilawa suka rera wannan waƙa, “Ki ɓuɓɓugo da ruwa, Ke rijiya! Rera waƙa game da ita,
Alors Israël chanta ce cantique: Jaillis, fontaine! Acclamez-la!
18 game da rijiyar da’ya’yan sarki suka haƙa, rijiyar da manyan mutane masu sandunan sarauta suka nuna da sandunansu.” Sa’an nan suka tashi daga hamadar, suka tafi Mattana,
fontaine creusée par des princes, qu'ont fouie les chefs du peuple avec le sceptre et leurs bâtons!
19 daga Mattana, suka tafi Nahaliyel, daga Nahaliyel, suka tafi Bamot,
Et du désert on vint à Mathana, et de Mathana à Nahaliel, et de Nahaliel à Bamoth;
20 daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake cikin Mowab inda ƙwanƙolin Fisga yake fuskantar hamada.
et de Bamoth à la vallée située dans le pays de Moab, au sommet du Pisga qui domine la plaine du désert.
21 Isra’ila suka aiki manzanni wurin Sihon sarkin Amoriyawa su ce,
Et Israël, envoya des messagers à Sihon, Roi, des Amoréens, pour lui dire:
22 “Ka bari mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu shiga wata gona ba, ba za mu kuma shiga gonar inabi, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babbar hanyar sarki, har mu fita ƙasarka.”
Laisse-moi, passer par ton pays; nous ne nous répandrons point dans les champs et les vignes, ne boirons point l'eau des puits; nous suivrons la route royale jusqu'à ce que nous ayons passé ta frontière.
23 Amma Sihon bai bar Isra’ila su ratsa ta yankinsa ba. Sai ya tara dukan sojojinsa, suka fita zuwa cikin hamada, su yaƙi Isra’ila. Da ya kai Yahaz, sai ya yaƙi Isra’ila.
Mais Sihon n'accorda pas à Israël le passage sur son territoire, et Sihon rassembla tout son peuple et marcha à la rencontre d'Israël du côté du désert, et pénétra jusqu'à Jahats et livra bataille à Israël.
24 Isra’ila fa suka kashe shi da takobi, suka ƙwace ƙasarsa, tun daga kogin Arnon har zuwa kogin Yabbok, zuwa kan iyakar Ammonawa kawai, gama sun yi wa iyakansu katanga.
Et Israël le battit, avec le tranchant de l'épée et conquit son pays de l'Arnon au Jabbok, jusqu'aux Ammonites; car la frontière des Ammonites était fortifiée.
25 Isra’ila suka ci dukan biranen Amoriyawa, suka kuma zauna a cikinsu, haɗe da babban birnin Heshbon da dukan ƙauyukanta.
Et Israël occupa toutes ces villes, et s'établit dans toutes les villes des Amoréens, à Hesbon et dans toutes ses dépendances.
26 Sihon sarkin Amoriyawa ya yi mulkin Heshbon, bayan ya ci sarkin Mowab na dā da yaƙi, ya kuma ƙwace dukan ƙasarsa har zuwa arewancin kogin Arnon.
Car Hesbon était la ville de Sihon, Roi des Amoréens, et il avait fait la guerre au précédent roi de Moab et lui avait pris tout son pays jusqu'à l'Arnon.
27 Shi ya sa Amoriyawa suka rubuta wannan waƙa game da Heshbon suka ce, “Ku zo mu sāke gina Heshbon, birnin Sihon.
C'est pourquoi les poètes disent: Entrez dans Hesbon! Qu'on relève et fortifie la cité de Sihon!
28 “Mayaƙansa sun fito kamar harshen wuta suka ƙone birnin Ar na Mowab suna hallaka’yan ƙasar tuddan Arnon.
Car un feu est sorti de Hesbon, Une flamme de la cité de Sihon: Il a dévoré le fort de Moab, Des maîtres des hauteurs de l'Arnon.
29 Kaitonki, Mowab! Gunkinki Kemosh ya yashe mutanenki; aka kuma kama su, aka kai su bauta wajen Sihon sarkin Amoriyawa.
Malheur à toi, Moab! C'en est fait de toi, peuple de Camos! De ses fils il a fait des fugitifs Et de ses filles des captives de Sihon, Roi des Amoréens…
30 “Amma mun tumɓuke su, mun hallaka garuruwan Heshbon har zuwa Dibon. Mun ragargaza su har zuwa Nofa wanda ya miƙe zuwa Medeba.”
Nous lançâmes nos traits, … Hesbon est détruite jusqu'à Dibon, et nous ravageâmes jusqu'à Nopha, l'incendie atteignit Médéba.
31 Ta haka Isra’ila suka zauna a ƙasar Amoriyawa.
Et pendant le séjour d'Israël dans le pays des Amoréens
32 Sai Musa ya aika’yan leƙen asiri zuwa Yazer. Daga baya, sai Isra’ilawa suka ci ƙauyukan da suke kewaye, suka kuma kori Amoriyawa da suke zaune a can.
Moïse envoya reconnaître Jaëzer, et ils s'emparèrent de ses dépendances, et il expulsa les Amoréens qui y étaient.
33 Sai suka juya suka haura kan hanya ta zuwa Bashan, inda Og yake sarauta, ya kuwa fito tare da dukan sojojinsa suka yi yaƙi da Isra’ila a Edireyi.
Et se détournant, ils montèrent du côté de Basan, et Og, Roi de Basan, vint à leur rencontre, lui et tout son peuple, pour les attaquer, à Edreï.
34 Ubangiji ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na ba da shi a gare ka, da dukan sojojinsa da kuma ƙasarsa. Ka yi da shi yadda ka yi da Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon.”
Alors l'Éternel dit à Moïse: Ne le crains pas; car je le livre entre tes mains, lui et tout son peuple et son pays, et tu le traiteras comme tu as traité Sihon, roi des Amoréens qui résidait à Hesbon.
35 Ta haka suka kashe shi, tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa, ba wanda ya ragu. Suka kuma mamaye ƙasarsa.
Et ils le battirent lui et ses fils et tout son peuple jusqu'à ne pas lui laisser un réchappé, et ils occupèrent son pays.