< Ƙidaya 21 >
1 Sa’ad da sarkin Arad, mutumin Kan’ana, wanda yake zaune a Negeb, da ya ji cewa Isra’ila yana zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fito, yă yaƙi Isra’ilawa, yă kuma kama waɗansunsu.
Le Cananéen, roi d'Arad, qui habitait dans le Midi, apprit qu'Israël venait par le chemin d'Atharim. Il fit la guerre à Israël et fit prisonniers quelques-uns de ses habitants.
2 Sai Isra’ila suka yi alkawari wa Ubangiji suka ce, “In ka ba da waɗannan mutane a hannunmu, za mu hallaka dukan garuruwansu ƙaf.”
Israël fit un vœu à Yahvé et dit: « Si tu livres ce peuple entre mes mains, je détruirai ses villes par interdit. »
3 Ubangiji kuwa ya saurari kukan Isra’ila, ya kuma ba da Kan’aniyawa a gare su. Suka hallaka su da biranensu ƙaf; saboda haka aka sa wa wurin suna Horma.
L'Éternel écouta la voix d'Israël et livra les Cananéens, qui furent dévoués par interdit, eux et leurs villes. Le nom du lieu s'appelait Horma.
4 Suka kama hanya daga Dutsen Hor ta hanya zuwa Jan Teku, don su kauce wa Edom. Amma mutane suka rasa haƙuri a hanya;
Ils partirent de la montagne de Hor, sur le chemin de la mer Rouge, pour contourner le pays d'Édom. L'âme du peuple était très découragée à cause du voyage.
5 suka yi wa Allah da Musa gunaguni, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu mu mutu a wannan hamada? Babu abinci! Babu ruwa! Mu dai mun gaji da wannan abinci marar amfani!”
Le peuple parlait contre Dieu et contre Moïse: « Pourquoi nous as-tu fait monter hors d'Égypte pour que nous mourions dans le désert? Car il n'y a pas de pain, il n'y a pas d'eau, et notre âme a horreur de cette nourriture dégoûtante! ».
6 Sai Ubangiji ya aiko da macizai masu dafin a cikinsu, suka sassari mutane, Isra’ilawa masu yawa kuwa suka mutu.
L'Éternel envoya des serpents venimeux parmi le peuple, et ils mordirent le peuple. Beaucoup de gens d'Israël moururent.
7 Mutanen suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi, da muka yi wa Ubangiji da kai gunaguni. Ka yi addu’a don Ubangiji yă ɗauke mana macizan nan.” Saboda haka Musa ya yi addu’a domin mutane.
Le peuple vint trouver Moïse et dit: « Nous avons péché, car nous avons parlé contre l'Éternel et contre toi. Prie Yahvé pour qu'il éloigne de nous les serpents. » Moïse pria pour le peuple.
8 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera siffar maciji ka rataye shi a bisa doguwar sanda; kowa da maciji ya sare shi, idan ya dubi macijin nan da ka rataye, zai rayu.”
Yahvé dit à Moïse: « Fais un serpent venimeux et place-le sur un poteau. Tous ceux qui seront mordus, quand ils le verront, vivront. »
9 Saboda haka Musa ya ƙera macijin tagulla, ya kuma rataye shi bisa doguwar sanda. Sa’an nan duk wanda maciji ya sare shi, ya kuma dubi macijin tagullar, zai warke.
Moïse fit un serpent d'airain, et le plaça sur le poteau. Si un homme avait été mordu par un serpent, lorsqu'il regardait le serpent d'airain, il vivait.
10 Isra’ilawa suka kama hanya, suka yi sansani a Obot.
Les enfants d'Israël partirent, et ils campèrent à Oboth.
11 Sai suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim a hamadar da take fuskantar Mowab, wajen fitowar rana.
Ils partirent d`Oboth, et campèrent à Iyeabarim, dans le désert qui est devant Moab, vers le soleil levant.
12 Daga nan kuma suka ci gaba, suka yi sansani a Kwarin Zered.
De là, ils partirent, et campèrent dans la vallée de Zered.
13 Suka tashi daga nan, suka sauka kusa da Arnon wanda yake a hamadar da ta miƙe zuwa iyakar Amoriyawa. Arnon shi ne iyakar Mowab, wanda yake tsakanin Mowab da Amoriyawa.
De là, ils partirent et campèrent de l'autre côté de l'Arnon, dans le désert qui sort de la frontière des Amoréens; car l'Arnon est la frontière de Moab, entre Moab et les Amoréens.
14 Shi ya sa Littafin Yaƙoƙin Ubangiji ya ce, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na tuddan Arnon,
C'est pourquoi il est dit dans le Livre des Guerres de Yahvé: « Vaheb à Supha, les vallées de l'Arnon,
15 da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”
le versant des vallées qui s'inclinent vers la demeure d'Ar, s'appuie sur la frontière de Moab. »
16 Daga can, suka gangara zuwa Beyer, wato, rijiyar da Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane duka, zan kuwa ba su ruwa.”
De là, ils allèrent jusqu'à Beer; c'est le puits dont Yahvé avait dit à Moïse: « Rassemblez le peuple, et je leur donnerai de l'eau. »
17 Sai Isra’ilawa suka rera wannan waƙa, “Ki ɓuɓɓugo da ruwa, Ke rijiya! Rera waƙa game da ita,
Alors Israël chanta ce cantique: « Ressort, bien! Chantez pour lui,
18 game da rijiyar da’ya’yan sarki suka haƙa, rijiyar da manyan mutane masu sandunan sarauta suka nuna da sandunansu.” Sa’an nan suka tashi daga hamadar, suka tafi Mattana,
le puits, que les princes ont creusé, que les nobles du peuple ont creusé, avec le sceptre, et avec leurs bâtons. » Ils partirent du désert pour aller à Mattana,
19 daga Mattana, suka tafi Nahaliyel, daga Nahaliyel, suka tafi Bamot,
puis de Mattana à Nahaliel, de Nahaliel à Bamoth,
20 daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake cikin Mowab inda ƙwanƙolin Fisga yake fuskantar hamada.
puis de Bamoth à la vallée qui est dans le champ de Moab, au sommet du Pisga, qui domine le désert.
21 Isra’ila suka aiki manzanni wurin Sihon sarkin Amoriyawa su ce,
Israël envoya des messagers à Sihon, roi des Amoréens, pour lui dire:
22 “Ka bari mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu shiga wata gona ba, ba za mu kuma shiga gonar inabi, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babbar hanyar sarki, har mu fita ƙasarka.”
« Laisse-moi passer par ton pays. Nous ne nous détournerons ni des champs ni des vignes. Nous ne boirons pas l'eau des puits. Nous suivrons la route royale, jusqu'à ce que nous ayons dépassé ta frontière. »
23 Amma Sihon bai bar Isra’ila su ratsa ta yankinsa ba. Sai ya tara dukan sojojinsa, suka fita zuwa cikin hamada, su yaƙi Isra’ila. Da ya kai Yahaz, sai ya yaƙi Isra’ila.
Sihon ne permit pas à Israël de franchir sa frontière. Sihon rassembla tout son peuple, sortit contre Israël dans le désert et arriva à Jahaz. Il combattit Israël.
24 Isra’ila fa suka kashe shi da takobi, suka ƙwace ƙasarsa, tun daga kogin Arnon har zuwa kogin Yabbok, zuwa kan iyakar Ammonawa kawai, gama sun yi wa iyakansu katanga.
Israël le frappa du tranchant de l'épée et prit possession de son pays, depuis l'Arnon jusqu'au Jabbok, jusqu'aux enfants d'Ammon, car la frontière des enfants d'Ammon était fortifiée.
25 Isra’ila suka ci dukan biranen Amoriyawa, suka kuma zauna a cikinsu, haɗe da babban birnin Heshbon da dukan ƙauyukanta.
Israël prit toutes ces villes. Israël habita dans toutes les villes des Amoréens, à Hesbon et dans tous ses villages.
26 Sihon sarkin Amoriyawa ya yi mulkin Heshbon, bayan ya ci sarkin Mowab na dā da yaƙi, ya kuma ƙwace dukan ƙasarsa har zuwa arewancin kogin Arnon.
Car Hesbon était la ville de Sihon, roi des Amoréens, qui avait combattu le précédent roi de Moab et lui avait enlevé tout son pays, jusqu'à l'Arnon.
27 Shi ya sa Amoriyawa suka rubuta wannan waƙa game da Heshbon suka ce, “Ku zo mu sāke gina Heshbon, birnin Sihon.
C'est pourquoi ceux qui parlent en proverbes disent, « Viens à Heshbon. Que la ville de Sihon soit bâtie et établie;
28 “Mayaƙansa sun fito kamar harshen wuta suka ƙone birnin Ar na Mowab suna hallaka’yan ƙasar tuddan Arnon.
car un feu est sorti de Heshbon, une flamme de la ville de Sihon. Elle a dévoré Ar de Moab, Les seigneurs des hauts lieux de l'Arnon.
29 Kaitonki, Mowab! Gunkinki Kemosh ya yashe mutanenki; aka kuma kama su, aka kai su bauta wajen Sihon sarkin Amoriyawa.
Malheur à toi, Moab! Vous êtes défaits, peuple de Chemosh! Il a donné ses fils comme fugitifs, et ses filles en captivité, à Sihon, roi des Amorites.
30 “Amma mun tumɓuke su, mun hallaka garuruwan Heshbon har zuwa Dibon. Mun ragargaza su har zuwa Nofa wanda ya miƙe zuwa Medeba.”
Nous leur avons tiré dessus. Heshbon a péri jusqu'à Dibon. Nous avons dévasté jusqu'à Nophah, Qui va jusqu'à Medeba. »
31 Ta haka Isra’ila suka zauna a ƙasar Amoriyawa.
Israël habita ainsi dans le pays des Amoréens.
32 Sai Musa ya aika’yan leƙen asiri zuwa Yazer. Daga baya, sai Isra’ilawa suka ci ƙauyukan da suke kewaye, suka kuma kori Amoriyawa da suke zaune a can.
Moïse envoya espionner Jazer. Ils prirent ses villages, et chassèrent les Amoréens qui s'y trouvaient.
33 Sai suka juya suka haura kan hanya ta zuwa Bashan, inda Og yake sarauta, ya kuwa fito tare da dukan sojojinsa suka yi yaƙi da Isra’ila a Edireyi.
Ils se retournèrent et montèrent par le chemin de Basan. Og, roi de Basan, sortit contre eux, lui et tout son peuple, pour combattre à Édréi.
34 Ubangiji ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na ba da shi a gare ka, da dukan sojojinsa da kuma ƙasarsa. Ka yi da shi yadda ka yi da Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon.”
Yahvé dit à Moïse: « Ne le crains pas, car je l'ai livré entre tes mains, avec tout son peuple et son pays. Tu lui feras ce que tu as fait à Sihon, roi des Amorites, qui habitait à Heshbon. »
35 Ta haka suka kashe shi, tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa, ba wanda ya ragu. Suka kuma mamaye ƙasarsa.
Et ils le frappèrent, ainsi que ses fils et tout son peuple, jusqu'à ce qu'il n'y ait plus de survivants; et ils possédèrent son pays.