< Ƙidaya 21 >

1 Sa’ad da sarkin Arad, mutumin Kan’ana, wanda yake zaune a Negeb, da ya ji cewa Isra’ila yana zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fito, yă yaƙi Isra’ilawa, yă kuma kama waɗansunsu.
Men da Kana'anæeren, Kongen af Arad, der boede i Sydlandet, hørte, at Israel rykkede frem ad Atarimvejen, angreb han Israel og tog nogle af dem til Fange.
2 Sai Isra’ila suka yi alkawari wa Ubangiji suka ce, “In ka ba da waɗannan mutane a hannunmu, za mu hallaka dukan garuruwansu ƙaf.”
Da aflagde Israel et Løfte til HERREN og sagde: »Hvis du giver dette Folk i min Haand, vil jeg lægge Band paa deres Byer!«
3 Ubangiji kuwa ya saurari kukan Isra’ila, ya kuma ba da Kan’aniyawa a gare su. Suka hallaka su da biranensu ƙaf; saboda haka aka sa wa wurin suna Horma.
Og HERREN hørte Israels Røst og gav Kana'anæerne i deres Haand, hvorefter de lagde Band paa dem og deres Byer. Derfor gav man Stedet Navnet Horma.
4 Suka kama hanya daga Dutsen Hor ta hanya zuwa Jan Teku, don su kauce wa Edom. Amma mutane suka rasa haƙuri a hanya;
Saa brød de op fra Bjerget Hor i Retning af det røde Hav for at komme uden om Edoms Land. Undervejs blev Folket utaalmodigt
5 suka yi wa Allah da Musa gunaguni, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu mu mutu a wannan hamada? Babu abinci! Babu ruwa! Mu dai mun gaji da wannan abinci marar amfani!”
og talte mod Gud og Moses og sagde: »Hvorfor førte I os ud af Ægypten, naar vi skal dø i Ørkenen? Her er jo hverken Brød eller Vand, og vi er lede ved denne usle Føde.«
6 Sai Ubangiji ya aiko da macizai masu dafin a cikinsu, suka sassari mutane, Isra’ilawa masu yawa kuwa suka mutu.
Da sendte HERREN Giftslanger blandt Folket, og de bed Folket saa en Mængde af Israel døde.
7 Mutanen suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi, da muka yi wa Ubangiji da kai gunaguni. Ka yi addu’a don Ubangiji yă ɗauke mana macizan nan.” Saboda haka Musa ya yi addu’a domin mutane.
Saa kom Folket til Moses og sagde: »Vi har syndet ved at tale imod HERREN og dig; gaa i Forbøn hos HERREN, at han tager Slangerne fra os!« Og Moses gik i Forbøn for Folket.
8 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera siffar maciji ka rataye shi a bisa doguwar sanda; kowa da maciji ya sare shi, idan ya dubi macijin nan da ka rataye, zai rayu.”
Da sagde HERREN til Moses: »Lav dig en Slange og sæt den paa en Stang, saa skal enhver slangebidt, der ser hen paa den, leve!«
9 Saboda haka Musa ya ƙera macijin tagulla, ya kuma rataye shi bisa doguwar sanda. Sa’an nan duk wanda maciji ya sare shi, ya kuma dubi macijin tagullar, zai warke.
Da lavede Moses en Kobberslange og satte den paa en Stang; og enhver, der saa hen paa Kobberslangen, naar en Slange havde bidt ham, beholdt Livet.
10 Isra’ilawa suka kama hanya, suka yi sansani a Obot.
Saa brød Israeliterne op og slog Lejr i Obot;
11 Sai suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim a hamadar da take fuskantar Mowab, wajen fitowar rana.
og de brød op fra Obot og slog Lejr i Ijje-Ha'abarim i Ørkenen østen for Moab.
12 Daga nan kuma suka ci gaba, suka yi sansani a Kwarin Zered.
Derfra brød de op og slog Lejr i Zereddalen.
13 Suka tashi daga nan, suka sauka kusa da Arnon wanda yake a hamadar da ta miƙe zuwa iyakar Amoriyawa. Arnon shi ne iyakar Mowab, wanda yake tsakanin Mowab da Amoriyawa.
Derfra brød de op og slog Lejr i Ørkenen hinsides Arnon, som udspringer paa Amoriternes Omraade, thi Arnon var Moabs Grænse mod Amoriterne.
14 Shi ya sa Littafin Yaƙoƙin Ubangiji ya ce, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na tuddan Arnon,
Derfor hedder det i Bogen om HERRENS Krige: .... Vaheb i Sufa og Dalene, Arnon og Dalenes Skrænt,
15 da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”
som strækker sig til Ars Sæde og læner sig til Moabs Grænse.
16 Daga can, suka gangara zuwa Beyer, wato, rijiyar da Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane duka, zan kuwa ba su ruwa.”
Derfra brød de op til Be'er; det er det Be'er, HERREN havde for Øje, da han sagde til Moses: »Kald Folket sammen, saa vil jeg give dem Vand!«
17 Sai Isra’ilawa suka rera wannan waƙa, “Ki ɓuɓɓugo da ruwa, Ke rijiya! Rera waƙa game da ita,
Da sang Israeliterne denne Sang: Brønd, væld frem! Syng til dens Pris!
18 game da rijiyar da’ya’yan sarki suka haƙa, rijiyar da manyan mutane masu sandunan sarauta suka nuna da sandunansu.” Sa’an nan suka tashi daga hamadar, suka tafi Mattana,
Brønd, som Høvdinger grov, som Folkets ædle bored med Herskerspir og Stave! Fra Ørkenen brød de op til Mattana;
19 daga Mattana, suka tafi Nahaliyel, daga Nahaliyel, suka tafi Bamot,
fra Mattana til Nahaliel; fra Nahaliel til Bamot;
20 daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake cikin Mowab inda ƙwanƙolin Fisga yake fuskantar hamada.
fra Bamot til Dalen paa Moabs Højslette, til Pisgas Top, som rager op over Ørkenen.
21 Isra’ila suka aiki manzanni wurin Sihon sarkin Amoriyawa su ce,
Israel sendte nu Sendebud til Amoriterkongen Sihon og lod sige:
22 “Ka bari mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu shiga wata gona ba, ba za mu kuma shiga gonar inabi, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babbar hanyar sarki, har mu fita ƙasarka.”
»Lad mig faa Lov at drage igennem dit Land! Vi vil ikke dreje ind paa Marker eller i Vinhaver, vi vil ikke drikke Vand af Brøndene, vi vil følge Kongevejen, indtil vi er naaet igennem dit Land!«
23 Amma Sihon bai bar Isra’ila su ratsa ta yankinsa ba. Sai ya tara dukan sojojinsa, suka fita zuwa cikin hamada, su yaƙi Isra’ila. Da ya kai Yahaz, sai ya yaƙi Isra’ila.
Men Sihon tillod ikke Israel at drage igennem sit Land; derimod samlede han alt sit Krigsfolk og rykkede ud i Ørkenen imod Israel, og da han naaede Jaza, angreb han Israel.
24 Isra’ila fa suka kashe shi da takobi, suka ƙwace ƙasarsa, tun daga kogin Arnon har zuwa kogin Yabbok, zuwa kan iyakar Ammonawa kawai, gama sun yi wa iyakansu katanga.
Men Israel slog ham med Sværdet og underlagde sig hans Land fra Arnon til Jabbok, til Ammoniternes Land; thi Ja'zer ligger ved Ammoniternes Grænse;
25 Isra’ila suka ci dukan biranen Amoriyawa, suka kuma zauna a cikinsu, haɗe da babban birnin Heshbon da dukan ƙauyukanta.
og Israel indtog alle disse Byer, og Israel bosatte sig i alle Amoriternes Byer, i Hesjbon og alle tilhørende Smaabyer.
26 Sihon sarkin Amoriyawa ya yi mulkin Heshbon, bayan ya ci sarkin Mowab na dā da yaƙi, ya kuma ƙwace dukan ƙasarsa har zuwa arewancin kogin Arnon.
Thi Hesjbon var Amoriterkongen Sihons By; han havde angrebet Moabs forrige Konge og frataget ham hele hans Land indtil Arnon.
27 Shi ya sa Amoriyawa suka rubuta wannan waƙa game da Heshbon suka ce, “Ku zo mu sāke gina Heshbon, birnin Sihon.
Derfor synger Skjaldene: Kom hid til Hesjbon, lad den blive bygget og grundfæstet, Sihons By!
28 “Mayaƙansa sun fito kamar harshen wuta suka ƙone birnin Ar na Mowab suna hallaka’yan ƙasar tuddan Arnon.
Thi Ild for ud fra Hesjbon, Ildslue fra Sihons Stad, den fortærede Moabs Byer, opaad Arnons Højder.
29 Kaitonki, Mowab! Gunkinki Kemosh ya yashe mutanenki; aka kuma kama su, aka kai su bauta wajen Sihon sarkin Amoriyawa.
Ve dig, Moab! Det er ude med dig, Kemosj's Folk! Han gjorde sine Sønner til Flygtninge og sine Døtre til Krigsfanger for Sihon, Amoriternes Konge.
30 “Amma mun tumɓuke su, mun hallaka garuruwan Heshbon har zuwa Dibon. Mun ragargaza su har zuwa Nofa wanda ya miƙe zuwa Medeba.”
Og vi skød dem ned, Hesjbon er tabt indtil Dibon; vi lagde dem øde til Nofa, som ligger ved Medeba.
31 Ta haka Isra’ila suka zauna a ƙasar Amoriyawa.
Saa bosatte Israel sig i Amoriternes Land.
32 Sai Musa ya aika’yan leƙen asiri zuwa Yazer. Daga baya, sai Isra’ilawa suka ci ƙauyukan da suke kewaye, suka kuma kori Amoriyawa da suke zaune a can.
Derpaa sendte Moses Spejdere til Ja'zer; og de erobrede det tillige med tilhørende Smaabyer, og han drev de der boende Amoriter bort.
33 Sai suka juya suka haura kan hanya ta zuwa Bashan, inda Og yake sarauta, ya kuwa fito tare da dukan sojojinsa suka yi yaƙi da Isra’ila a Edireyi.
Derpaa vendte de om og drog ad Basan til. Da rykkede Og, Kongen af Basan, ud imod dem med alle sine Krigere og angreb dem ved Edre'i.
34 Ubangiji ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na ba da shi a gare ka, da dukan sojojinsa da kuma ƙasarsa. Ka yi da shi yadda ka yi da Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon.”
Men HERREN sagde til Moses: »Frygt ikke for ham! Thi jeg giver ham og alle hans Krigere og hans Land i din Haand, saa at du kan handle med ham, som du handlede med Amoriterkongen Sihon, der boede i Hesjbon.«
35 Ta haka suka kashe shi, tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa, ba wanda ya ragu. Suka kuma mamaye ƙasarsa.
Da slog de ham og hans Sønner og alle hans Krigere, saa at ikke en eneste af dem undslap, og derpaa underlagde de sig hans Land.

< Ƙidaya 21 >