< Ƙidaya 20 >

1 A watan fari, dukan jama’ar Isra’ilawa suka iso Hamadan Zin. Suka sauka a Kadesh. A nan ne Miriyam ta mutu, aka kuma bizne ta.
Les enfants d'Israël, toute l'assemblée, arrivèrent dans le désert de Tsin, au premier mois. Le peuple resta à Kadès. C'est là que Miriam mourut et qu'on l'enterra.
2 Sai aka rasa ruwa da jama’a za su sha, mutane suka taru, suka tayar wa Musa da Haruna.
Il n'y avait pas d'eau pour l'assemblée; et ils s'assemblèrent contre Moïse et contre Aaron.
3 Suka yi gunaguni wa Musa suka ce, “Da ma mun mutu sa’ad da’yan’uwanmu suka mutu a gaban Ubangiji!
Le peuple se querella avec Moïse, et parla ainsi: « Nous aurions voulu mourir quand nos frères sont morts devant Yahvé!
4 Don me ka kawo jama’ar Ubangiji a wannan hamada, don mu da dabbobinmu mu mutu a nan ke nan?
Pourquoi as-tu fait venir l'assemblée de l'Éternel dans ce désert, pour que nous y mourions, nous et nos animaux?
5 Don me ka fitar da mu daga Masar zuwa wannan banzan wuri, inda babu hatsi ko ɓaure, inabi ko rumman. Kuma babu ruwan da za a sha?”
Pourquoi nous as-tu fait monter hors d'Égypte, pour nous amener dans ce mauvais lieu? Ce n'est pas un lieu de semence, ni de figues, ni de vignes, ni de grenades; il n'y a pas non plus d'eau à boire. »
6 Sai Musa da Haruna suka tashi daga taron, suka tafi ƙofar Tentin Sujada, suka fāɗi rubda ciki, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana musu.
Moïse et Aaron quittèrent la présence de l'assemblée pour se rendre à l'entrée de la tente de la Rencontre, et ils tombèrent sur leur visage. La gloire de Yahvé leur apparut.
7 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahvé parla à Moïse et dit:
8 “Ka ɗauki sandanka, kai da Haruna, ɗan’uwanka, ku tara jama’a, ku yi magana da dutsen a gabansu ya ba da ruwan da yake cikinsa. Za ka sa ruwa ya ɓuɓɓugo musu daga dutsen. Ta haka za ka ba taron jama’a da garkunansu ruwan sha.”
« Prends le bâton, rassemble l'assemblée, toi et Aaron, ton frère, et parle au rocher sous leurs yeux, pour qu'il verse son eau. Tu leur apporteras de l'eau du rocher, et tu feras boire l'assemblée et son bétail. »
9 Sai Musa ya je ya ɗauki sandan kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.
Moïse prit le bâton de devant l'Éternel, comme il le lui avait ordonné.
10 Shi da Haruna, suka tara jama’a a gaban dutsen, Musa ya ce musu, “Ku saurara, ku’yan tawaye, dole mu kawo muku ruwa daga wannan dutse?”
Moïse et Aaron rassemblèrent l'assemblée devant le rocher, et il leur dit: « Écoutez, rebelles! Faisons-nous sortir pour vous de l'eau de ce rocher? »
11 Sai Musa ya ɗaga hannu, ya bugi dutsen sau biyu da sandansa. Ruwa kuwa ya yi ta kwararowa, jama’a da dabbobinsu suka sha.
Moïse leva la main et frappa deux fois le rocher avec sa baguette, et de l'eau sortit en abondance. L'assemblée et son bétail burent.
12 Amma Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna. “Tun da yake ba ku gaskata ni ba, ba ku kuwa ɗaukaka ni a idon Isra’ilawa ba, to, ba za ku kai taron jama’an nan a ƙasar da na ba su ba.”
Yahvé dit à Moïse et à Aaron: « Parce que vous n'avez pas cru en moi, pour me sanctifier aux yeux des enfants d'Israël, vous ne ferez pas entrer cette assemblée dans le pays que je leur ai donné. »
13 Waɗannan su ne ruwan Meriba, inda Isra’ilawa suka yi wa Ubangiji gunaguni, inda kuma ya nuna kansa mai tsarki a cikinsu.
Ce sont les eaux de Meriba, parce que les enfants d'Israël ont lutté contre l'Éternel, et il a été sanctifié par elles.
14 Musa ya aiki manzanni daga Kadesh zuwa wurin sarkin Edom cewa, “Ga abin da ɗan’uwanka Isra’ila ya ce ka san duk irin wahalolin da ya same mu.
Moïse envoya des messagers de Kadès au roi d'Édom, en disant: « Ton frère Israël dit: Tu sais toutes les souffrances qui nous sont arrivées;
15 Kakanninmu sun gangaro zuwa Masar, muka zauna can shekaru da yawa. Masarawa suka wulaƙanta mu, da kuma kakanninmu,
comment nos pères sont descendus en Égypte, et nous avons vécu longtemps en Égypte. Les Égyptiens nous ont maltraités, nous et nos pères.
16 amma da muka yi kuka a gaban Ubangiji, ya kuwa ji mu, sai ya aiko mala’ika, ya fitar da mu daga Masar. “Yanzu ga mu a Kadesh, garin da yake kan iyakar yankinka.
Nous avons crié à Yahvé, qui a entendu notre voix, envoyé un ange et nous a fait sortir d'Égypte. Voici, nous sommes à Kadès, ville située à l'extrémité de ta frontière.
17 Muna roƙonka, ka yarda mana mu bi ta ƙasarka. Ba za mu bi ta wani fili, ko gonar inabi ba, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babban hanyar sarki, ba kuwa za mu kauce dama, ko hagu ba, har mu wuce yankinka.”
« Je vous en prie, laissez-nous passer dans votre pays. Nous ne passerons ni par les champs ni par les vignes, et nous ne boirons pas l'eau des puits. Nous suivrons la route du roi. Nous ne nous détournerons ni à droite ni à gauche, jusqu'à ce que nous ayons franchi votre frontière. »
18 Amma Edom ya amsa ya ce, “Ba za ku bi ta nan ba; in kuka kuskura, za mu fito, mu yaƙe ku da takobi.”
Édom lui dit: « Tu ne passeras pas par moi, de peur que je ne sorte l'épée contre toi. »
19 Sai Isra’ilawa suka amsa, suka ce, “Za mu bi ta babbar hanya, in mu, ko dabbobinmu suka sha ruwanku, za mu biya. Mu dai muna so mu wuce ne kawai.”
Les enfants d'Israël lui dirent: « Nous monterons par la grande route; et si nous buvons ton eau, moi et mon bétail, j'en donnerai le prix. Mais laisse-moi seulement, sans rien faire d'autre, passer sur mes pieds. »
20 Sai mutanen Edom suka sāke amsa suka ce, “Ba za ku bi nan ba dai.” Sai Edom ya fito da runduna mai ƙarfi da yawa gaske a kan Isra’ila.
Il dit: « Tu ne passeras pas. » Edom sortit contre lui avec un peuple nombreux et une main forte.
21 Da yake Edom suka ƙi su bar su su ratsa yankinsu, sai Isra’ila suka juya suka janye daga gare su.
Ainsi, Edom refusa de laisser passer Israël par sa frontière, et Israël se détourna de lui.
22 Dukan Jama’ar Isra’ilawa suka tashi daga Kadesh, suka zo Dutsen Hor.
Ils partirent de Kadès, et les enfants d'Israël, toute la congrégation, arrivèrent à la montagne de Hor.
23 A Dutsen Hor, kusa da iyakar Edom, Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
Yahvé parla à Moïse et à Aaron sur la montagne de Hor, à la frontière du pays d'Édom, et dit:
24 “Haruna zai rasu. Ba zai shiga ƙasar da na ba Isra’ilawa ba, domin ku biyu, kun ƙi ku bi umarnina a ruwan Meriba.
« Aaron sera recueilli auprès de son peuple, car il n'entrera pas dans le pays que j'ai donné aux enfants d'Israël, parce que vous vous êtes rebellés contre ma parole aux eaux de Meriba.
25 Ka kawo Haruna da ɗansa Eleyazar, ka kai su a bisan Dutsen Hor.
Prends Aaron et Éléazar, son fils, et fais-les monter sur la montagne de Hor.
26 Ka tuɓe taguwar Haruna ka sa wa ɗansa Eleyazar, gama Haruna zai rasu a can.”
Dépouille Aaron de ses vêtements, et mets-les sur Éléazar, son fils. Aaron sera recueilli, et c'est là qu'il mourra. »
27 Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarta. Suka hau Dutsen Hor a idon dukan jama’a.
Moïse fit ce que l'Éternel lui avait ordonné. Ils montèrent sur la montagne de Hor, sous les yeux de toute l'assemblée.
28 Musa ya tuɓe taguwar Haruna, ya kuma sa wa Eleyazar ɗan Haruna. Nan kuwa Haruna ya mutu a bisa dutsen. Sa’an nan Musa da Eleyazar suka sauka daga dutsen,
Moïse dépouilla Aaron de ses vêtements et les fit revêtir à son fils Éléazar. Aaron mourut là, au sommet de la montagne, et Moïse et Eléazar descendirent de la montagne.
29 sa’ad da dukan jama’a kuwa suka ji cewa Haruna ya mutu, sai dukan gidan Isra’ila suka yi makoki dominsa har kwana talatin.
Lorsque toute l'assemblée vit qu'Aaron était mort, ils pleurèrent Aaron pendant trente jours, toute la maison d'Israël.

< Ƙidaya 20 >