< Ƙidaya 20 >
1 A watan fari, dukan jama’ar Isra’ilawa suka iso Hamadan Zin. Suka sauka a Kadesh. A nan ne Miriyam ta mutu, aka kuma bizne ta.
And the sones of Israel and al the multitude camen in to the deseert of Syn, in the firste monethe. And the puple dwellide in Cades; and Marie was deed there, and biried in the same place.
2 Sai aka rasa ruwa da jama’a za su sha, mutane suka taru, suka tayar wa Musa da Haruna.
And whanne the puple hadde nede to watir, thei yeden togidere ayens Moises and Aaron; and thei weren turned in to dissensioun,
3 Suka yi gunaguni wa Musa suka ce, “Da ma mun mutu sa’ad da’yan’uwanmu suka mutu a gaban Ubangiji!
and seiden, We wolden that we hadden perischid among oure britheren bifor the Lord.
4 Don me ka kawo jama’ar Ubangiji a wannan hamada, don mu da dabbobinmu mu mutu a nan ke nan?
Whi han ye led out the chirche of the Lord in to wildirnesse, that bothe we and oure beestis die?
5 Don me ka fitar da mu daga Masar zuwa wannan banzan wuri, inda babu hatsi ko ɓaure, inabi ko rumman. Kuma babu ruwan da za a sha?”
Whi han ye maad vs to stie from Egipt, and han brouyt vs in to this werste place, which may not be sowun, which nether bryngith forth fige tre, nether vineris, nether pumgranatis, ferthermore and hath not watir to drynke?
6 Sai Musa da Haruna suka tashi daga taron, suka tafi ƙofar Tentin Sujada, suka fāɗi rubda ciki, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana musu.
And whanne the multitude was left, Moises and Aaron entriden in to the tabernacle of boond of pees, and felden lowe to erthe, and crieden to God, and seiden, Lord God, here the cry of this puple, and opene to hem thi tresour, a welle of quyk watir, that whanne thei ben fillid, the grutchyng of hem ceesse. And the glorie of the Lord apperide on hem;
7 Ubangiji ya ce wa Musa,
and the Lord spak to Moises,
8 “Ka ɗauki sandanka, kai da Haruna, ɗan’uwanka, ku tara jama’a, ku yi magana da dutsen a gabansu ya ba da ruwan da yake cikinsa. Za ka sa ruwa ya ɓuɓɓugo musu daga dutsen. Ta haka za ka ba taron jama’a da garkunansu ruwan sha.”
and seide, Take the yerde, and gadere the puple, thou, and Aaron thi brother; and speke ye to the stoon bifore hem, and it schal yyue watris. And whanne thou hast led watir out of the stoon, al the multitude schal drynke, and the beestis therof `schulden drynke.
9 Sai Musa ya je ya ɗauki sandan kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.
Therfor Moises took the yerde that was in the `siyt of the Lord, as the Lord comaundide to hym,
10 Shi da Haruna, suka tara jama’a a gaban dutsen, Musa ya ce musu, “Ku saurara, ku’yan tawaye, dole mu kawo muku ruwa daga wannan dutse?”
whanne the multitude was gaderid bifor the stoon; and he seide to hem, Here ye, rebel and vnbileueful; whether we moun brynge out of this stoon watir to you?
11 Sai Musa ya ɗaga hannu, ya bugi dutsen sau biyu da sandansa. Ruwa kuwa ya yi ta kwararowa, jama’a da dabbobinsu suka sha.
And whanne Moises hadde reisid the hond, and hadde smyte the flynt twies with the yerde, largeste watris yeden out, so that the puple drank, and the beestis drunken.
12 Amma Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna. “Tun da yake ba ku gaskata ni ba, ba ku kuwa ɗaukaka ni a idon Isra’ilawa ba, to, ba za ku kai taron jama’an nan a ƙasar da na ba su ba.”
And the Lord seide to Moises and to Aaron, For ye bileueden not to me, that ye schulden halewe me bifor the sones of Israel, ye schulen not lede these puples in to the lond which Y schal yyue to hem.
13 Waɗannan su ne ruwan Meriba, inda Isra’ilawa suka yi wa Ubangiji gunaguni, inda kuma ya nuna kansa mai tsarki a cikinsu.
This is the watir of ayenseiyng; there the sones of Israel stryueden ayens the Lord, and he was halewid in hem.
14 Musa ya aiki manzanni daga Kadesh zuwa wurin sarkin Edom cewa, “Ga abin da ɗan’uwanka Isra’ila ya ce ka san duk irin wahalolin da ya same mu.
In the meene tyme Moises sente messangeres fro Cades to the kyng of Edom, whiche seiden, Israel thi brother sendith these thinges. Thou knowist al the trauel that took vs,
15 Kakanninmu sun gangaro zuwa Masar, muka zauna can shekaru da yawa. Masarawa suka wulaƙanta mu, da kuma kakanninmu,
hou oure fadris yeden doun in to Egipt, and we dwelliden there myche tyme, and Egipcians turmentiden vs and oure fadris; and hou we crieden to the Lord,
16 amma da muka yi kuka a gaban Ubangiji, ya kuwa ji mu, sai ya aiko mala’ika, ya fitar da mu daga Masar. “Yanzu ga mu a Kadesh, garin da yake kan iyakar yankinka.
and he herde vs, and sente an aungel that ledde vs out of Egipt. And lo! we ben set in the citee of Cades, which is in thi laste coostis,
17 Muna roƙonka, ka yarda mana mu bi ta ƙasarka. Ba za mu bi ta wani fili, ko gonar inabi ba, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babban hanyar sarki, ba kuwa za mu kauce dama, ko hagu ba, har mu wuce yankinka.”
and we bisechen that it be leueful to vs to passe thorou thi lond; we schulen not go bi feeldis, nether bi vyneris, nether we schulen drynke watris of thi pittis; but we schulen go in the comyn weie, and we schulen not bowe to the riyt side, nether to the left side, til we passen thi termes.
18 Amma Edom ya amsa ya ce, “Ba za ku bi ta nan ba; in kuka kuskura, za mu fito, mu yaƙe ku da takobi.”
To whom Edom answeride, Ye schulen not passe bi me, ellis Y schal be armed, and come ayens thee.
19 Sai Isra’ilawa suka amsa, suka ce, “Za mu bi ta babbar hanya, in mu, ko dabbobinmu suka sha ruwanku, za mu biya. Mu dai muna so mu wuce ne kawai.”
And the sones of Israel seiden, We schulen go bi the weie comynli vsid, and if we and oure beestis drynken thi watris, we schulen yyue that that is iust; noon hardnesse schal be in prijs, onely passe we swiftli.
20 Sai mutanen Edom suka sāke amsa suka ce, “Ba za ku bi nan ba dai.” Sai Edom ya fito da runduna mai ƙarfi da yawa gaske a kan Isra’ila.
And he answeride, Ye schulen not passe. And anoon he yede out ayens Israel, with a multitude without noumbre, and `strong hond,
21 Da yake Edom suka ƙi su bar su su ratsa yankinsu, sai Isra’ila suka juya suka janye daga gare su.
nether he wolde assente to Israel bisechynge, that he schulde graunte passage bi hise coostis. Wherfor Israel turnede awey fro hym.
22 Dukan Jama’ar Isra’ilawa suka tashi daga Kadesh, suka zo Dutsen Hor.
And whanne thei hadden moued tentis fro Cades, thei camen in to the hil of Hor, which is in the endis of the lond of Edom;
23 A Dutsen Hor, kusa da iyakar Edom, Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
where the Lord spak to Moyses and seide, Aaron go to his puples;
24 “Haruna zai rasu. Ba zai shiga ƙasar da na ba Isra’ilawa ba, domin ku biyu, kun ƙi ku bi umarnina a ruwan Meriba.
for he schal not entre in to the lond which Y yaf to the sones of Israel, for he was vnbileueful to my mouth, at the watris of ayenseiyng.
25 Ka kawo Haruna da ɗansa Eleyazar, ka kai su a bisan Dutsen Hor.
Take thou Aaron, and his sone with hym, and thou schalt lede hem in to the hil of Hor;
26 Ka tuɓe taguwar Haruna ka sa wa ɗansa Eleyazar, gama Haruna zai rasu a can.”
and whanne thou hast maad nakid the fadir of his cloth, thou schalt clothe `with it Eleazar, his sone, and Aaron schal be gederid, and schal die there.
27 Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarta. Suka hau Dutsen Hor a idon dukan jama’a.
Moises dide as the Lord comaundide; and thei stieden in to the hil of Hor, bifor al the multitude.
28 Musa ya tuɓe taguwar Haruna, ya kuma sa wa Eleyazar ɗan Haruna. Nan kuwa Haruna ya mutu a bisa dutsen. Sa’an nan Musa da Eleyazar suka sauka daga dutsen,
And whanne he hadde maad nakid Aaron of hise clothis, he clothide with tho Eleazar, his sone. Sotheli whanne Aaron was deed in the `cop of the hil, Moises cam doun with Eleazar.
29 sa’ad da dukan jama’a kuwa suka ji cewa Haruna ya mutu, sai dukan gidan Isra’ila suka yi makoki dominsa har kwana talatin.
Sotheli al the multitude siy that Aaron was deed, and wepte on hym thretti daies, bi alle her meyness.