< Ƙidaya 20 >

1 A watan fari, dukan jama’ar Isra’ilawa suka iso Hamadan Zin. Suka sauka a Kadesh. A nan ne Miriyam ta mutu, aka kuma bizne ta.
In March/April [of the next year], the Israeli people traveled/walked to the Zin Desert and (camped/set up their tents) near Kadesh [town]. While they/we were there, [Moses’/my older sister] Miriam died and was buried there.
2 Sai aka rasa ruwa da jama’a za su sha, mutane suka taru, suka tayar wa Musa da Haruna.
There was no water for the people to drink there, so they came to Aaron and Moses/me.
3 Suka yi gunaguni wa Musa suka ce, “Da ma mun mutu sa’ad da’yan’uwanmu suka mutu a gaban Ubangiji!
They complained and said, “We wish that we had died in front of Yahweh’s Sacred Tent when our fellow Israelis died!
4 Don me ka kawo jama’ar Ubangiji a wannan hamada, don mu da dabbobinmu mu mutu a nan ke nan?
(Did you bring us, who are Yahweh’s people, into this desert to die along with our livestock?/You brought us, who are Yahweh’s people, into this desert to die along with our livestock!) [RHQ]
5 Don me ka fitar da mu daga Masar zuwa wannan banzan wuri, inda babu hatsi ko ɓaure, inabi ko rumman. Kuma babu ruwan da za a sha?”
Why did you bring us from Egypt to this miserable place [RHQ]? There is no grain, there are no figs, no grapes, and no pomegranates here. And there is no water for us to drink!”
6 Sai Musa da Haruna suka tashi daga taron, suka tafi ƙofar Tentin Sujada, suka fāɗi rubda ciki, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana musu.
Aaron and Moses/I turned away from the people and went to the entrance of the Sacred Tent and prostrated themselves/ourselves on the ground. Then Yahweh appeared to them/us with his bright glory,
7 Ubangiji ya ce wa Musa,
and he said to Moses/me,
8 “Ka ɗauki sandanka, kai da Haruna, ɗan’uwanka, ku tara jama’a, ku yi magana da dutsen a gabansu ya ba da ruwan da yake cikinsa. Za ka sa ruwa ya ɓuɓɓugo musu daga dutsen. Ta haka za ka ba taron jama’a da garkunansu ruwan sha.”
“You and Aaron must take Aaron’s walking stick with you and gather all the people together. While the people are watching, command that water will flow out of that [large] rock over there. Water for the people will flow from it; all they and all their livestock will have enough water to drink.”
9 Sai Musa ya je ya ɗauki sandan kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.
So Moses/I did what Yahweh told him/me to do. He/I took Aaron’s walking stick from the place in the Sacred Tent where it was kept.
10 Shi da Haruna, suka tara jama’a a gaban dutsen, Musa ya ce musu, “Ku saurara, ku’yan tawaye, dole mu kawo muku ruwa daga wannan dutse?”
Then Aaron and he/I summoned all the people to gather at the rock. Then Moses/I shouted to them, “All you rebellious people, listen! Is it necessary for us to give you water from this rock?”
11 Sai Musa ya ɗaga hannu, ya bugi dutsen sau biyu da sandansa. Ruwa kuwa ya yi ta kwararowa, jama’a da dabbobinsu suka sha.
Then Moses/I raised his/my hand and [instead of speaking to the rock], he/I struck the rock two times with the walking stick. And water gushed/poured out. So all the people and their livestock drank all the water that they wanted.
12 Amma Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna. “Tun da yake ba ku gaskata ni ba, ba ku kuwa ɗaukaka ni a idon Isra’ilawa ba, to, ba za ku kai taron jama’an nan a ƙasar da na ba su ba.”
But Yahweh said to Aaron and Moses/me, “You did not believe that I could demonstrate my power to the Israeli people [and give them water without your striking the rock]. So you will not lead them into the land that I am giving to them!”
13 Waɗannan su ne ruwan Meriba, inda Isra’ilawa suka yi wa Ubangiji gunaguni, inda kuma ya nuna kansa mai tsarki a cikinsu.
Later this place was called Meribah, [which means ‘arguing’], because there the Israeli people argued with Yahweh, and there he showed his power to them [by giving them water].
14 Musa ya aiki manzanni daga Kadesh zuwa wurin sarkin Edom cewa, “Ga abin da ɗan’uwanka Isra’ila ya ce ka san duk irin wahalolin da ya same mu.
[While the people were] at Kadesh [town], Moses/I sent messengers to the king of Edom to tell him this: “Your relatives, the Israeli people, are sending you this message. You know the many troubles/hardships that have happened to us.
15 Kakanninmu sun gangaro zuwa Masar, muka zauna can shekaru da yawa. Masarawa suka wulaƙanta mu, da kuma kakanninmu,
You know that our ancestors went down to Egypt. You know that they stayed there for many years. They suffered because the [rulers of] Egypt caused them to become their slaves [and to work very hard].
16 amma da muka yi kuka a gaban Ubangiji, ya kuwa ji mu, sai ya aiko mala’ika, ya fitar da mu daga Masar. “Yanzu ga mu a Kadesh, garin da yake kan iyakar yankinka.
“But when they called out to Yahweh, he heard them and sent an angel who brought them out of Egypt. Now we have set up our tents here at Kadesh, a town at the border of your land.
17 Muna roƙonka, ka yarda mana mu bi ta ƙasarka. Ba za mu bi ta wani fili, ko gonar inabi ba, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babban hanyar sarki, ba kuwa za mu kauce dama, ko hagu ba, har mu wuce yankinka.”
Please allow us to travel through your country. We will [be careful to] not walk through your fields and your vineyards. We will not even drink water from your wells. As we travel, we will stay on the king’s highway, [the main road that goes from the south to the north], and we will not leave that road until we have crossed the border [of your country in the north].”
18 Amma Edom ya amsa ya ce, “Ba za ku bi ta nan ba; in kuka kuskura, za mu fito, mu yaƙe ku da takobi.”
But the king of Edom refused. He replied, “Stay out of my country! If you try [to enter it], I will [send my army to] attack you!”
19 Sai Isra’ilawa suka amsa, suka ce, “Za mu bi ta babbar hanya, in mu, ko dabbobinmu suka sha ruwanku, za mu biya. Mu dai muna so mu wuce ne kawai.”
The Israeli messengers replied, “[If we travel through your country], we will stay on the main road. If we and any of our livestock drink any of your water, we will pay for it. We want only to travel through your country. We do not want anything else.”
20 Sai mutanen Edom suka sāke amsa suka ce, “Ba za ku bi nan ba dai.” Sai Edom ya fito da runduna mai ƙarfi da yawa gaske a kan Isra’ila.
But the king replied, “No! Stay out of our country! We will not [allow you] to travel through our land!” Then he sent the strongest soldiers in his army to prevent the Israelis [from entering his country].
21 Da yake Edom suka ƙi su bar su su ratsa yankinsu, sai Isra’ila suka juya suka janye daga gare su.
So, because [the king of] Edom refused to allow the Israelis to travel through his country, the Israelis turned [and traveled a different way].
22 Dukan Jama’ar Isra’ilawa suka tashi daga Kadesh, suka zo Dutsen Hor.
The Israeli people left Kadesh. They went to Hor Mountain,
23 A Dutsen Hor, kusa da iyakar Edom, Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
[which is at the border of Edom]. While they were there, Yahweh said to Aaron and Moses/me,
24 “Haruna zai rasu. Ba zai shiga ƙasar da na ba Isra’ilawa ba, domin ku biyu, kun ƙi ku bi umarnina a ruwan Meriba.
“It is time for Aaron to die [EUP]. He will not enter the land that I am giving to you Israelis, because the two of you disobeyed me [when I told you to speak to the rock to cause] the water [to flow] at Meribah.
25 Ka kawo Haruna da ɗansa Eleyazar, ka kai su a bisan Dutsen Hor.
Now you, Moses, take Aaron and his son Eleazar up on Hor Mountain.
26 Ka tuɓe taguwar Haruna ka sa wa ɗansa Eleyazar, gama Haruna zai rasu a can.”
There you must remove Aaron’s robes [that he wears when he does the work of a priest], and put them on his son, Eleazar. Aaron will die up there.”
27 Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarta. Suka hau Dutsen Hor a idon dukan jama’a.
So Moses/I did what Yahweh commanded. The three of them/us climbed up Hor Mountain, while all the Israeli people watched.
28 Musa ya tuɓe taguwar Haruna, ya kuma sa wa Eleyazar ɗan Haruna. Nan kuwa Haruna ya mutu a bisa dutsen. Sa’an nan Musa da Eleyazar suka sauka daga dutsen,
At the top of the mountain, Moses/I took off the robes that Aaron wore [while he did the work of a priest] and put them on Eleazar. Then Aaron died there on the top of the mountain, and Eleazar and Moses/I went back down.
29 sa’ad da dukan jama’a kuwa suka ji cewa Haruna ya mutu, sai dukan gidan Isra’ila suka yi makoki dominsa har kwana talatin.
When the Israeli people realized that Aaron had died, they all mourned for him for 30 days.

< Ƙidaya 20 >