< Ƙidaya 20 >
1 A watan fari, dukan jama’ar Isra’ilawa suka iso Hamadan Zin. Suka sauka a Kadesh. A nan ne Miriyam ta mutu, aka kuma bizne ta.
And the sons of Israel, all the congregation, come [into] the wilderness of Zin in the first month, and the people abide in Kadesh; and Miriam dies there and is buried there.
2 Sai aka rasa ruwa da jama’a za su sha, mutane suka taru, suka tayar wa Musa da Haruna.
And there has been no water for the congregation, and they are assembled against Moses and against Aaron,
3 Suka yi gunaguni wa Musa suka ce, “Da ma mun mutu sa’ad da’yan’uwanmu suka mutu a gaban Ubangiji!
and the people strive with Moses and speak, saying, “And oh that we had expired when our brothers expired before YHWH!
4 Don me ka kawo jama’ar Ubangiji a wannan hamada, don mu da dabbobinmu mu mutu a nan ke nan?
And why have you brought in the assembly of YHWH to this wilderness to die there, we and our beasts?
5 Don me ka fitar da mu daga Masar zuwa wannan banzan wuri, inda babu hatsi ko ɓaure, inabi ko rumman. Kuma babu ruwan da za a sha?”
And why have you brought us up out of Egypt to bring us to this evil place? [It is] not a place of seed, and fig, and vine, and pomegranate; and there is no water to drink.”
6 Sai Musa da Haruna suka tashi daga taron, suka tafi ƙofar Tentin Sujada, suka fāɗi rubda ciki, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana musu.
And Moses and Aaron go in from the presence of the assembly to the opening of the Tent of Meeting and fall on their faces, and the glory of YHWH is seen by them.
7 Ubangiji ya ce wa Musa,
And YHWH speaks to Moses, saying,
8 “Ka ɗauki sandanka, kai da Haruna, ɗan’uwanka, ku tara jama’a, ku yi magana da dutsen a gabansu ya ba da ruwan da yake cikinsa. Za ka sa ruwa ya ɓuɓɓugo musu daga dutsen. Ta haka za ka ba taron jama’a da garkunansu ruwan sha.”
“Take the rod and assemble the congregation—you and your brother Aaron—and you have spoken to the rock before their eyes, and it has given its water, and you have brought out water to them from the rock, and have watered the congregation and their beasts.”
9 Sai Musa ya je ya ɗauki sandan kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.
And Moses takes the rod from before YHWH as He has commanded him,
10 Shi da Haruna, suka tara jama’a a gaban dutsen, Musa ya ce musu, “Ku saurara, ku’yan tawaye, dole mu kawo muku ruwa daga wannan dutse?”
and Moses and Aaron assemble the assembly to the front of the rock, and he says to them, “Now hear, O rebels, do we bring out water to you from this rock?”
11 Sai Musa ya ɗaga hannu, ya bugi dutsen sau biyu da sandansa. Ruwa kuwa ya yi ta kwararowa, jama’a da dabbobinsu suka sha.
And Moses lifts up his hand and strikes the rock with his rod twice; and much water comes out, and the congregation drinks, and their beasts [drink].
12 Amma Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna. “Tun da yake ba ku gaskata ni ba, ba ku kuwa ɗaukaka ni a idon Isra’ilawa ba, to, ba za ku kai taron jama’an nan a ƙasar da na ba su ba.”
And YHWH says to Moses and to Aaron, “Because you have not believed in Me to sanctify Me before the eyes of the sons of Israel, therefore you do not bring in this assembly to the land which I have given to them.”
13 Waɗannan su ne ruwan Meriba, inda Isra’ilawa suka yi wa Ubangiji gunaguni, inda kuma ya nuna kansa mai tsarki a cikinsu.
These [are] the waters of Meribah, because the sons of Israel have “striven” with YHWH, and He is sanctified among them.
14 Musa ya aiki manzanni daga Kadesh zuwa wurin sarkin Edom cewa, “Ga abin da ɗan’uwanka Isra’ila ya ce ka san duk irin wahalolin da ya same mu.
And Moses sends messengers from Kadesh to the king of Edom, “Thus said your brother Israel: You have known all the travail which has found us,
15 Kakanninmu sun gangaro zuwa Masar, muka zauna can shekaru da yawa. Masarawa suka wulaƙanta mu, da kuma kakanninmu,
that our fathers go down to Egypt, and we dwell in Egypt [for] many days, and the Egyptians do evil to us and to our fathers;
16 amma da muka yi kuka a gaban Ubangiji, ya kuwa ji mu, sai ya aiko mala’ika, ya fitar da mu daga Masar. “Yanzu ga mu a Kadesh, garin da yake kan iyakar yankinka.
then we cry to YHWH, and He hears our voice, and sends a Messenger, and is bringing us out of Egypt; and behold, we [are] in Kadesh, a city [in] the extremity of your border.
17 Muna roƙonka, ka yarda mana mu bi ta ƙasarka. Ba za mu bi ta wani fili, ko gonar inabi ba, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babban hanyar sarki, ba kuwa za mu kauce dama, ko hagu ba, har mu wuce yankinka.”
Please let us pass over through your land; we do not pass over through a field or through a vineyard, nor do we drink waters of a well; we go the way of the king, we do not turn aside [to] the right or left until we pass over your border.”
18 Amma Edom ya amsa ya ce, “Ba za ku bi ta nan ba; in kuka kuskura, za mu fito, mu yaƙe ku da takobi.”
And Edom says to him, “You do not pass over through me, lest I come out to meet you with the sword.”
19 Sai Isra’ilawa suka amsa, suka ce, “Za mu bi ta babbar hanya, in mu, ko dabbobinmu suka sha ruwanku, za mu biya. Mu dai muna so mu wuce ne kawai.”
And the sons of Israel say to him, “We go in the highway, and if we drink of your waters—I and my livestock—then I have given their price; only, let me pass over on my feet, nothing [more].”
20 Sai mutanen Edom suka sāke amsa suka ce, “Ba za ku bi nan ba dai.” Sai Edom ya fito da runduna mai ƙarfi da yawa gaske a kan Isra’ila.
And he says, “You do not pass over”; and Edom comes out to meet him with many people and with a strong hand;
21 Da yake Edom suka ƙi su bar su su ratsa yankinsu, sai Isra’ila suka juya suka janye daga gare su.
and Edom refuses to permit Israel to pass over through his border, and Israel turns aside from off him.
22 Dukan Jama’ar Isra’ilawa suka tashi daga Kadesh, suka zo Dutsen Hor.
And the sons of Israel, all the congregation, journey from Kadesh and come to Mount Hor,
23 A Dutsen Hor, kusa da iyakar Edom, Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
and YHWH speaks to Moses and to Aaron in Mount Hor, on the border of the land of Edom, saying,
24 “Haruna zai rasu. Ba zai shiga ƙasar da na ba Isra’ilawa ba, domin ku biyu, kun ƙi ku bi umarnina a ruwan Meriba.
“Aaron is gathered to his people, for he does not go into the land which I have given to the sons of Israel, because that you provoked My mouth at the waters of Meribah.
25 Ka kawo Haruna da ɗansa Eleyazar, ka kai su a bisan Dutsen Hor.
Take Aaron and his son Eleazar, and cause them to go up Mount Hor,
26 Ka tuɓe taguwar Haruna ka sa wa ɗansa Eleyazar, gama Haruna zai rasu a can.”
and strip Aaron of his garments, and you have clothed his son Eleazar [with] them, and Aaron is gathered, and dies there.”
27 Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarta. Suka hau Dutsen Hor a idon dukan jama’a.
And Moses does as YHWH has commanded, and they go up to Mount Hor before the eyes of all the congregation,
28 Musa ya tuɓe taguwar Haruna, ya kuma sa wa Eleyazar ɗan Haruna. Nan kuwa Haruna ya mutu a bisa dutsen. Sa’an nan Musa da Eleyazar suka sauka daga dutsen,
and Moses strips Aaron of his garments, and clothes his son Eleazar with them, and Aaron dies there on the top of the mountain; and Moses comes down—Eleazar also—from the mountain,
29 sa’ad da dukan jama’a kuwa suka ji cewa Haruna ya mutu, sai dukan gidan Isra’ila suka yi makoki dominsa har kwana talatin.
and all the congregation sees that Aaron has expired, and all the house of Israel laments Aaron [for] thirty days.