< Ƙidaya 2 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
Le Seigneur parla encore à Moïse et à Aaron, disant:
2 “Duk sa’ad da Isra’ilawa suka yi sansani, kowane mutum zai sauka a inda tutar ƙungiyar kabilarsa take. Sansanin zai kasance a kewaye da Tentin Sujada.”
Les enfants d’Israël, chacun selon ses bandes, ses étendards, ses drapeaux et les maisons de sa parenté, camperont autour du tabernacle d’alliance.
3 Kabilar Yahuda za su yi sansani bisa ga ƙa’idarsu a gabas, wajen fitowar rana. Shugaban mutanen Yahuda kuwa shi ne Nashon ɗan Amminadab.
Juda plantera ses tentes vers l’orient selon les bandes de son armée, et le prince de ses enfants sera Nahasson, fils d’Aminadab;
4 Yawan mutanen sashensa 74,600 ne.
Et le nombre total des combattants de sa race, est de soixante-quatorze mille six cents.
5 Kabilar Issakar za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Netanel ɗan Zuwar.
Près de lui campèrent ceux de la tribu d’Issachar; leur prince fut Nathanael fils de Suar;
6 Yawan mutanen sashensa 54,400 ne.
Et le nombre total de ses combattants, de cinquante-quatre mille quatre cents.
7 Kabilar Zebulun za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Eliyab ɗan Helon.
Dans la tribu de Zabulon le prince fut Eliab, fils d’Hélon.
8 Yawan mutanen sashensa 57,400 ne.
Toute l’armée des combattants de sa race fut de cinquante-sept mille quatre cents,
9 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Yahuda bisa ga sashensu sun kai 186,400. Su ne za su ja gaba.
Tous ceux qui ont été dénombrés dans le camp de Juda, furent cent quatre-vingt-six mille quatre cents; et ils sortiront les premiers selon leurs bandes.
10 A kudu, a nan ne sashe sansanin mutanen Ruben a ƙarƙashin ƙa’idarsu, za su yi sansani. Shugaban mutanen Ruben shi ne Elizur ɗan Shedeyur.
Dans le camp des enfants de Ruben vers le côté méridional, le prince sera Eli sur, fils de Sédéur;
11 Yawan mutanen sashensa 46,500 ne.
Et toute l’armée de ses combattants qui ont été dénombrés, quarante-six mille cinq cents.
12 Kabilar Simeyon za su yi sansani biye da su. Shugaban mutanensa shi ne Shelumiyel ɗan Zurishaddai.
Près de lui campèrent ceux de la tribu de Siméon; leur prince fut Salamiel, fils de Surisaddaï,
13 Yawan mutanen sashensa 59,300 ne.
Et toute l’armée de ses combattants qui ont été dénombrés, cinquante-neuf mille trois cents.
14 Kabilar Gad za su zama na biye. Shugaban mutanensa shi ne Eliyasaf ɗan Reyuwel.
Dans la tribu de Gad, le prince fut Eliasaph, fils de Duel;
15 Yawan mutanen sashensa 45,650 ne.
Et toute l’armée de ses combattants qui ont été dénombrés, quarante-cinq mille six cent cinquante.
16 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Ruben, bisa ga sashensu sun kai 151,450. Su ne za su zama na biyu in za a tashi.
Tous ceux qui ont été recensés dans le camp de Ruben furent cent cinquante-un mille quatre cent cinquante, selon leurs bandes; ils marcheront au second rang.
17 Sa’an nan Lawiyawa ɗauke da Tentin Sujada za su kasance a tsakiyar sansani sa’ad da aka tashi tafiya. Za su kama hanya kamar yadda aka dokace su su zauna a sansani, kowa a wurinsa a ƙarƙashin ƙa’idarsu.
Alors le tabernacle de témoignage sera enlevé par les soins des Lévites et par leurs bandes: de la manière qu’il sera dressé, il sera aussi enlevé. Chacun marchera en sa place et en son rang.
18 Ta wajen yamma kuma sashen Efraim za su yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugaban mutanensa, shi ne Elishama ɗan Ammihud.
Vers le côté occidental sera le camp des enfants d’Ephraïm; leur prince fut Elisama, fils d’Ammiud;
19 Yawan mutanen sashensa 40,500 ne.
Et toute l’armée de ses combattants qui ont été dénombrés, quarante mille cinq cents.
20 Kabilar Manasse ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Gamaliyel ɗan Fedazur.
Et avec eux, la tribu des enfants de Manassé; leur prince fut Gamaliel, fils de Phadassur;
21 Yawan mutanen sashensa 32,200 ne.
Et toute l’armée de ses combattants qui ont été dénombrés, trente-deux mille deux cents.
22 Na biye da su su ne mutanen Benyamin. Shugaban mutanensu kuwa Abidan ɗan Gideyoni.
Dans la tribu des fils de Benjamin, le prince fut Abidan, fils de Gédéon;
23 Yawan mutanen sashensa 35,400 ne.
Et toute l’armée de ses combattants qui ont été recensés, trente-cinq mille quatre cents.
24 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 108,100 ne. Su ne za su zama na uku sa’ad da za a tashi.
Tous ceux qui ont été dénombrés dans le camp d’Ephraïm, furent cent huit mille cent, selon leurs bandes; ils marcheront les troisièmes.
25 A arewa za a sami sashen sansanin Dan, a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugabansu shi ne Ahiyezer ɗan Ammishaddai.
Vers la partie de l’aquilon ont campé les fils de Dan; leur prince fut Ahiézer, fils d’Ammisaddaï;
26 Yawan mutanen sashensa 62,700 ne.
Toute l’armée de ses combattants qui ont été dénombrés, soixante-deux mille sept cents.
27 Kabilar Asher ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Fagiyel ɗan Okran.
C’est près de Dan que plantèrent leurs tentes ceux de la tribu d’Aser; leur prince fut Phégiel, fils d’Ochran;
28 Yawan mutanen sashensa 41,500 ne.
Toute l’armée de ses combattants qui ont été comptés, quarante-un mille cinq cents,
29 Kabilar Naftali za su zama na biye da su. Shugaban mutanen kuwa shi ne Ahira ɗan Enan.
Quant à la tribu des enfants de Nephthali, le prince fut Ahira, fils d’Enan;
30 Yawan mutanen sashensa 53,400 ne
Toute l’armée de ses combattants, cinquante-trois mille quatre cents.
31 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 157,600. Su ne za su zama na ƙarshe, ƙarƙashin ƙa’idarsu.
Tous ceux qui ont été dénombrés dans le camp de Dan, furent cent cinquante-sept mille six cents; et ils marcheront les derniers.
32 Waɗannan su ne Isra’ilawan da aka a ƙidaya bisa ga iyalansu. Dukansu da suke a sansani, mutane 603,550 ne.
Ce nombre des enfants d’Israël, selon les maisons de leur parenté et les bandes de leur armée divisée, était de six cent trois mille cinq cent cinquante.
33 Ba a dai ƙidaya Lawiyawa tare da sauran Isra’ilawa ba yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Mais les Lévites n’ont pas été dénombrés parmi les enfants d’Israël; car ainsi l’avait ordonné le Seigneur à Moïse.
34 Saboda haka Isra’ilawa suka yi duk ko mene ne da Ubangiji ya umarci Musa. Ta haka ne suka yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu kowanne tare da kabilarsa da danginsa.
Et les enfants d’Israël firent selon tout ce qu’avait commandé le Seigneur. Ils campèrent selon leurs bandes, et marchèrent selon les familles et les maisons de leurs pères.

< Ƙidaya 2 >