< Ƙidaya 2 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
Et l’Éternel parla à Moïse et à Aaron, disant:
2 “Duk sa’ad da Isra’ilawa suka yi sansani, kowane mutum zai sauka a inda tutar ƙungiyar kabilarsa take. Sansanin zai kasance a kewaye da Tentin Sujada.”
Les fils d’Israël camperont chacun près de sa bannière, sous les enseignes de leurs maisons de pères; ils camperont autour de la tente d’assignation, à distance, vis-à-vis.
3 Kabilar Yahuda za su yi sansani bisa ga ƙa’idarsu a gabas, wajen fitowar rana. Shugaban mutanen Yahuda kuwa shi ne Nashon ɗan Amminadab.
[Voici] ceux qui camperont à l’orient, vers le levant, [sous] la bannière du camp de Juda, selon leurs armées: le prince des fils de Juda, Nakhshon, fils d’Amminadab,
4 Yawan mutanen sashensa 74,600 ne.
et son armée; et ses dénombrés, 74 600.
5 Kabilar Issakar za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Netanel ɗan Zuwar.
– Et ceux qui camperont près de lui, sont la tribu d’Issacar: le prince des fils d’Issacar, Nethaneël, fils de Tsuar,
6 Yawan mutanen sashensa 54,400 ne.
et son armée; et ses dénombrés, 54 400.
7 Kabilar Zebulun za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Eliyab ɗan Helon.
– [Avec eux] sera la tribu de Zabulon: le prince des fils de Zabulon, Éliab, fils de Hélon,
8 Yawan mutanen sashensa 57,400 ne.
et son armée; et ses dénombrés, 57 400.
9 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Yahuda bisa ga sashensu sun kai 186,400. Su ne za su ja gaba.
– Tous les dénombrés du camp de Juda, 186 400, selon leurs armées; ils partiront les premiers.
10 A kudu, a nan ne sashe sansanin mutanen Ruben a ƙarƙashin ƙa’idarsu, za su yi sansani. Shugaban mutanen Ruben shi ne Elizur ɗan Shedeyur.
La bannière du camp de Ruben, selon ses armées, sera vers le midi: le prince des fils de Ruben, Élitsur, fils de Shedéur,
11 Yawan mutanen sashensa 46,500 ne.
et son armée; et ses dénombrés, 46 500.
12 Kabilar Simeyon za su yi sansani biye da su. Shugaban mutanensa shi ne Shelumiyel ɗan Zurishaddai.
– Et ceux qui camperont près de lui, sont la tribu de Siméon: le prince des fils de Siméon, Shelumiel, fils de Tsurishaddaï,
13 Yawan mutanen sashensa 59,300 ne.
et son armée; et ses dénombrés, 59 300.
14 Kabilar Gad za su zama na biye. Shugaban mutanensa shi ne Eliyasaf ɗan Reyuwel.
– Et [avec eux] sera la tribu de Gad: le prince des fils de Gad, Éliasaph, fils de Rehuel,
15 Yawan mutanen sashensa 45,650 ne.
et son armée; et ses dénombrés, 45 650.
16 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Ruben, bisa ga sashensu sun kai 151,450. Su ne za su zama na biyu in za a tashi.
– Tous les dénombrés du camp de Ruben, 151 450, selon leurs armées; et ils partiront les seconds.
17 Sa’an nan Lawiyawa ɗauke da Tentin Sujada za su kasance a tsakiyar sansani sa’ad da aka tashi tafiya. Za su kama hanya kamar yadda aka dokace su su zauna a sansani, kowa a wurinsa a ƙarƙashin ƙa’idarsu.
Et la tente d’assignation partira, le camp des Lévites étant au milieu des camps; comme ils auront campé, ainsi ils partiront, chacun à sa place, selon leurs bannières.
18 Ta wajen yamma kuma sashen Efraim za su yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugaban mutanensa, shi ne Elishama ɗan Ammihud.
La bannière du camp d’Éphraïm, selon ses armées, sera vers l’occident: le prince des fils d’Éphraïm, Élishama, fils d’Ammihud,
19 Yawan mutanen sashensa 40,500 ne.
et son armée; et ses dénombrés, 40 500.
20 Kabilar Manasse ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Gamaliyel ɗan Fedazur.
– Et près de lui la tribu de Manassé: le prince des fils de Manassé, Gameliel, fils de Pedahtsur,
21 Yawan mutanen sashensa 32,200 ne.
et son armée; et ses dénombrés, 32 200.
22 Na biye da su su ne mutanen Benyamin. Shugaban mutanensu kuwa Abidan ɗan Gideyoni.
– Et [avec eux] sera la tribu de Benjamin: le prince des fils de Benjamin, Abidan, fils de Guidhoni,
23 Yawan mutanen sashensa 35,400 ne.
et son armée; et ses dénombrés, 35 400.
24 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 108,100 ne. Su ne za su zama na uku sa’ad da za a tashi.
– Tous les dénombrés du camp d’Éphraïm, 108 100, selon leurs armées; et ils partiront les troisièmes.
25 A arewa za a sami sashen sansanin Dan, a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugabansu shi ne Ahiyezer ɗan Ammishaddai.
La bannière du camp de Dan, selon ses armées, sera vers le nord: le prince des fils de Dan, Akhiézer, fils d’Ammishaddaï,
26 Yawan mutanen sashensa 62,700 ne.
et son armée; et ses dénombrés, 62 700.
27 Kabilar Asher ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Fagiyel ɗan Okran.
– Et ceux qui camperont près de lui, sont la tribu d’Aser: le prince des fils d’Aser, Paghiel, fils d’Ocran,
28 Yawan mutanen sashensa 41,500 ne.
et son armée; et ses dénombrés, 41 500.
29 Kabilar Naftali za su zama na biye da su. Shugaban mutanen kuwa shi ne Ahira ɗan Enan.
– Et [avec eux] sera la tribu de Nephthali: le prince des fils de Nephthali, Akhira, fils d’Énan,
30 Yawan mutanen sashensa 53,400 ne
et son armée; et ses dénombrés, 53 400.
31 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 157,600. Su ne za su zama na ƙarshe, ƙarƙashin ƙa’idarsu.
– Tous les dénombrés du camp de Dan, 157 600; ils partiront les derniers, selon leurs bannières.
32 Waɗannan su ne Isra’ilawan da aka a ƙidaya bisa ga iyalansu. Dukansu da suke a sansani, mutane 603,550 ne.
Ce sont là les dénombrés des fils d’Israël, selon leurs maisons de pères. Tous les dénombrés des camps, selon leurs armées, furent 603 550.
33 Ba a dai ƙidaya Lawiyawa tare da sauran Isra’ilawa ba yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Mais les Lévites ne furent pas dénombrés parmi les fils d’Israël, ainsi que l’Éternel l’avait commandé à Moïse.
34 Saboda haka Isra’ilawa suka yi duk ko mene ne da Ubangiji ya umarci Musa. Ta haka ne suka yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu kowanne tare da kabilarsa da danginsa.
Et les fils d’Israël firent selon tout ce que l’Éternel avait commandé à Moïse: ainsi ils campèrent selon leurs bannières, et ainsi ils partirent, chacun selon leurs familles, selon leurs maisons de pères.

< Ƙidaya 2 >