< Ƙidaya 2 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And the Lord spake vnto Moses, and to Aaron, saying,
2 “Duk sa’ad da Isra’ilawa suka yi sansani, kowane mutum zai sauka a inda tutar ƙungiyar kabilarsa take. Sansanin zai kasance a kewaye da Tentin Sujada.”
Euery man of the children of Israel shall campe by his standerd, and vnder the ensigne of their fathers house: farre off about the Tabernacle of the Congregation shall they pitch.
3 Kabilar Yahuda za su yi sansani bisa ga ƙa’idarsu a gabas, wajen fitowar rana. Shugaban mutanen Yahuda kuwa shi ne Nashon ɗan Amminadab.
On the East side towarde the rising of the sunne, shall they of the standerd of the hoste of Iudah pitch according to their armies: and Nahshon the sonne of Amminadab shalbe captaine of the sonnes of Iudah.
4 Yawan mutanen sashensa 74,600 ne.
And his hoste and the nomber of the were seuentie and foure thousande and sixe hundreth.
5 Kabilar Issakar za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Netanel ɗan Zuwar.
Next vnto him shall they of the tribe of Issachar pitch, and Nethaneel the sonne of Zuar shalbe the captaine of the sonnes of Issachar:
6 Yawan mutanen sashensa 54,400 ne.
And his hoste, and the nomber thereof were foure and fiftie thousand, and foure hundreth.
7 Kabilar Zebulun za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Eliyab ɗan Helon.
Then the tribe of Zebulun, and Eliab the sonne of Helon, captaine ouer the sonnes of Zebulun:
8 Yawan mutanen sashensa 57,400 ne.
And his hoste, and the nomber thereof seuen and fiftie thousand and foure hundreth:
9 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Yahuda bisa ga sashensu sun kai 186,400. Su ne za su ja gaba.
The whole nomber of the hoste of Iudah are an hundreth fourescore and sixe thousande, and foure hundreth according to their armies: they shall first set foorth.
10 A kudu, a nan ne sashe sansanin mutanen Ruben a ƙarƙashin ƙa’idarsu, za su yi sansani. Shugaban mutanen Ruben shi ne Elizur ɗan Shedeyur.
On the South side shalbe ye standerd of the host of Reuben according to their armies, and the captaine ouer the sonnes of Reuben shalbe Elizur the sonne of Shedeur.
11 Yawan mutanen sashensa 46,500 ne.
And his host, and the nomber thereof sixe and fourty thousand and fiue hundreth.
12 Kabilar Simeyon za su yi sansani biye da su. Shugaban mutanensa shi ne Shelumiyel ɗan Zurishaddai.
And by him shall the tribe of Simeon pitch, and the captaiue ouer the sonnes of Simeon shall be Shelumiel the sonne of Zurishaddai:
13 Yawan mutanen sashensa 59,300 ne.
And his hoste, and the nomber of them, nine and fiftie thousand and three hundreth.
14 Kabilar Gad za su zama na biye. Shugaban mutanensa shi ne Eliyasaf ɗan Reyuwel.
And the tribe of Gad, and the captaine ouer the sonnes of Gad shall be Eliasaph the sonne of Deuel:
15 Yawan mutanen sashensa 45,650 ne.
And his host and the nomber of the were fiue and fourtye thousande, sixe hundreth and fiftie.
16 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Ruben, bisa ga sashensu sun kai 151,450. Su ne za su zama na biyu in za a tashi.
All the nomber of the campe of Reuben were an hundreth and one and fiftie thousande, and foure hundreth and fiftie according to their armies, and they shall set foorth in the seconde place.
17 Sa’an nan Lawiyawa ɗauke da Tentin Sujada za su kasance a tsakiyar sansani sa’ad da aka tashi tafiya. Za su kama hanya kamar yadda aka dokace su su zauna a sansani, kowa a wurinsa a ƙarƙashin ƙa’idarsu.
Then the Tabernacle of the Congregation shall goe with the host of the Leuites, in the mids of the campe as they haue pitched, so shall they goe forwarde, euery man in his order according to their standerds.
18 Ta wajen yamma kuma sashen Efraim za su yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugaban mutanensa, shi ne Elishama ɗan Ammihud.
The standerd of the campe of Ephraim shalbe toward the west according to their armies: and ye captaine ouer the sonnes of Ephraim shall be Elishama the sonne of Ammihud:
19 Yawan mutanen sashensa 40,500 ne.
And his host and the nomber of the were fortie thousand and fiue hundreth.
20 Kabilar Manasse ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Gamaliyel ɗan Fedazur.
And by him shalbe the tribe of Manasseh, and the captaine ouer the sonnes of Manasseh shalbe Gamliel the sonne of Pedahzur:
21 Yawan mutanen sashensa 32,200 ne.
And his hoste and the nomber of them were two and thirtie thousand and two hundreth.
22 Na biye da su su ne mutanen Benyamin. Shugaban mutanensu kuwa Abidan ɗan Gideyoni.
And the tribe of Beniamin, and ye captaine ouer the sonnes of Beniamin shalbe Abidan the sonne of Gideoni:
23 Yawan mutanen sashensa 35,400 ne.
And his host, and the nomber of the were fiue and thirtie thousand and foure hundreth.
24 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 108,100 ne. Su ne za su zama na uku sa’ad da za a tashi.
All the nomber of the campe of Ephraim were an hundreth and eight thousande and one hundreth according to their armies, and they shall go in the third place.
25 A arewa za a sami sashen sansanin Dan, a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugabansu shi ne Ahiyezer ɗan Ammishaddai.
The standerd of the host of Dan shalbe toward the North according to their armies: and the captaine ouer the children of Dan shall be Ahiezer the sonne of Ammishaddai:
26 Yawan mutanen sashensa 62,700 ne.
And his host and the number of them were two and threescore thousand and seue hundreth.
27 Kabilar Asher ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Fagiyel ɗan Okran.
And by him shall the tribe of Asher pitch, and the captaine ouer the sonnes of Asher shalbe Pagiel the sonne of Ocran.
28 Yawan mutanen sashensa 41,500 ne.
And his host and the nomber of them were one and fourtie thousand and fiue hundreth.
29 Kabilar Naftali za su zama na biye da su. Shugaban mutanen kuwa shi ne Ahira ɗan Enan.
Then the tribe of Naphtali, and the captaine ouer the children of Naphtali shall be Ahira the sonne of Enan:
30 Yawan mutanen sashensa 53,400 ne
And his host and the nomber of them were three and fiftie thousand and foure hundreth.
31 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 157,600. Su ne za su zama na ƙarshe, ƙarƙashin ƙa’idarsu.
All the nomber of the host of Dan was an hundreth and seuen and fiftie thousand and sixe hundreth: they shall goe hinmost with their standerdes.
32 Waɗannan su ne Isra’ilawan da aka a ƙidaya bisa ga iyalansu. Dukansu da suke a sansani, mutane 603,550 ne.
These are the summes of the childre of Israel by ye houses of their fathers, all the nomber of ye host, according to their armies, six hundreth and three thousand, fiue hundreth and fiftie.
33 Ba a dai ƙidaya Lawiyawa tare da sauran Isra’ilawa ba yadda Ubangiji ya umarci Musa.
But the Leuites were not nombred among the children of Israel, as the Lord had commanded Moses.
34 Saboda haka Isra’ilawa suka yi duk ko mene ne da Ubangiji ya umarci Musa. Ta haka ne suka yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu kowanne tare da kabilarsa da danginsa.
And the children of Israel did according to all that the Lord had commanded Moses: so they pitched according to their standards, and so they iourneyed euery one with his families, according to the houses of their fathers.

< Ƙidaya 2 >