< Ƙidaya 2 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And the Lord said to Moses and Aaron,
2 “Duk sa’ad da Isra’ilawa suka yi sansani, kowane mutum zai sauka a inda tutar ƙungiyar kabilarsa take. Sansanin zai kasance a kewaye da Tentin Sujada.”
The children of Israel are to put up their tents in the order of their families, by the flags of their fathers' houses, facing the Tent of meeting on every side.
3 Kabilar Yahuda za su yi sansani bisa ga ƙa’idarsu a gabas, wajen fitowar rana. Shugaban mutanen Yahuda kuwa shi ne Nashon ɗan Amminadab.
Those whose tents are on the east side, looking to the dawn, will be round the flag of the children of Judah, with Nahshon, the son of Amminadab, as their chief.
4 Yawan mutanen sashensa 74,600 ne.
The number of his army was seventy-four thousand, six hundred.
5 Kabilar Issakar za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Netanel ɗan Zuwar.
And nearest to him will be the tribe of Issachar, with Nethanel, the son of Zuar, as their chief.
6 Yawan mutanen sashensa 54,400 ne.
The number of his army was fifty-four thousand, four hundred.
7 Kabilar Zebulun za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Eliyab ɗan Helon.
After him, the tribe of Zebulun, with Eliab, the son of Helon, as their chief.
8 Yawan mutanen sashensa 57,400 ne.
The number of his army was fifty-seven thousand, four hundred.
9 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Yahuda bisa ga sashensu sun kai 186,400. Su ne za su ja gaba.
The number of all the armies of Judah was a hundred and eighty-six thousand, four hundred. They go forward first.
10 A kudu, a nan ne sashe sansanin mutanen Ruben a ƙarƙashin ƙa’idarsu, za su yi sansani. Shugaban mutanen Ruben shi ne Elizur ɗan Shedeyur.
On the south side is the flag of the children of Reuben, in the order of their armies, with Elizur, the son of Shedeur, as their chief.
11 Yawan mutanen sashensa 46,500 ne.
The number of his army was forty-six thousand, five hundred.
12 Kabilar Simeyon za su yi sansani biye da su. Shugaban mutanensa shi ne Shelumiyel ɗan Zurishaddai.
And nearest to him, the tribe of Simeon, with Shelumiel, the son of Zurishaddai, as their chief.
13 Yawan mutanen sashensa 59,300 ne.
The number of his army was fifty-nine thousand, three hundred.
14 Kabilar Gad za su zama na biye. Shugaban mutanensa shi ne Eliyasaf ɗan Reyuwel.
Then the tribe of Gad, with Eliasaph, son of Reuel, as their chief.
15 Yawan mutanen sashensa 45,650 ne.
The number of his army was forty-five thousand, six hundred and fifty.
16 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Ruben, bisa ga sashensu sun kai 151,450. Su ne za su zama na biyu in za a tashi.
The number of all the armies of Reuben together came to a hundred and fifty-one thousand, four hundred and fifty. They go forward second.
17 Sa’an nan Lawiyawa ɗauke da Tentin Sujada za su kasance a tsakiyar sansani sa’ad da aka tashi tafiya. Za su kama hanya kamar yadda aka dokace su su zauna a sansani, kowa a wurinsa a ƙarƙashin ƙa’idarsu.
Then the Tent of meeting is to go forward, with the tents of the Levites, in the middle of the armies; in the same order as their tents are placed, they are to go forward, every man under his flag.
18 Ta wajen yamma kuma sashen Efraim za su yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugaban mutanensa, shi ne Elishama ɗan Ammihud.
On the west side will be the flag of the children of Ephraim, with Elishama, the son of Ammihud, as their chief.
19 Yawan mutanen sashensa 40,500 ne.
The number of his army was forty thousand, five hundred.
20 Kabilar Manasse ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Gamaliyel ɗan Fedazur.
And by him the tribe of Manasseh with Gamaliel, the son of Pedahzur, as their chief.
21 Yawan mutanen sashensa 32,200 ne.
The number of his army was thirty-two thousand, two hundred.
22 Na biye da su su ne mutanen Benyamin. Shugaban mutanensu kuwa Abidan ɗan Gideyoni.
Then the tribe of Benjamin, with Abidan, the son of Gideoni, as their chief.
23 Yawan mutanen sashensa 35,400 ne.
The number of his army was thirty-five thousand, four hundred.
24 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 108,100 ne. Su ne za su zama na uku sa’ad da za a tashi.
The number of all the armies of Ephraim was a hundred and eight thousand, one hundred. They go forward third.
25 A arewa za a sami sashen sansanin Dan, a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugabansu shi ne Ahiyezer ɗan Ammishaddai.
On the north side will be the flag of the children of Dan, with Ahiezer, the son of Ammishaddai, as their chief.
26 Yawan mutanen sashensa 62,700 ne.
The number of his army was sixty-two thousand, seven hundred.
27 Kabilar Asher ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Fagiyel ɗan Okran.
Nearest to him will be the tribe of Asher, with Pagiel, the son of Ochran, as their chief.
28 Yawan mutanen sashensa 41,500 ne.
The number of his army was forty-one thousand, five hundred;
29 Kabilar Naftali za su zama na biye da su. Shugaban mutanen kuwa shi ne Ahira ɗan Enan.
Then the tribe of Naphtali, with Ahira, the son of Enan, as their chief.
30 Yawan mutanen sashensa 53,400 ne
The number of his army was fifty-three thousand, four hundred.
31 Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 157,600. Su ne za su zama na ƙarshe, ƙarƙashin ƙa’idarsu.
The number of all the armies in the tents of Dan was a hundred and fifty-seven thousand, six hundred. They will go forward last, by their flags.
32 Waɗannan su ne Isra’ilawan da aka a ƙidaya bisa ga iyalansu. Dukansu da suke a sansani, mutane 603,550 ne.
These are all who were numbered of the children of Israel, in the order of their fathers' families: all the armies in their tents together came to six hundred and three thousand, five hundred and fifty.
33 Ba a dai ƙidaya Lawiyawa tare da sauran Isra’ilawa ba yadda Ubangiji ya umarci Musa.
But the Levites were not numbered among the children of Israel, as the Lord said to Moses.
34 Saboda haka Isra’ilawa suka yi duk ko mene ne da Ubangiji ya umarci Musa. Ta haka ne suka yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu kowanne tare da kabilarsa da danginsa.
So the children of Israel did as the Lord said to Moses, so they put up their tents by their flags, and they went forward in the same order, by their families, and by their fathers' houses.

< Ƙidaya 2 >