< Ƙidaya 19 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
RAB Musa'yla Harun'a şöyle dedi:
2 “Wannan ita ce ƙa’ida wadda Ubangiji ya umarta. Faɗa wa Isra’ilawa su kawo maka jan karsana marar lahani, ko marar aibi wadda ba a taɓa sa ta tă yi noma ba.
“RAB'bin buyurduğu yasanın kuralı şudur: İsrailliler'e size kusursuz, özürsüz, boyunduruk takmamış kızıl bir inek getirmelerini söyleyin.
3 Ka ba wa Eleyazar firist; a kuma kai ta bayan sansani, a yanka a gaban Eleyazar.
İnek Kâhin Elazar'a verilsin; ordugahın dışına çıkarılıp onun önünde kesilecek.
4 Sa’an nan Eleyazar firist zai ɗiba jininta a yatsarsa, yă yayyafa sau bakwai wajen gaban Tentin Sujada.
Kâhin Elazar parmağıyla kanından alıp yedi kez Buluşma Çadırı'nın önüne doğru serpecek.
5 Sa’an nan a ƙone dukan karsanar, haɗe da fatarta, naman, jinin da kayan cikin, yayinda Eleyazar yake kallo.
Sonra Elazar'ın gözü önünde inek, derisi, eti, kanı ve gübresiyle birlikte yakılacak.
6 Firist zai ɗauki itacen al’ul, da hizzob, da jan ulu, yă jefa su a kan karsanar da ake ƙonewa.
Kâhin biraz sedir ağacı, mercanköşkotu ve kırmızı iplik alıp yanmakta olan ineğin üzerine atacak.
7 Bayan haka, dole firist yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka. Sa’an nan zai iya shiga cikin sansani, amma zai kasance da ƙazanta har yamma.
Sonra giysilerini yıkayacak, yıkanacak. Ancak o zaman ordugaha girebilir. Ama akşama dek kirli sayılacaktır.
8 Dole mutumin da ya ƙone ta yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka, shi ma zai kasance da ƙazanta har yamma.
İneği yakan kişi de giysilerini yıkayacak, yıkanacak. O da akşama dek kirli sayılacak.
9 “Mutumin da yake da tsarki, zai tara tokar karsanar, yă sa ta a wurin da yake da tsabta a bayan sansani. Jama’ar Isra’ilawa ne za su adana shi don amfani a ruwan tsabtaccewa; wannan domin tsarkakewa ne daga zunubi.
“Temiz sayılan bir kişi ineğin külünü toplayıp ordugahın dışında temiz sayılan bir yere koyacak. İsrail topluluğu temizlenme suyu için bu külü saklayacak; bu, günahtan arınmak içindir.
10 Dole mutumin da ya tara tokar karsanar yă wanke rigunarsa, zai kuwa kasance da ƙazanta har yamma. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta har abada ga Isra’ilawa, da kuma baƙin da suke zama a cikinsu.
İneğin külünü toplayan adam giysilerini yıkayacak, akşama dek kirli sayılacak. Bu kural hem İsrailliler, hem de aralarında yaşayan yabancılar için kalıcı olacaktır.
11 “Duk wanda ya taɓa gawa, zai kasance da ƙazanta har kwana bakwai.
“Herhangi bir insan ölüsüne dokunan kişi yedi gün kirli sayılacaktır.
12 Dole yă tsarkake kansa da ruwa a rana ta uku, da kuma a rana ta bakwai; sa’an nan zai zama da tsarki. Amma in bai tsarkake kansa a rana ta uku da kuma a rana ta bakwai ba, ba zai kasance da tsarki ba.
Üçüncü ve yedinci gün temizlenme suyuyla kendini arındıracak, böylece paklanmış olacak. Üçüncü ve yedinci gün kendini arındırmazsa, paklanmış sayılmayacak.
13 Duk wanda ya taɓa gawar wani, bai kuma tsarkake kansa ba, ya ƙazantar da tabanakul na Ubangiji ke nan. Dole a ware wannan mutum daga cikin Isra’ilawa. Gama ba a yayyafa ruwan tsabtaccewa a kansa ba; ya ƙazantu, ya kasance da ƙazanta ke nan.
Herhangi bir insan ölüsüne dokunup da kendini arındırmayan kişi RAB'bin Konutu'nu kirletmiş olur. O kişi İsrail'den atılmalı. Temizlenme suyu üzerine dökülmediği için kirli sayılır, kirliliği üzerinde kalır.
14 “Ga ƙa’idar da za a bi in mutum ya mutu a cikin tenti. Duk wanda ya shiga tentin, kuma duk wanda yake cikinsa, za su zama da ƙazanta har kwana bakwai,
“Çadırda biri öldüğü zaman uygulanacak kural şudur: Çadıra giren ve çadırda bulunan herkes yedi gün kirli sayılacaktır.
15 kuma kowane abin da ake zuba kaya, wanda ba shi da murfi a kansa, zai zama da ƙazanta.
Kapağı iple bağlanmamış, ağzı açık her kap kirli sayılacaktır.
16 “Wanda duk yake a fili, ya kuma taɓa gawa wanda aka kashe da takobi, ko wanda ya mutu mutuwar Allah, ko ƙashin mutum, ko kabari, zai ƙazantu har bakwai.
“Kırda kılıçla öldürülmüş ya da doğal ölümle ölmüş birine, insan kemiğine ya da mezara her dokunan yedi gün kirli sayılacaktır.
17 “Ga wanda ya ƙazantu kuwa, a ɗiba toka daga hadaya ta ƙonawa ta tsarkakewa, a zuba a cikin tulu, sa’an nan a zuba ruwa mai gudu a kansu.
“Kirli sayılan kişi için bir kabın içine yakılan günah sunusunun külünden koyun, üstüne duru su dökeceksiniz.
18 Sa’an nan wanda yake tsarkakakke, zai ɗauki hizzob yă tsoma a ruwa, yă yayyafa a tentin da dukan kayayyakinsa, da kuma a kan mutanen da suke wurin. Dole kuma yă yayyafa ruwan a kan duk wanda ya taɓa ƙashin mutu, ko kabari, ko kuma wanda aka kashe, ko wanda ya yi mutuwa ta Allah.
Temiz sayılan bir adam mercanköşkotunu alıp suya batıracak. Sonra çadırın, bütün eşyaların ve orada bulunanların üzerine serpecek. Kemiğe, öldürülmüş ya da doğal ölümle ölmüş kişiye ya da mezara dokunanın üzerine de suyu serpecek.
19 A rana ta uku, da ta bakwai kuma mai tsarkakewa zai yayyafa wa marar tsarkin ruwa, a rana ta bakwai kuma yă tsarkake shi. Wanda aka tsarkaken kuwa, dole yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka da yamma, zai kuma tsarkaka.
Temiz sayılan adam, üçüncü ve yedinci gün kirli sayılanın üzerine suyu serpecek. Yedinci gün onu arındıracak. Arınan kişi giysilerini yıkayacak, yıkanacak ve akşam temiz sayılacak.
20 Amma in wanda yake da ƙazanta bai tsarkake kansa ba, dole a ware shi daga cikin jama’a, domin ya ƙazantar da wuri mai tsarki na Ubangiji. Ba a yayyafa masa ruwa na tsarkakewa ba, ya zama da ƙazanta.
Ancak, kirli sayılan biri kendini arındırmazsa topluluğun arasından atılmalı. Çünkü RAB'bin Tapınağı'nı kirletmiştir. Temizlenme suyu üzerine dökülmediği için kirli sayılır.
21 Wannan za tă zama musu dawwammamiyar farilla. “Mutumin da ya yayyafa ruwa na tsarkakewa, shi ma dole yă wanke rigarsa. Duk wanda kuma ya taɓa ruwan tsarkakewa, zai kasance da ƙazanta har yamma.
Onlar için bu kural kalıcı olacaktır. Temizlenme suyunu serpen kişi de giysisini yıkamalı. Temizlenme suyuna dokunan kişi akşama dek kirli sayılacak.
22 Duk abin da mai ƙazanta ya taɓa, ya ƙazantu, kowa kuma ya taɓa wannan abu, ya ƙazantu ke nan, har yamma.”
Kirli sayılan birinin dokunduğu nesne kirli sayılır; o nesneye dokunan da akşama dek kirli sayılır.”