< Ƙidaya 19 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
Yahweh falou com Moisés e com Arão, dizendo:
2 “Wannan ita ce ƙa’ida wadda Ubangiji ya umarta. Faɗa wa Isra’ilawa su kawo maka jan karsana marar lahani, ko marar aibi wadda ba a taɓa sa ta tă yi noma ba.
“Este é o estatuto da lei que Yahweh ordenou. Diga aos filhos de Israel que lhe tragam uma novilha vermelha sem mancha, na qual não há defeito, e que nunca foi jungida.
3 Ka ba wa Eleyazar firist; a kuma kai ta bayan sansani, a yanka a gaban Eleyazar.
Você a entregará a Eleazar, o sacerdote, e ele a trará para fora do acampamento, e alguém a matará diante de sua face.
4 Sa’an nan Eleyazar firist zai ɗiba jininta a yatsarsa, yă yayyafa sau bakwai wajen gaban Tentin Sujada.
Eleazar, o sacerdote, tomará um pouco do sangue dela com o dedo, e aspergirá o sangue dela em direção à frente da Tenda da Reunião sete vezes.
5 Sa’an nan a ƙone dukan karsanar, haɗe da fatarta, naman, jinin da kayan cikin, yayinda Eleyazar yake kallo.
A novilha será queimada à sua vista; sua pele, e sua carne, e seu sangue, com seu esterco, será queimado.
6 Firist zai ɗauki itacen al’ul, da hizzob, da jan ulu, yă jefa su a kan karsanar da ake ƙonewa.
O padre pegará madeira de cedro, hissopo e escarlate e atirá-la-á no meio da queima da novilha.
7 Bayan haka, dole firist yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka. Sa’an nan zai iya shiga cikin sansani, amma zai kasance da ƙazanta har yamma.
Então o sacerdote lavará suas vestes, e banhará sua carne em água, e depois entrará no acampamento, e o sacerdote ficará imundo até a noite.
8 Dole mutumin da ya ƙone ta yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka, shi ma zai kasance da ƙazanta har yamma.
Aquele que a queimar lavará suas vestes em água, e banhará sua carne em água, e será imundo até a noite.
9 “Mutumin da yake da tsarki, zai tara tokar karsanar, yă sa ta a wurin da yake da tsabta a bayan sansani. Jama’ar Isra’ilawa ne za su adana shi don amfani a ruwan tsabtaccewa; wannan domin tsarkakewa ne daga zunubi.
“Um homem limpo recolherá as cinzas da novilha e as depositará fora do acampamento em um lugar limpo; e será guardado para a congregação das crianças de Israel para uso na água para limpeza de impurezas. É uma oferta pelo pecado.
10 Dole mutumin da ya tara tokar karsanar yă wanke rigunarsa, zai kuwa kasance da ƙazanta har yamma. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta har abada ga Isra’ilawa, da kuma baƙin da suke zama a cikinsu.
Aquele que recolher as cinzas da novilha lavará suas roupas, e ficará imundo até a noite. Será para os filhos de Israel, e para o estrangeiro que vive como um estrangeiro entre eles, por um estatuto para sempre.
11 “Duk wanda ya taɓa gawa, zai kasance da ƙazanta har kwana bakwai.
“Aquele que tocar o cadáver de qualquer homem será imundo por sete dias.
12 Dole yă tsarkake kansa da ruwa a rana ta uku, da kuma a rana ta bakwai; sa’an nan zai zama da tsarki. Amma in bai tsarkake kansa a rana ta uku da kuma a rana ta bakwai ba, ba zai kasance da tsarki ba.
Ele se purificará com água no terceiro dia, e no sétimo dia estará limpo; mas se não se purificar no terceiro dia, então no sétimo dia não estará limpo.
13 Duk wanda ya taɓa gawar wani, bai kuma tsarkake kansa ba, ya ƙazantar da tabanakul na Ubangiji ke nan. Dole a ware wannan mutum daga cikin Isra’ilawa. Gama ba a yayyafa ruwan tsabtaccewa a kansa ba; ya ƙazantu, ya kasance da ƙazanta ke nan.
Quem tocar um morto, o corpo de um homem que morreu, e não se purificar, profanará o tabernáculo de Javé; e essa alma será cortada de Israel; porque a água para a impureza não foi aspergida sobre ele, ele será imundo. Sua impureza ainda está sobre ele.
14 “Ga ƙa’idar da za a bi in mutum ya mutu a cikin tenti. Duk wanda ya shiga tentin, kuma duk wanda yake cikinsa, za su zama da ƙazanta har kwana bakwai,
“Esta é a lei quando um homem morre em uma tenda: todos que entram na tenda, e todos que estão na tenda, devem estar imundos sete dias.
15 kuma kowane abin da ake zuba kaya, wanda ba shi da murfi a kansa, zai zama da ƙazanta.
Todo recipiente aberto, que não tem cobertura presa, é imundo.
16 “Wanda duk yake a fili, ya kuma taɓa gawa wanda aka kashe da takobi, ko wanda ya mutu mutuwar Allah, ko ƙashin mutum, ko kabari, zai ƙazantu har bakwai.
“Quem no campo aberto tocar alguém que for morto com uma espada, ou um cadáver, ou um osso de um homem, ou uma sepultura, será imundo sete dias.
17 “Ga wanda ya ƙazantu kuwa, a ɗiba toka daga hadaya ta ƙonawa ta tsarkakewa, a zuba a cikin tulu, sa’an nan a zuba ruwa mai gudu a kansu.
“Para os impuros, eles devem tomar das cinzas da queima da oferta pelo pecado; e água corrente deve ser derramada sobre eles em um recipiente.
18 Sa’an nan wanda yake tsarkakakke, zai ɗauki hizzob yă tsoma a ruwa, yă yayyafa a tentin da dukan kayayyakinsa, da kuma a kan mutanen da suke wurin. Dole kuma yă yayyafa ruwan a kan duk wanda ya taɓa ƙashin mutu, ko kabari, ko kuma wanda aka kashe, ko wanda ya yi mutuwa ta Allah.
Uma pessoa limpa pegará o hissopo, mergulhá-lo-á na água e aspergi-lo-á sobre a tenda, sobre todos os vasos, sobre as pessoas que lá estavam e sobre aquele que tocou o osso, ou o morto, ou o morto, ou a sepultura.
19 A rana ta uku, da ta bakwai kuma mai tsarkakewa zai yayyafa wa marar tsarkin ruwa, a rana ta bakwai kuma yă tsarkake shi. Wanda aka tsarkaken kuwa, dole yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka da yamma, zai kuma tsarkaka.
A pessoa limpa deve aspergir sobre o impuro no terceiro dia, e no sétimo dia. No sétimo dia, ele o purificará. Ele lavará suas roupas e se banhará em água, e será limpo à noite.
20 Amma in wanda yake da ƙazanta bai tsarkake kansa ba, dole a ware shi daga cikin jama’a, domin ya ƙazantar da wuri mai tsarki na Ubangiji. Ba a yayyafa masa ruwa na tsarkakewa ba, ya zama da ƙazanta.
Mas o homem que for imundo, e não se purificar, essa alma será extirpada do meio da assembléia, porque contaminou o santuário de Iavé. A água para a impureza não foi aspergida sobre ele. Ele é impuro.
21 Wannan za tă zama musu dawwammamiyar farilla. “Mutumin da ya yayyafa ruwa na tsarkakewa, shi ma dole yă wanke rigarsa. Duk wanda kuma ya taɓa ruwan tsarkakewa, zai kasance da ƙazanta har yamma.
Será um estatuto perpétuo para eles. Aquele que asperge a água para a impureza lavará suas roupas, e aquele que toca a água para a impureza será imundo até a noite.
22 Duk abin da mai ƙazanta ya taɓa, ya ƙazantu, kowa kuma ya taɓa wannan abu, ya ƙazantu ke nan, har yamma.”
“O que a pessoa imunda tocar será imundo; e a alma que tocar será imunda até a noite”.

< Ƙidaya 19 >