< Ƙidaya 18 >
1 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Kai da’ya’yanka, da kuma iyalin mahaifinka za ku ɗauki hakkin abin da ya shafi Tentin Sujada, kai da’ya’yanka kaɗai za ku ɗauki hakkin aikinku wanda ya shafi firistoci.
Yahvé dit à Aaron: « Toi, tes fils et la maison de tes pères avec toi, vous porterez l'iniquité du sanctuaire; toi et tes fils avec toi, vous porterez l'iniquité de votre sacerdoce.
2 Ka kawo’yan’uwanka Lawiyawa daga kabilar kakanka tare da kai, don su taimake ka sa’ad da kai da’ya’yanka kuke hidima a gaban Tentin Sujada.
Fais aussi approcher de toi tes frères, la tribu de Lévi, la tribu de ton père, afin qu'ils soient associés à toi et qu'ils te servent; mais toi et tes fils avec toi, vous serez devant la tente du témoignage.
3 Za su kasance a ƙarƙashinka, su ne kuma za su yi dukan hidima ta Tenti, amma kada su je kusa da kayayyakin wuri mai tsarki, ko bagade, in ba haka ba, da kai da su, za ku mutu.
Ils observeront tes ordres et les devoirs de toute la tente; seulement, ils ne s'approcheront pas des ustensiles du sanctuaire ni de l'autel, afin qu'ils ne meurent pas, ni eux ni toi.
4 Za su haɗa hannu tare da kai su ɗauki nauyin lura da Tentin Sujada, dukan ayyuka a Tenti, ba kuma wanda zai zo kusa da inda kake.
Ils s'attacheront à toi et garderont la responsabilité de la Tente de la Rencontre, pour tout le service de la Tente. L'étranger ne s'approchera pas de toi.
5 “Kai ne za ka ɗauki nauyin lura da wuri mai tsarki da bagade, domin kada fushi yă sāke fāɗa a kan Isra’ilawa.
Vous accomplirez les fonctions du sanctuaire et de l'autel, afin qu'il n'y ait plus de colère contre les enfants d'Israël.
6 Ni da kaina na zaɓo’yan’uwanka Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa a matsayin kyauta a gare ku, keɓaɓɓu don Ubangiji, domin su yi hidima a Tentin Sujada.
Voici, j'ai pris moi-même vos frères les Lévites parmi les enfants d'Israël. Ils te sont offerts, ils sont consacrés à l'Éternel, pour faire le service de la Tente de la Rencontre.
7 Amma kai ne kaɗai da’ya’yanka za ku yi aiki a matsayin firistoci game da kowane abu a Tentin Sujada da kuma bayan labule. Ina ba ka aikin firist, yă zama naka. Duk wani kuma da ya zo kusa da wuri mai tsarki, dole a kashe shi.”
Toi et tes fils avec toi, vous exercerez votre sacerdoce pour tout ce qui concerne l'autel et ce qui est en deçà du voile. Tu feras le service. Je vous fais don du service de la prêtrise. L'étranger qui s'approchera sera mis à mort. »
8 Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Na ba ka aikin lura da hadayun da za a miƙa mini, dukan tsarkakan hadayun da Isra’ilawa suka ba ni, na ba ka su su zama rabonka da na’ya’yanka har abada.
Yahvé parla à Aaron: « Voici, je t'ai donné moi-même l'ordre d'offrir mes offrandes par agitation, toutes les choses saintes des enfants d'Israël. Je te les ai données, à cause de l'onction, ainsi qu'à tes fils, comme une part pour toujours.
9 Kai za ka riƙe sashe mafi tsarki na hadayun da suka ragu daga wuta. Daga dukan kyautai mafi tsarki na hadayun da suka miƙa mini, ko ta gari, ko don zunubi, ko kuma don laifi, wannan kashi naka ne da’ya’yanka.
Voici ce qui vous appartiendra parmi les choses très saintes du feu: toute offrande qu'ils m'offriront, toute offrande de farine, tout sacrifice pour le péché et tout sacrifice de culpabilité, sera très sainte pour vous et pour vos fils.
10 Ku ci shi a matsayin abu mafi tsarki; kowane namiji zai ci. Dole ku ɗauke shi da tsarki.
Vous en mangerez comme des choses très saintes. Tout mâle en mangera. Ce sera pour vous une chose sainte.
11 “Har yanzu kuma duk abin da aka keɓe daga kyautai na dukan hadayun kaɗawa na Isra’ilawa naka ne. Na ba da wannan gare ka da’ya’yanka maza da mata, a kowane lokaci. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
« Ceci est aussi à toi: l'offrande de leurs dons, toutes les offrandes des enfants d'Israël. Je te les ai données, à toi, à tes fils et à tes filles avec toi, comme une part pour toujours. Tous ceux qui sont purs dans ta maison en mangeront.
12 “Na ba ka duk man zaitun mafi kyau, da ruwan inabi mafi kyau duka, da hatsi mafi kyau duka na nunan farinsu da suke bayarwa ga Ubangiji.
« Je te donne tout le meilleur de l'huile, tout le meilleur de la vendange et du blé, les prémices de ce qu'ils apportent à l'Éternel.
13 Dukan nunan fari na ƙasar da suke kawo wa Ubangiji, zai zama naka. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
Les prémices de tout ce qui se trouve dans leur pays, qu'ils apporteront à l'Éternel, seront à toi. Tous ceux qui sont propres dans votre maison en mangeront.
14 “Kome a Isra’ila da aka keɓe wa Ubangiji, zai zama naka.
« Tout ce qui est consacré en Israël sera à toi.
15 Kowane haihuwar fari, ta mutum, ko ta dabba da suka miƙa wa Ubangiji, naka ne. Amma ka fanshi kowace haihuwar fari ta mutum, ko ta dabbar da take haram.
Tout ce qui ouvre le ventre, de toute chair qu'on offre à l'Éternel, tant des hommes que des animaux, sera à vous. Toutefois, vous rachèterez les premiers-nés des hommes et vous rachèterez les premiers-nés des animaux impurs.
16 Sa’ad da suke wata ɗaya da haihuwa, dole a fanshe su a bakin shekel biyar-biyar, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri da ake amfani da shi, wanda nauyinsa ya kai gera ashirin.
Tu rachèteras ceux d'entre eux qui sont âgés d'un mois, selon ton estimation, pour cinq sicles d'argent, selon le sicle du sanctuaire, qui pèse vingt gérachs.
17 “Amma kada ka fanshe ɗan fari na saniya, tunkiya, ko akuya; gama suna da tsarki. Ka yayyafa jininsu a bisan bagade, ka kuma ƙone kitsensu kamar hadayar da ka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
« Mais tu ne rachèteras pas le premier-né d'une vache, ni le premier-né d'une brebis, ni le premier-né d'une chèvre. Ils sont saints. Tu feras l'aspersion de leur sang sur l'autel, et tu brûleras leur graisse en offrande consumée par le feu, comme une odeur agréable à Yahvé.
18 Namansu zai zama naka, haka ma ƙirji na kaɗawa da cinyar dama za su zama naka.
Leur viande sera à toi, comme la poitrine offerte par onction et comme la cuisse droite, elle sera à toi.
19 Kome da aka keɓe daga tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka miƙa wa Ubangiji, na ba ka, da kai da’ya’yanka maza da mata a matsayin zaunannen rabo. Wannan madawwamin alkawarin gishiri ne a gaban Ubangiji dominka da zuriyarka.”
Toutes les offrandes par ondulation des choses saintes que les enfants d'Israël offrent à l'Éternel, je vous les donne, à vous, à vos fils et à vos filles avec vous, comme une part pour toujours. C'est une alliance de sel pour toujours devant l'Éternel, pour toi et pour ta descendance avec toi. »
20 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Ba ka da gādo a ƙasarsu, ba kuwa za ka sami rabo daga cikinsu ba; ni ne rabonka da gādonka a cikin Isra’ilawa.
Yahvé dit à Aaron: « Tu n'auras pas d'héritage dans leur pays, et tu n'auras pas de part au milieu d'eux. Je suis ta part et ton héritage parmi les enfants d'Israël.
21 “Na ba wa Lawiyawa dukan zakka na Isra’ilawa a matsayin gādonsu, saboda aikin da suke yi yayinda suke hidima a Tentin Sujada.
« Aux fils de Lévi, voici, j'ai donné en héritage toute la dîme en Israël, en contrepartie du service qu'ils font, le service de la tente d'assignation.
22 Daga yanzu zuwa gaba, kada Isra’ilawa su yi kusa da Tentin Sujada, in ba haka ba kuwa su sha hukuncin zunubinsu, su kuma mutu.
Désormais, les enfants d'Israël ne s'approcheront plus de la Tente de la Rencontre, de peur de porter le péché et de mourir.
23 Lawiyawa ne za su yi aikin Tentin Sujada, su kuma ɗauki nauyin kowane laifin da aka aikata a wurin. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce daga yanzu har tsararraki masu zuwa. Ba za su sami gādo a cikin Isra’ilawa ba.
Mais les Lévites feront le service de la Tente d'assignation, et ils porteront leur faute. Ce sera une loi pour toujours, de génération en génération. Ils n'auront pas d'héritage parmi les enfants d'Israël.
24 A maimako haka, na ba wa Lawiyawa zakka da Isra’ilawa suka kawo domin hadaya ga Ubangiji, a matsayin gādonsu. Shi ya sa na ce game da su, ‘Ba su da gādo a cikin Isra’ilawa.’”
En revanche, j'ai donné en héritage aux Lévites la dîme des enfants d'Israël, qu'ils offrent en offrande à Yahvé. C'est pourquoi je leur ai dit: « Ils n'auront pas d'héritage parmi les enfants d'Israël. »
25 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahvé parla à Moïse et dit:
26 “Ka yi wa Lawiyawa magana, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka karɓi zakka daga Isra’ila da na ba ku gādo, dole ku miƙa kashi ɗaya bisa goma na wannan zakka a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Tu parleras aux Lévites et tu leur diras: « Lorsque vous prélèverez sur les enfants d'Israël la dîme que je vous donne en héritage, vous en ferez une offrande pour Yahvé, la dîme de la dîme.
27 Za a lissafta hadayarku kamar hatsin da aka sussuka daga masussuka, ko ruwan inabi daga wurin matsewar inabi.
Ton offrande ondulatoire te sera créditée comme le grain de l'aire et comme la plénitude de la cuve.
28 Ta haka za ku miƙa hadaya ga Ubangiji daga cikin dukan zakkar da kuka karɓa daga wurin Isra’ilawa. Daga waɗannan zakka kuwa dole ku ba Haruna firist rabon Ubangiji.
C'est ainsi que tu présenteras à l'Éternel une offrande par ondulation de toutes les dîmes que tu recevras des enfants d'Israël, et tu en donneras une au prêtre Aaron.
29 Dole ku miƙa wa Ubangiji rabo mafi kyau da kuma sashi mafi tsarki na kowane abin da aka ba ku.’
De toutes vos offrandes, vous présenterez à Yahvé chaque offrande par ondulation, dans toutes ses parties les meilleures, même la partie sainte.''
30 “Ka faɗa wa Lawiyawa cewa, ‘Sa’ad da kuka miƙa sashi mafi kyau, za a lissafta shi a matsayin abin da ya fito daga masussuka, ko wurin matsewar ruwan inabi ne.
Tu leur diras: « Lorsque vous en aurez récolté le meilleur, il sera porté au crédit des Lévites comme le produit de l'aire de battage et comme le produit du pressoir.
31 Da kai da gidanka, za ku iya cin abin da ya rage a ko’ina, gama ladan aikinku ne a Tentin Sujada.
Vous pourrez en manger partout, vous et vos familles, car c'est votre récompense pour votre service dans la Tente de la Rencontre.
32 Ta wurin miƙa masa sashi mafi kyau, ba za ku zama masu laifi a wannan batu ba; ta haka ba za ku ƙazantar da tsarkakakkun hadayu na Isra’ilawa ba, ba kuwa za ku mutu ba.’”
Tu ne porteras pas de péché à cause d'elle, lorsque tu en auras tiré le meilleur. Tu ne profaneras pas les choses saintes des enfants d'Israël, afin de ne pas mourir.'"