< Ƙidaya 18 >

1 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Kai da’ya’yanka, da kuma iyalin mahaifinka za ku ɗauki hakkin abin da ya shafi Tentin Sujada, kai da’ya’yanka kaɗai za ku ɗauki hakkin aikinku wanda ya shafi firistoci.
And Jehovah saith unto Aaron, 'Thou, and thy sons, and the house of thy father with thee, do bear the iniquity of the sanctuary; and thou, and thy sons with thee, do bear the iniquity of your priesthood;
2 Ka kawo’yan’uwanka Lawiyawa daga kabilar kakanka tare da kai, don su taimake ka sa’ad da kai da’ya’yanka kuke hidima a gaban Tentin Sujada.
and also thy brethren, the tribe of Levi, the tribe of thy father, bring near with thee, and they are joined unto thee, and serve thee, even thou and thy sons with thee, before the tent of the testimony.
3 Za su kasance a ƙarƙashinka, su ne kuma za su yi dukan hidima ta Tenti, amma kada su je kusa da kayayyakin wuri mai tsarki, ko bagade, in ba haka ba, da kai da su, za ku mutu.
'And they have kept thy charge, and the charge of all the tent; only, unto the vessels of the sanctuary and unto the altar they do not come near, and they die not, either they or you;
4 Za su haɗa hannu tare da kai su ɗauki nauyin lura da Tentin Sujada, dukan ayyuka a Tenti, ba kuma wanda zai zo kusa da inda kake.
and they have been joined unto thee, and have kept the charge of the tent of meeting, for all the service of the tent; and a stranger doth not come near unto you;
5 “Kai ne za ka ɗauki nauyin lura da wuri mai tsarki da bagade, domin kada fushi yă sāke fāɗa a kan Isra’ilawa.
and ye have kept the charge of the sanctuary, and the charge of the altar, and there is no more wrath against the sons of Israel.
6 Ni da kaina na zaɓo’yan’uwanka Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa a matsayin kyauta a gare ku, keɓaɓɓu don Ubangiji, domin su yi hidima a Tentin Sujada.
'And I, lo, I have taken your brethren the Levites from the midst of the sons of Israel; to you a gift they are given by Jehovah, to do the service of the tent of meeting;
7 Amma kai ne kaɗai da’ya’yanka za ku yi aiki a matsayin firistoci game da kowane abu a Tentin Sujada da kuma bayan labule. Ina ba ka aikin firist, yă zama naka. Duk wani kuma da ya zo kusa da wuri mai tsarki, dole a kashe shi.”
and thou, and thy sons with thee, do keep your priesthood, for everything of the altar, and within the vail, and ye have served; a service of gift I make your priesthood; and the stranger who is coming near is put to death.'
8 Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Na ba ka aikin lura da hadayun da za a miƙa mini, dukan tsarkakan hadayun da Isra’ilawa suka ba ni, na ba ka su su zama rabonka da na’ya’yanka har abada.
And Jehovah speaketh unto Aaron: 'And I, lo, I have given to thee the charge of My heave-offerings, of all the hallowed things of the sons of Israel — to thee I have given them for the anointing, and to thy sons, by a statute age-during.
9 Kai za ka riƙe sashe mafi tsarki na hadayun da suka ragu daga wuta. Daga dukan kyautai mafi tsarki na hadayun da suka miƙa mini, ko ta gari, ko don zunubi, ko kuma don laifi, wannan kashi naka ne da’ya’yanka.
This is thine of the most holy things, from the fire: all their offering, to all their present, and to all their sin-offering, and to all their guilt-offering, which they give back to Me, is most holy to thee, and to thy sons;
10 Ku ci shi a matsayin abu mafi tsarki; kowane namiji zai ci. Dole ku ɗauke shi da tsarki.
in the holy of holies thou dost eat it; every male doth eat it; holy it is to thee.
11 “Har yanzu kuma duk abin da aka keɓe daga kyautai na dukan hadayun kaɗawa na Isra’ilawa naka ne. Na ba da wannan gare ka da’ya’yanka maza da mata, a kowane lokaci. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
'And this [is] thine: the heave-offering of their gift, to all the wave-offerings of the sons of Israel, to thee I have given them, and to thy sons, and to thy daughters with thee, by a statute age-during; every clean one in thy house doth eat it;
12 “Na ba ka duk man zaitun mafi kyau, da ruwan inabi mafi kyau duka, da hatsi mafi kyau duka na nunan farinsu da suke bayarwa ga Ubangiji.
all the best of the oil, and all the best of the new wine, and wheat — their first -[fruits] which they give to Jehovah — to thee I have given them.
13 Dukan nunan fari na ƙasar da suke kawo wa Ubangiji, zai zama naka. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
'The first-fruits of all that [is] in their land, which they bring in to Jehovah, are thine; every clean one in thy house doth eat it;
14 “Kome a Isra’ila da aka keɓe wa Ubangiji, zai zama naka.
every devoted thing in Israel is thine,
15 Kowane haihuwar fari, ta mutum, ko ta dabba da suka miƙa wa Ubangiji, naka ne. Amma ka fanshi kowace haihuwar fari ta mutum, ko ta dabbar da take haram.
every one opening a womb of all flesh which they bring near to Jehovah, among man and among beast, is thine; only, thou dost certainly ransom the first-born of man, and the firstling of the unclean beast thou dost ransom.
16 Sa’ad da suke wata ɗaya da haihuwa, dole a fanshe su a bakin shekel biyar-biyar, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri da ake amfani da shi, wanda nauyinsa ya kai gera ashirin.
'And their ransomed ones from a son of a month, thou dost ransom with thy valuation, of silver, five shekels, by the shekel of the sanctuary, twenty gerahs it [is].
17 “Amma kada ka fanshe ɗan fari na saniya, tunkiya, ko akuya; gama suna da tsarki. Ka yayyafa jininsu a bisan bagade, ka kuma ƙone kitsensu kamar hadayar da ka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
'Only, the firstling of a cow, or the firstling of a sheep, or the firstling of a goat, thou dost not ransom, holy they [are]: their blood thou dost sprinkle on the altar, and of their fat thou makest perfume, a fire-offering of sweet fragrance to Jehovah,
18 Namansu zai zama naka, haka ma ƙirji na kaɗawa da cinyar dama za su zama naka.
and their flesh is thine, as the breast of the wave-offering, and as the right leg, it is thine;
19 Kome da aka keɓe daga tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka miƙa wa Ubangiji, na ba ka, da kai da’ya’yanka maza da mata a matsayin zaunannen rabo. Wannan madawwamin alkawarin gishiri ne a gaban Ubangiji dominka da zuriyarka.”
all the heave-offerings of the holy things which the sons of Israel lift up to Jehovah I have given to thee and to thy sons, and to thy daughters with thee, by a statute age-during, a covenant of salt, age-during it [is] before Jehovah, to thee and to thy seed with thee.'
20 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Ba ka da gādo a ƙasarsu, ba kuwa za ka sami rabo daga cikinsu ba; ni ne rabonka da gādonka a cikin Isra’ilawa.
And Jehovah saith unto Aaron, 'In their land thou dost not inherit, and a portion thou hast not in their midst: I [am] thy portion, and thine inheritance in the midst of the sons of Israel;
21 “Na ba wa Lawiyawa dukan zakka na Isra’ilawa a matsayin gādonsu, saboda aikin da suke yi yayinda suke hidima a Tentin Sujada.
and to the sons of Levi, lo, I have given all the tenth in Israel for inheritance in exchange for their service which they are serving — the service of the tent of meeting.
22 Daga yanzu zuwa gaba, kada Isra’ilawa su yi kusa da Tentin Sujada, in ba haka ba kuwa su sha hukuncin zunubinsu, su kuma mutu.
'And the sons of Israel come no more near unto the tent of meeting, to bear sin, to die,
23 Lawiyawa ne za su yi aikin Tentin Sujada, su kuma ɗauki nauyin kowane laifin da aka aikata a wurin. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce daga yanzu har tsararraki masu zuwa. Ba za su sami gādo a cikin Isra’ilawa ba.
and the Levites have done the service of the tent of meeting, and they — they bear their iniquity; a statute age-during to your generations, that in the midst of the sons of Israel they have no inheritance;
24 A maimako haka, na ba wa Lawiyawa zakka da Isra’ilawa suka kawo domin hadaya ga Ubangiji, a matsayin gādonsu. Shi ya sa na ce game da su, ‘Ba su da gādo a cikin Isra’ilawa.’”
but the tithe of the sons of Israel which they lift up to Jehovah, a heave-offering, I have given to the Levites for inheritance; therefore I have said of them, In the midst of the sons of Israel they have no inheritance.'
25 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah speaketh unto Moses, saying,
26 “Ka yi wa Lawiyawa magana, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka karɓi zakka daga Isra’ila da na ba ku gādo, dole ku miƙa kashi ɗaya bisa goma na wannan zakka a matsayin hadaya ga Ubangiji.
'And unto the Levites thou dost speak; and thou hast said unto them, When ye take from the sons of Israel the tithe which I have given to you from them, for your inheritance, then ye have lifted up from it the heave-offering of Jehovah, a tithe of the tithe;
27 Za a lissafta hadayarku kamar hatsin da aka sussuka daga masussuka, ko ruwan inabi daga wurin matsewar inabi.
and your heave-offering hath been reckoned to you as corn from the threshing-floor, and as fulness from the wine-vat;
28 Ta haka za ku miƙa hadaya ga Ubangiji daga cikin dukan zakkar da kuka karɓa daga wurin Isra’ilawa. Daga waɗannan zakka kuwa dole ku ba Haruna firist rabon Ubangiji.
so ye do lift up — ye also — the heave-offering of Jehovah from all your tithes which ye receive from the sons of Israel; and ye have given from it the heave-offering of Jehovah to Aaron the priest;
29 Dole ku miƙa wa Ubangiji rabo mafi kyau da kuma sashi mafi tsarki na kowane abin da aka ba ku.’
out of all your gifts ye do lift up the whole heave-offering of Jehovah; out of all its fat, — its hallowed part — out of it.
30 “Ka faɗa wa Lawiyawa cewa, ‘Sa’ad da kuka miƙa sashi mafi kyau, za a lissafta shi a matsayin abin da ya fito daga masussuka, ko wurin matsewar ruwan inabi ne.
'And thou hast said unto them, In your lifting up its fat out of it, then it hath been reckoned to the Levites, as increase of a threshing-floor, and as increase of a wine-vat;
31 Da kai da gidanka, za ku iya cin abin da ya rage a ko’ina, gama ladan aikinku ne a Tentin Sujada.
and ye have eaten it in every place, ye and your households, for it [is] your hire in exchange for your service in the tent of meeting;
32 Ta wurin miƙa masa sashi mafi kyau, ba za ku zama masu laifi a wannan batu ba; ta haka ba za ku ƙazantar da tsarkakakkun hadayu na Isra’ilawa ba, ba kuwa za ku mutu ba.’”
and ye bear no sin for it, in your lifting up its fat out of it, and the holy things of the sons of Israel ye do not pollute, and ye die not.'

< Ƙidaya 18 >