< Ƙidaya 18 >
1 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Kai da’ya’yanka, da kuma iyalin mahaifinka za ku ɗauki hakkin abin da ya shafi Tentin Sujada, kai da’ya’yanka kaɗai za ku ɗauki hakkin aikinku wanda ya shafi firistoci.
And the Lord spoke to Aaron, saying, Thou and thy sons and thy father's house shall bear the sins of the holy things, and thou and thy sons shall bear the iniquity of your priesthood.
2 Ka kawo’yan’uwanka Lawiyawa daga kabilar kakanka tare da kai, don su taimake ka sa’ad da kai da’ya’yanka kuke hidima a gaban Tentin Sujada.
And take to thyself thy brethren the tribe of Levi, the family of thy father, and let them be joined to thee, and let them minister to thee; and thou and thy sons with thee [shall minister] before the tabernacle of witness.
3 Za su kasance a ƙarƙashinka, su ne kuma za su yi dukan hidima ta Tenti, amma kada su je kusa da kayayyakin wuri mai tsarki, ko bagade, in ba haka ba, da kai da su, za ku mutu.
And they shall keep thy charges, and the charges of the tabernacle; only they shall not approach the holy vessels and the altar, so both they and you shall not die.
4 Za su haɗa hannu tare da kai su ɗauki nauyin lura da Tentin Sujada, dukan ayyuka a Tenti, ba kuma wanda zai zo kusa da inda kake.
And they shall be joined to thee, and shall keep the charges of the tabernacle of witness, in all the services of the tabernacle; and a stranger shall not approach to thee.
5 “Kai ne za ka ɗauki nauyin lura da wuri mai tsarki da bagade, domin kada fushi yă sāke fāɗa a kan Isra’ilawa.
And ye shall keep the charges of the holy things, and the charges of the altar, and [so] there shall not be anger among the children of Israel.
6 Ni da kaina na zaɓo’yan’uwanka Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa a matsayin kyauta a gare ku, keɓaɓɓu don Ubangiji, domin su yi hidima a Tentin Sujada.
And I have taken your brethren the Levites out of the midst of the children of Israel, a present given to the Lord, to minister in the services of the tabernacle of witness.
7 Amma kai ne kaɗai da’ya’yanka za ku yi aiki a matsayin firistoci game da kowane abu a Tentin Sujada da kuma bayan labule. Ina ba ka aikin firist, yă zama naka. Duk wani kuma da ya zo kusa da wuri mai tsarki, dole a kashe shi.”
And thou and thy sons after thee shall keep up your priestly ministration, according to the whole manner of the altar, and that which is within the veil; and ye shall minister in the services as the office of your priesthood; and the stranger that comes near shall die.
8 Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Na ba ka aikin lura da hadayun da za a miƙa mini, dukan tsarkakan hadayun da Isra’ilawa suka ba ni, na ba ka su su zama rabonka da na’ya’yanka har abada.
And the Lord said to Aaron, And, behold, I have given you the charge of the first-fruits of all things consecrated to me by the children of Israel; and I have given them to thee as an honour, and to thy sons after thee for a perpetual ordinance.
9 Kai za ka riƙe sashe mafi tsarki na hadayun da suka ragu daga wuta. Daga dukan kyautai mafi tsarki na hadayun da suka miƙa mini, ko ta gari, ko don zunubi, ko kuma don laifi, wannan kashi naka ne da’ya’yanka.
And let this be to you from all the holy things that are consecrated [to me, even] the burnt-offerings, from all their gifts, and from all their sacrifices, and from every trespass-offering of theirs, and from all their sin-offerings, whatever things they give to me of all their holy things, they shall be thine and thy sons'.
10 Ku ci shi a matsayin abu mafi tsarki; kowane namiji zai ci. Dole ku ɗauke shi da tsarki.
In the most holy place shall ye eat them; every male shall eat them, thou and thy sons: they shall be holy to thee.
11 “Har yanzu kuma duk abin da aka keɓe daga kyautai na dukan hadayun kaɗawa na Isra’ilawa naka ne. Na ba da wannan gare ka da’ya’yanka maza da mata, a kowane lokaci. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
And this shall be to you of the first-fruits of their gifts, of all the wave-offerings of the children of Israel; to thee have I given them and to thy sons and thy daughters with thee, a perpetual ordinance; every clean person in thy house shall eat them.
12 “Na ba ka duk man zaitun mafi kyau, da ruwan inabi mafi kyau duka, da hatsi mafi kyau duka na nunan farinsu da suke bayarwa ga Ubangiji.
Every first-offering of oil, and every first-offering of wine, their first-fruits of corn, whatsoever they may give to the Lord, to thee have I given them.
13 Dukan nunan fari na ƙasar da suke kawo wa Ubangiji, zai zama naka. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
All the first-fruits that are in their land, whatsoever they shall offer to the Lord, shall be thine: every clean person in thy house shall eat them.
14 “Kome a Isra’ila da aka keɓe wa Ubangiji, zai zama naka.
Every devoted thing among the children of Israel shall be thine.
15 Kowane haihuwar fari, ta mutum, ko ta dabba da suka miƙa wa Ubangiji, naka ne. Amma ka fanshi kowace haihuwar fari ta mutum, ko ta dabbar da take haram.
And every thing that opens the womb of all flesh, whatsoever they bring to the Lord, whether man or beast, shall be thine: only the first-born of men shall be surely redeemed, and thou shalt redeem the first-born of unclean cattle.
16 Sa’ad da suke wata ɗaya da haihuwa, dole a fanshe su a bakin shekel biyar-biyar, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri da ake amfani da shi, wanda nauyinsa ya kai gera ashirin.
And the redemption of them [shall be] from a month old; their valuation of five shekels—it is twenty oboli according to the holy shekel.
17 “Amma kada ka fanshe ɗan fari na saniya, tunkiya, ko akuya; gama suna da tsarki. Ka yayyafa jininsu a bisan bagade, ka kuma ƙone kitsensu kamar hadayar da ka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
But thou shalt not redeem the first-born of calves and the first-born of sheep and the first-born of goats; they are holy: and thou shalt pour their blood upon the altar, and thou shalt offer the fat as a burnt-offering for a smell of sweet savour to the Lord.
18 Namansu zai zama naka, haka ma ƙirji na kaɗawa da cinyar dama za su zama naka.
And the flesh shall be thine, as also the breast of the wave-offering and as the right shoulder, it shall be thine.
19 Kome da aka keɓe daga tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka miƙa wa Ubangiji, na ba ka, da kai da’ya’yanka maza da mata a matsayin zaunannen rabo. Wannan madawwamin alkawarin gishiri ne a gaban Ubangiji dominka da zuriyarka.”
Every special offering of the holy things, whatsoever the children of Israel shall specially offer to the Lord, I have given to thee and to thy sons and to thy daughters with thee, a perpetual ordinance: it is a covenant of salt for ever before the Lord, for thee and thy seed after thee.
20 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Ba ka da gādo a ƙasarsu, ba kuwa za ka sami rabo daga cikinsu ba; ni ne rabonka da gādonka a cikin Isra’ilawa.
And the Lord said to Aaron, Thou shalt have no inheritance in their land, neither shalt thou have any portion among them; for I [am] thy portion and thine inheritance in the midst of the children of Israel.
21 “Na ba wa Lawiyawa dukan zakka na Isra’ilawa a matsayin gādonsu, saboda aikin da suke yi yayinda suke hidima a Tentin Sujada.
And, behold, I have given to the sons of Levi every tithe in Israel for an inheritance for their services, whereinsoever they perform ministry in the tabernacle of witness.
22 Daga yanzu zuwa gaba, kada Isra’ilawa su yi kusa da Tentin Sujada, in ba haka ba kuwa su sha hukuncin zunubinsu, su kuma mutu.
And the children of Israel shall no more draw nigh to the tabernacle of witness to incur fatal guilt.
23 Lawiyawa ne za su yi aikin Tentin Sujada, su kuma ɗauki nauyin kowane laifin da aka aikata a wurin. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce daga yanzu har tsararraki masu zuwa. Ba za su sami gādo a cikin Isra’ilawa ba.
And the Levite himself shall perform the service of the tabernacle of witness; and they shall bear their iniquities, it is a perpetual statute throughout their generations; and in the midst of the children of Israel they shall not receive an inheritance.
24 A maimako haka, na ba wa Lawiyawa zakka da Isra’ilawa suka kawo domin hadaya ga Ubangiji, a matsayin gādonsu. Shi ya sa na ce game da su, ‘Ba su da gādo a cikin Isra’ilawa.’”
Because I have given as a distinct portion to the Levites for an inheritance the tithes of the children of Israel, whatsoever they shall offer to the Lord; therefore I said to them, In the midst of the children of Israel they shall have no inheritance.
25 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke to Moses, saying,
26 “Ka yi wa Lawiyawa magana, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka karɓi zakka daga Isra’ila da na ba ku gādo, dole ku miƙa kashi ɗaya bisa goma na wannan zakka a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Thou shalt also speak to the Levites, and shalt say to them, If ye take the tithe from the children of Israel, which I have given you from them for an inheritance, then shall ye separate from it a heave-offering to the Lord, a tenth of the tenth.
27 Za a lissafta hadayarku kamar hatsin da aka sussuka daga masussuka, ko ruwan inabi daga wurin matsewar inabi.
And your heave-offerings shall be reckoned to you as corn from the floor, and an offering from the wine-press.
28 Ta haka za ku miƙa hadaya ga Ubangiji daga cikin dukan zakkar da kuka karɓa daga wurin Isra’ilawa. Daga waɗannan zakka kuwa dole ku ba Haruna firist rabon Ubangiji.
So shall ye also separate them from all the offerings of the Lord out of all your tithes, whatsoever ye shall receive from the children of Israel; and ye shall give of them an offering to the Lord to Aaron the priest.
29 Dole ku miƙa wa Ubangiji rabo mafi kyau da kuma sashi mafi tsarki na kowane abin da aka ba ku.’
Of all your gifts ye shall offer an offering to the Lord, and of every first-fruit the consecrated part from it.
30 “Ka faɗa wa Lawiyawa cewa, ‘Sa’ad da kuka miƙa sashi mafi kyau, za a lissafta shi a matsayin abin da ya fito daga masussuka, ko wurin matsewar ruwan inabi ne.
And thou shalt say to them, When ye shall offer the first-fruits from it, then shall it be reckoned to the Levites as produce from the threshing-floor, and as produce from the wine-press.
31 Da kai da gidanka, za ku iya cin abin da ya rage a ko’ina, gama ladan aikinku ne a Tentin Sujada.
And ye shall eat it in any place, ye and your families; for this is your reward for your services in the tabernacle of witness.
32 Ta wurin miƙa masa sashi mafi kyau, ba za ku zama masu laifi a wannan batu ba; ta haka ba za ku ƙazantar da tsarkakakkun hadayu na Isra’ilawa ba, ba kuwa za ku mutu ba.’”
And ye shall not bear sin by reason of it, for ye shall have offered an offering of first-fruits from it, and ye shall not profane the holy things of the children of Israel, that ye die not.