< Ƙidaya 17 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah speaketh unto Moses, saying,
2 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka kuma karɓi sanduna goma sha biyu daga wurinsu, sanda guda daga kowane shugaban gidan kakanninsu. Ka rubuta sunan kowa a sandansa.
'Speak unto the sons of Israel, and take from them each a rod, for a father's house, from all their princes, for the house of their fathers, twelve rods; the name of each thou dost write on his rod,
3 A kan sandan Lawi kuwa ka rubuta sunan Haruna, gama dole a sami sanda ɗaya saboda shugaban gidan kakanninsu.
and Aaron's name thou dost write on the tribe of Levi; for one rod [is] for the head of their fathers' house:
4 Ka ajiye su a Tentin Sujada, a gaba akwatin Alkawari, inda zan sadu da kai.
and thou hast placed them in the tent of meeting, before the testimony, where I meet with you.
5 Sandan mutumin da na zaɓa zai yi toho, da haka zan raba kaina da gunagunin da Isra’ilawa suke yi.”
'And it hath come to pass, the man's rod on whom I fix doth flourish, and I have caused to cease from off me the murmurings of the sons of Israel, which they are murmuring against you.'
6 Saboda haka Musa ya yi magana da Isra’ilawa, sai shugabanninsu suka ba shi sanduna goma sha biyu, sanda ɗaya don shugaba, bisa ga gidajen kakanninsu, sandan Haruna kuma yana a cikinsu.
And Moses speaketh unto the sons of Israel, and all their princes give unto him one rod for a prince, one rod for a prince, for their fathers' house, twelve rods, and the rod of Aaron [is] in the midst of their rods;
7 Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada.
and Moses placeth the rods before Jehovah, in the tent of the testimony.
8 Kashegari da Musa ya shiga cikin Tentin Sujada sai ga sandan Haruna na gidan Lawiyawa ya yi toho, ya yi furanni, ya kuma yi’ya’yan almon.
And it cometh to pass, on the morrow, that Moses goeth in unto the tent of the testimony, and lo, the rod of Aaron hath flourished for the house of Levi, and is bringing out flourishing, and doth blossom blossoms, and doth produce almonds;
9 Sai Musa ya fitar wa dukan Isra’ilawa dukan sandunan da suke daga gaban Ubangiji. Suka duba, kowa kuma ya ɗauki sandansa.
and Moses bringeth out all the rods from before Jehovah, unto all the sons of Israel, and they look, and take each his rod.
10 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka mayar da sandan Haruna a akwatin Alkawari, don a ajiye shi alama ga masu tawaye. Wannan zai kawo ƙarshen gunaguninsu a kaina, domin kada su mutu.”
And Jehovah saith unto Moses, 'Put back the rod of Aaron, before the testimony, for a charge, for a sign to the sons of rebellion, and thou dost remove their murmurings from off me, and they do not die;'
11 Musa kuwa ya aikata kamar dai yadda Ubangiji ya umarce shi.
and Moses doth as Jehovah hath commanded him; so he hath done.
12 Sai Isra’ilawa suka ce wa Musa, “To, ai in haka ne, mun ƙare ke nan!
And the sons of Israel speak unto Moses, saying, 'Lo, we have expired; we have perished; we have all of us perished;
13 Idan an ce duk wanda ya zo kusa da tabanakul na Ubangiji zai mutu, ai rayuwarmu kamar mun mutu ke nan.”
any who is at all drawing near unto the tabernacle of Jehovah dieth; have we not been consumed — to expire?'