< Ƙidaya 17 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spak to Moises, `and seide, Speke thou to the sones of Israel,
2 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka kuma karɓi sanduna goma sha biyu daga wurinsu, sanda guda daga kowane shugaban gidan kakanninsu. Ka rubuta sunan kowa a sandansa.
and take thou yerdis, bi her kynredis, bi ech kynrede o yeerde, take thou of alle the princes of the lynagis twelue yerdis; and thou schalt write the name of each lynage aboue his yerde;
3 A kan sandan Lawi kuwa ka rubuta sunan Haruna, gama dole a sami sanda ɗaya saboda shugaban gidan kakanninsu.
forsothe the name of Aaron schal be in the lynage of Leuy, and o yerde schal conteyne alle the meynees of hem.
4 Ka ajiye su a Tentin Sujada, a gaba akwatin Alkawari, inda zan sadu da kai.
And thou schalt putte tho yerdis in the tabernacle of boond of pees, bifor the witnessyng, where Y schal speke to thee; the yerde of hym schal buriowne, whom Y schal chese of hem;
5 Sandan mutumin da na zaɓa zai yi toho, da haka zan raba kaina da gunagunin da Isra’ilawa suke yi.”
and Y schal refreyne fro me the playnyngis of the sones of Israel, bi whiche thei grutchen ayens you.
6 Saboda haka Musa ya yi magana da Isra’ilawa, sai shugabanninsu suka ba shi sanduna goma sha biyu, sanda ɗaya don shugaba, bisa ga gidajen kakanninsu, sandan Haruna kuma yana a cikinsu.
And Moyses spak to the sones of Israel; and alle princes yauen to hym yerdis, bi alle lynagis; and the yerdis weren twelue, without the yerde of Aaron.
7 Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada.
And whanne Moises hadde put tho yerdis bifor the Lord, in the tabernacle of witnessyng, he yede ayen in the day suynge,
8 Kashegari da Musa ya shiga cikin Tentin Sujada sai ga sandan Haruna na gidan Lawiyawa ya yi toho, ya yi furanni, ya kuma yi’ya’yan almon.
and founde that the yerde of Aaron, `in the hows of Leuy, buriounnede; and whanne knoppis weren greet, the blossoms `hadden broke out, whiche weren alargid in leeuys, and weren fourmed in to alemaundis.
9 Sai Musa ya fitar wa dukan Isra’ilawa dukan sandunan da suke daga gaban Ubangiji. Suka duba, kowa kuma ya ɗauki sandansa.
Therfor Moyses brouyte forth alle the yerdis fro the siyt of the Lord to al the sones of Israel; and thei sien, and resseyueden ech his yerde.
10 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka mayar da sandan Haruna a akwatin Alkawari, don a ajiye shi alama ga masu tawaye. Wannan zai kawo ƙarshen gunaguninsu a kaina, domin kada su mutu.”
And the Lord seide to Moises, Bere ayen the yerde of Aaron in to the tabernacle of witnessyng, that it be kept there in to `the signe of the rebel sones of Israel, and that her `playntis reste fro me, lest thei dien.
11 Musa kuwa ya aikata kamar dai yadda Ubangiji ya umarce shi.
And Moises dide, as the Lord comaundide.
12 Sai Isra’ilawa suka ce wa Musa, “To, ai in haka ne, mun ƙare ke nan!
Forsothe the sones of Israel seiden to Moises, Lo! we ben wastid, alle we perischiden;
13 Idan an ce duk wanda ya zo kusa da tabanakul na Ubangiji zai mutu, ai rayuwarmu kamar mun mutu ke nan.”
who euer neiyeth to the tabernacle of the Lord, he dieth; whethir we schulen be doon awei alle `til to deeth?

< Ƙidaya 17 >