< Ƙidaya 17 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
2 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka kuma karɓi sanduna goma sha biyu daga wurinsu, sanda guda daga kowane shugaban gidan kakanninsu. Ka rubuta sunan kowa a sandansa.
Speak unto the children of Israel, and take of them a staff, a staff for each father's house, of all their princes according to the houses of their fathers, twelve staves: thou shalt write each one's name upon his staff.
3 A kan sandan Lawi kuwa ka rubuta sunan Haruna, gama dole a sami sanda ɗaya saboda shugaban gidan kakanninsu.
And Aaron's name shalt thou write upon the staff of Levi; for one staff shall be for [each] head of their fathers' houses.
4 Ka ajiye su a Tentin Sujada, a gaba akwatin Alkawari, inda zan sadu da kai.
And thou shalt lay them up in the tent of meeting before the testimony, where I meet with you.
5 Sandan mutumin da na zaɓa zai yi toho, da haka zan raba kaina da gunagunin da Isra’ilawa suke yi.”
And it shall come to pass, that the man whom I shall choose, his staff shall bud forth; and I will make to cease from before me the murmurings of the children of Israel, that they murmur against you.
6 Saboda haka Musa ya yi magana da Isra’ilawa, sai shugabanninsu suka ba shi sanduna goma sha biyu, sanda ɗaya don shugaba, bisa ga gidajen kakanninsu, sandan Haruna kuma yana a cikinsu.
And Moses spoke to the children of Israel, and all their princes gave him a staff, one staff for each prince according to their fathers' houses, twelve staves, and the staff of Aaron was among their staves.
7 Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada.
And Moses laid the staves before Jehovah in the tent of the testimony.
8 Kashegari da Musa ya shiga cikin Tentin Sujada sai ga sandan Haruna na gidan Lawiyawa ya yi toho, ya yi furanni, ya kuma yi’ya’yan almon.
And it came to pass, when on the morrow Moses went into the tent of the testimony, behold, the staff of Aaron for the house of Levi had budded, and brought forth buds, and bloomed blossoms, and ripened almonds.
9 Sai Musa ya fitar wa dukan Isra’ilawa dukan sandunan da suke daga gaban Ubangiji. Suka duba, kowa kuma ya ɗauki sandansa.
And Moses brought out all the staves from before Jehovah to all the children of Israel, and they looked and took each one his staff.
10 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka mayar da sandan Haruna a akwatin Alkawari, don a ajiye shi alama ga masu tawaye. Wannan zai kawo ƙarshen gunaguninsu a kaina, domin kada su mutu.”
And Jehovah said to Moses, Bring Aaron's staff again before the testimony, to be kept as a token for the sons of rebellion, that thou mayest put an end to their murmurings before me, that they may not die.
11 Musa kuwa ya aikata kamar dai yadda Ubangiji ya umarce shi.
And Moses did so: as Jehovah had commanded him, so did he.
12 Sai Isra’ilawa suka ce wa Musa, “To, ai in haka ne, mun ƙare ke nan!
And the children of Israel spoke to Moses, saying, Lo, we expire, we perish, we all perish.
13 Idan an ce duk wanda ya zo kusa da tabanakul na Ubangiji zai mutu, ai rayuwarmu kamar mun mutu ke nan.”
Every one that comes at all near to the tabernacle of Jehovah shall die: shall we then expire altogether?