< Ƙidaya 17 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spake unto Moses, saying,
2 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka kuma karɓi sanduna goma sha biyu daga wurinsu, sanda guda daga kowane shugaban gidan kakanninsu. Ka rubuta sunan kowa a sandansa.
Speak unto the children of Israel, and take of them rods, one for each fathers’ house, of all their princes according to their fathers’ houses, twelve rods: write thou every man’s name upon his rod.
3 A kan sandan Lawi kuwa ka rubuta sunan Haruna, gama dole a sami sanda ɗaya saboda shugaban gidan kakanninsu.
And thou shalt write Aaron’s name upon the rod of Levi; for there shall be one rod for each head of their fathers’ houses.
4 Ka ajiye su a Tentin Sujada, a gaba akwatin Alkawari, inda zan sadu da kai.
And thou shalt lay them up in the tent of meeting before the testimony, where I meet with you.
5 Sandan mutumin da na zaɓa zai yi toho, da haka zan raba kaina da gunagunin da Isra’ilawa suke yi.”
And it shall come to pass, that the rod of the man whom I shall choose shall bud: and I will make to cease from me the murmurings of the children of Israel, which they murmur against you.
6 Saboda haka Musa ya yi magana da Isra’ilawa, sai shugabanninsu suka ba shi sanduna goma sha biyu, sanda ɗaya don shugaba, bisa ga gidajen kakanninsu, sandan Haruna kuma yana a cikinsu.
And Moses spake unto the children of Israel; and all their princes gave him rods, for each prince one, according to their fathers’ houses, even twelve rods: and the rod of Aaron was among their rods.
7 Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada.
And Moses laid up the rods before Jehovah in the tent of the testimony.
8 Kashegari da Musa ya shiga cikin Tentin Sujada sai ga sandan Haruna na gidan Lawiyawa ya yi toho, ya yi furanni, ya kuma yi’ya’yan almon.
And it came to pass on the morrow, that Moses went into the tent of the testimony; and, behold, the rod of Aaron for the house of Levi was budded, and put forth buds, and produced blossoms, and bare ripe almonds.
9 Sai Musa ya fitar wa dukan Isra’ilawa dukan sandunan da suke daga gaban Ubangiji. Suka duba, kowa kuma ya ɗauki sandansa.
And Moses brought out all the rods from before Jehovah unto all the children of Israel: and they looked, and took every man his rod.
10 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka mayar da sandan Haruna a akwatin Alkawari, don a ajiye shi alama ga masu tawaye. Wannan zai kawo ƙarshen gunaguninsu a kaina, domin kada su mutu.”
And Jehovah said unto Moses, Put back the rod of Aaron before the testimony, to be kept for a token against the children of rebellion; that thou mayest make an end of their murmurings against me, that they die not.
11 Musa kuwa ya aikata kamar dai yadda Ubangiji ya umarce shi.
Thus did Moses: as Jehovah commanded him, so did he.
12 Sai Isra’ilawa suka ce wa Musa, “To, ai in haka ne, mun ƙare ke nan!
And the children of Israel spake unto Moses, saying, Behold, we perish, we are undone, we are all undone.
13 Idan an ce duk wanda ya zo kusa da tabanakul na Ubangiji zai mutu, ai rayuwarmu kamar mun mutu ke nan.”
Every one that cometh near, that cometh near unto the tabernacle of Jehovah, dieth: shall we perish all of us?