< Ƙidaya 16 >
1 Kora ɗan Izhar, wanda yake Balawe ne daga dangin Kohatawa, wata rana ya nemi Datan da Abiram’ya’yan Eliyab, da On ɗan Felet dukansu daga kabilar Ruben, suka haɗa kai
Or Coré, fils de Jitshar, fils de Kéhath, fils de Lévi, fit une entreprise, avec Dathan et Abiram enfants d'Eliab, et On, fils de Péleth, enfants de Ruben;
2 suka tayar wa Musa. Sai suka nemi goyon bayan sanannun shugabannin Isra’ilawa da aka naɗa a majalisa su guda 250,
Et ils s'élevèrent contre Moïse, avec deux cent cinquante hommes des enfants d'Israël, qui étaient des principaux de l'assemblée, lesquels on appelait pour tenir le conseil, et qui étaient des gens de réputation.
3 tare kuwa suka zo wurin Musa da Haruna, suka ce musu, “Kun wuce gona da iri! Dukan jama’an nan masu tsarki ne, kowannensu, Ubangiji kuma yana tare da su. Me ya sa kuke ɗaukan kanku fiye da taron jama’ar Ubangiji?”
Et ils s'assemblèrent contre Moïse et contre Aaron, et leur dirent: Qu'il vous suffise, puisque tous ceux de l'assemblée sont saints, et que l'Eternel est au milieu d'eux, pourquoi vous élevez-vous par dessus l'assemblée de l'Eternel?
4 Da Musa ya ji haka, sai ya fāɗi rubda ciki ya yi addu’a
Ce que Moïse ayant entendu, il se prosterna le visage [contre terre].
5 Sai ya ce wa Kora da dukan waɗannan da suke tare shi, “Da safe, Ubangiji zai nuna wane ne yake nasa, da kuma wane ne yake da tsarki. Zai kuma sa mutumin yă zo kusa da shi. Mutumin da ya zaɓa kuwa zai sa yă zo kusa da shi.
Et il parla à Coré et à tous ceux qui étaient assemblés avec lui, [et] leur dit: [Demain] au matin l'Eternel donnera à connaître celui qui lui appartient, et celui qui est le saint, et il le fera approcher de lui; il fera, dis-je, approcher de lui celui qu'il aura choisi.
6 Kai Kora da ƙungiyarka, gobe, za ku ɗauki farantai,
Faites ceci, prenez-vous des encensoirs; que Coré, [dis-je], et tous ceux qui sont assemblés avec lui, [prennent des encensoirs].
7 ku zuba wuta a ciki, ku kuma zuba musu turaren wuta a gaban Ubangiji. Sa’an nan wanda Ubangiji ya zaɓa a tsakaninmu sh ne mai tsarki. Ku Lawiyawa ku ne kuka wuce gona da iri!”
Et demain mettez-y du feu, et mettez-y du parfum devant l'Eternel; et l'homme que l'Eternel aura choisi sera le saint. Enfants de Lévi; qu'il vous suffise.
8 Musa ya kuma ce wa Kora, “Yanzu ku saurara, ku Lawiyawa!
Moïse dit aussi à Coré: Ecoutez maintenant, enfants de Lévi.
9 Ashe, bai ishe ku ba, cewa Allah na Isra’ila, ya keɓe ku daga sauran jama’ar Isra’ilawa, ya kuma kawo ku kusa da shi don ku yi aiki a tabanakul na Ubangiji, ku kuma tsaya a gaba jama’a don ku yi musu aiki?
Est-ce trop peu de chose pour vous que le Dieu d'Israël vous ait séparés de l'assemblée d'Israël, en vous faisant approcher de lui pour être employés au service du pavillon de l'Eternel, et pour assister devant l'assemblée afin de la servir?
10 Ya kawo ku da kuma dukan’yan’uwanku Lawiyawa kusa da shi, amma yanzu kuna ƙoƙari ku karɓi aikin firist.
Et qu'il t'ait fait approcher, [toi] et tous tes frères, les enfants de Lévi, avec toi, que vous recherchiez encore la Sacrificature?
11 Kai da ƙungiyarka kun haɗa kai kuna yi wa Haruna gunaguni, amma wane ne Haruna? A zahiri tawaye ne kuke wa Ubangiji.”
C'est pourquoi toi, et tous ceux qui sont assemblés avec toi, vous vous [êtes] assemblés contre l'Eternel; car qui est Aaron que vous murmuriez contre lui?
12 Sai Musa ya aika a kira Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab maza, amma suka ce, “Ba za mu zo ba!
Et Moïse envoya appeler Dathan et Abiram, enfants d'Eliab, qui répondirent: Nous n'y monterons point.
13 Bai isa ba ne da ka fitar da mu daga ƙasar mai zub da madara da zuma, ka kawo mu nan hamada don ka kashe mu? Yanzu kuma so kake ka mai da kanka sarki a bisanmu?
Est-ce peu de chose que tu nous aies fait monter hors d'un pays découlant de lait et de miel, pour nous faire mourir dans ce désert, que même tu veuilles dominer sur nous?
14 Ban da haka ma, ai, ba ka riga ka kai mu ƙasar mai zub da madara da zuma ba, ba ka ba mu gādon filaye da gonakin annabi ba, yanzu kuma kana so ka ruɗe mu. Mun ƙi, ba za mun zo ba!”
Nous as-tu fait venir en un pays découlant de lait et de miel; et nous as-tu donné quelque héritage de champs ou de vignes? crèveras-tu les yeux de ces gens-ici? nous n'y monterons point.
15 Sai Musa ya husata ƙwarai, ya ce wa Ubangiji, “Kada ka karɓi hadayarsu. Ban ƙwace wani jakinsu ba, ban kuwa cuce waninsu ba.”
Alors Moïse fut fort irrité, et dit à l'Eternel: Ne regarde point à leur offrande; je n'ai point pris d'eux un seul âne, et je n'ai point fait de mal à aucun d'eux.
16 Musa ya ce wa Kora, “Da kai da kuma dukan ƙungiyarka za ku bayyana a gaban Ubangiji gobe, kai da su. Haruna ma zai kasance a can.
Puis Moïse dit à Coré: Toi et tous ceux qui sont assemblés avec toi, trouvez-vous demain devant l'Eternel, toi, [dis-je], et ceux-ci; et Aaron aussi.
17 Kowannenku zai ɗauki faranti yă zuba turare a ciki. Wato, farantai 250 ke nan, a kuma miƙa su a gaban Ubangiji. Kai da Haruna za ku miƙa farantanku, ku ma.”
Et prenez chacun vos encensoirs, et mettez-y du parfum; et que chacun présente devant l'Eternel son encensoir, qui seront deux cent cinquante encensoirs; et toi et Aaron aussi, chacun avec son encensoir.
18 Sai kowane mutum ya ɗauki farantinsa, ya sa wuta da kuma turare a ciki, suka tsaya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada.
Ils prirent donc chacun son encensoir, et y mirent du feu, et ensuite du parfum, et ils se tinrent à l'entrée du Tabernacle d'assignation, et Moïse et Aaron s'y tinrent aussi.
19 Sa’ad da Kora ya tara mabiyansa don su yi hamayya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan taron.
Et Coré fit assembler contr'eux toute l'assemblée à l'entrée du Tabernacle d'assignation; et la gloire de l'Eternel apparut à toute l'assemblée.
20 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
Puis l'Eternel parla à Moïse et à Aaron, en disant:
21 “Ku ware kanku daga taron nan don in gama da su nan take.”
Séparez-vous du milieu de cette assemblée, et je les consumerai en un moment.
22 Amma Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki suka tā da murya suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin dukan’yan adam, za ka husata da dukan taron ne, bayan mutum ɗaya ne ya yi zunubi?”
Mais ils se prosternèrent le visage [contre terre], et dirent: Ô [Dieu] Fort? Dieu des esprits de toute chair? un seul homme aura péché, et te mettras-tu en colère contre toute l'assemblée?
23 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Et l'Eternel parla à Moïse, en disant:
24 “Faɗa wa taron cewa, ‘Ku nisanci tentin Kora, da na Datan, da na Abiram.’”
Parle à l'assemblée, et lui dis: retirez-vous d'auprès des pavillons de Coré, de Dathan, et d'Abiram.
25 Musa ya tashi ya tafi wurin Datan da Abiram, dattawan Isra’ilawa kuwa suka bi shi.
Moïse donc se leva et s'en alla vers Dathan et Abiram; et les Anciens d'Israël le suivirent.
26 Ya gargaɗe taron ya ce, “Ku ƙaurace wa tentin waɗannan mugayen mutane! Kada ku taɓa kome da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.”
Et il parla à l'assemblée, en disant: Retirez-vous, je vous prie, d'auprès des tentes de ces méchants hommes, et ne touchez à rien qui leur appartienne, de peur que vous ne soyez consumés pour tous leurs péchés.
27 Sai suka tashi daga inda tentin Kora, da Datan, da Abiram suke. Datan da Abiram kuwa suka fita suna tsaye tare da matansu da’ya’yansu da’yan ƙananansu a ƙofar tentinsu.
Ils se retirèrent donc d'auprès des pavillons de Coré, de Dathan et d'Abiram. Et Dathan et Abiram sortirent; et se tinrent debout à l'entrée de leurs tentes, avec leurs femmes, leurs enfants, et leurs familles.
28 Sai Musa ya ce musu, “Da haka za ku san cewa Ubangiji ne ya aiko ni, in yi dukan waɗannan abubuwa, ba da nufin kaina na yi su ba.
Et Moïse dit: Vous connaîtrez à ceci que l'Eternel m'a envoyé pour faire toutes ces choses-là, et que je n'ai rien fait de moi-même.
29 In waɗannan mutane sun mutu kamar yadda mutane suke mutuwa, in abin da yakan sami kowa shi ne ya same su, to, ba Ubangiji ne ya aiko ni ba.
Si ceux-là meurent comme tous les hommes meurent, et s'ils sont punis de la punition de tous les hommes, l'Eternel ne m'a point envoyé.
30 Amma in Ubangiji ya kawo wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara cikin kabari a raye, ta haka za ku sani mutanen nan sun rena Ubangiji.” (Sheol )
Mais si l'Eternel crée un cas tout nouveau, et que la terre ouvre sa bouche, et les engloutisse avec tout ce qui leur appartient, et qu'ils descendent tout vifs dans le gouffre; alors vous saurez que ces hommes-là ont irrité par mépris l'Eternel. (Sheol )
31 Nan da nan da ya gama faɗi wannan, sai ƙasa ta tsage inda Datan da Abiram suke tsaye,
Et il arriva qu'aussitôt qu'il eut achevé de dire toutes ces paroles, la terre qui était sous eux, se fendit.
32 ta kuma buɗe bakinta, ta haɗiye su tare da mutanen gidansu da dukan mutanen Kora da dukan abin da yake mallakarsu.
Et la terre ouvrit sa bouche, et les engloutit, avec leurs tentes, et tous les hommes qui étaient à Coré, et tout leur bien.
33 Suka gangara cikin kabari da rai, tare dukan mallakarsu; ƙasa ta rufe su, suka hallaka, suka rabu da jama’ar. (Sheol )
Ils descendirent donc tout vifs dans le gouffre, eux, et tous ceux qui étaient à eux; et la terre les couvrit, et ils périrent au milieu de l'assemblée. (Sheol )
34 Da jin kukansu, dukan Isra’ilawa da suke kewaye da su suka gudu, suna ihu, “Ƙasa za tă haɗiye mu, mu ma!”
Et tout Israël qui était autour d'eux, s'enfuit à leur cri; car ils disaient: [Prenons garde] que la terre ne nous engloutisse.
35 Sai wuta ta fito daga wurin Ubangiji ta cinye mutane 250 da suke miƙa hadaya da turare.
Et le feu sortit de part de l'Eternel, et consuma les deux cent cinquante hommes qui offraient le parfum.
36 Ubangiji ya ce wa Musa,
Puis l'Eternel parla à Moïse, en disant:
37 “Ka gaya wa Eleyazar ɗan Haruna, firist, yă kawar da farantan ƙona turare daga wurin da wutar ta cinye, yă watsar da gawayin a wani wuri, gama farantan tsarkakakku ne,
Dis à Eléazar fils d'Aaron, Sacrificateur, qu'il relève les encensoirs du milieu de l'incendie, et qu'on en épande le feu au loin, car ils sont sanctifiés;
38 gama an yi amfani da farantan don miƙa mini turare. Sai ka ɗauki farantan mutanen da suka yi zunubin da ya jawo musu mutuwa ka ƙera farantan, ka yi murfin bagade da su, gama an miƙa su a gaban Ubangiji, suka zama tsarkakakku. Bari su zama alama ga Isra’ilawa.”
[Savoir] les encensoirs de ceux qui ont péché sur leurs âmes, et qu'on en fasse des plaques larges pour couvrir l'autel; puisqu'ils les ont offerts devant l'Eternel ils seront sanctifiés, et ils seront pour signe aux enfants d'Israël.
39 Haka Eleyazar, firist, ya tattara farantan tagulla waɗanda mutanen da aka hallaka suka kawo, ya ƙera murfin bagade da su,
Ainsi Eléazar Sacrificateur prit les encensoirs d'airain, que ces hommes qui furent brûlés avaient présentés, et on en fit des plaques pour couvrir l'autel.
40 yadda Ubangiji ya umarce shi, ta wurin Musa. Wannan ya zama abin tuni ga Isra’ilawa domin kada wani da ba firist ba, bai kuwa fito a cikin zuriyar Haruna ba, yă zo don yă ƙona turare a gaban Ubangiji, domin kada yă zama kamar Kora da mabiyansa.
C'est un mémorial pour les enfants d'Israël, afin qu'aucun étranger qui n'est pas de la race d'Aaron, ne s'approche point pour faire le parfum en la présence de l'Eternel, et qu'il ne soit comme Coré, et comme ceux qui ont été assemblés avec lui; ainsi que l'Eternel en a parlé par le moyen de Moïse.
41 Kashegari dukan taron Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna suka ce, “Kun kashe mutanen Ubangiji.”
Or dès le lendemain toute l'assemblée des enfants d'Israël murmura contre Moïse et contre Aaron, en disant: Vous avez fait mourir le peuple de l'Eternel.
42 Bayan haka, sai dukan jama’a suka taru domin su nuna rashin yardansu da abin da suke zato Musa da Haruna ne suka aikata. Da suka fuskanci Tentin Sujada, nan take sai girgije ya rufe shi, ɗaukaka Ubangiji kuwa ta bayyana.
Et il arriva comme l'assemblée s'amassait contre Moïse et contre Aaron, qu'ils regardèrent vers le Tabernacle d'assignation, et voici la nuée le couvrit, et la gloire de l'Eternel apparut.
43 Sai Musa da Haruna suka je gaban Tentin Sujada,
Moïse donc et Aaron vinrent devant le Tabernacle d'assignation.
44 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
Et l'Eternel parla à Moïse, en disant:
45 “Ku nisanci wannan taro, gama yanzu nan zan hallaka su.” Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki.
Otez-vous du milieu de cette assemblée, et je les consumerai en un moment. Alors ils se prosternèrent le visage contre terre.
46 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki farantinka ka sa turare a ciki, da wuta daga bagade, ka yi maza ka tafi wajen taron, ka yi kafara dominsu. Gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko; an kuma fara annoba.”
Puis Moïse dit à Aaron: Prends l'encensoir, et mets-y du feu de dessus l'autel, mets-y aussi du parfum, et va promptement à l'assemblée, et fais propitiation pour eux; car une grande colère est partie de devant l'Eternel; la plaie est commencée.
47 Saboda haka Haruna ya yi kamar yadda Musa ya faɗa, ya ruga a guje zuwa tsakiyar taron. An riga an fara annobar a cikin mutane, amma Haruna ya miƙa turaren ya kuma yi kafara dominsu.
Et Aaron prit l'encensoir, comme Moïse lui avait dit, et il courut au milieu de l'assemblée, et voici la plaie avait déjà commencé sur le peuple. Alors il mit du parfum, et fit propitiation pour le peuple.
48 Ya tsaya tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.
Et comme il se tenait entre les morts elles vivants, la plaie fut arrêtée.
49 Amma mutane 14,700 ne suka mutu a annobar, ban da waɗanda suka mutu a sanadin Kora.
Et il y en eut quatorze mille sept cents qui moururent de cette plaie, outre ceux qui étaient morts pour le fait de Coré.
50 Sai Haruna ya komo wurin Musa a ƙofar Tentin Sujada, gama annobar ta ƙare.
Et Aaron retourna vers Moïse à l'entrée du Tabernacle d'assignation, après que la plaie fut arrêtée.