< Ƙidaya 16 >

1 Kora ɗan Izhar, wanda yake Balawe ne daga dangin Kohatawa, wata rana ya nemi Datan da Abiram’ya’yan Eliyab, da On ɗan Felet dukansu daga kabilar Ruben, suka haɗa kai
Now Korach, the son of Yizhar, the son of Kehath, the son of Levi, was presumptuous, together with Dathan and Abiram, the sons of Eliab, and On, the son of Peleth, sons of Reuben:
2 suka tayar wa Musa. Sai suka nemi goyon bayan sanannun shugabannin Isra’ilawa da aka naɗa a majalisa su guda 250,
So that they rose up before Moses, with certain men of the children of Israel, in number two hundred and fifty; [who were] princes of the congregation, called to the assembly, men of renown.
3 tare kuwa suka zo wurin Musa da Haruna, suka ce musu, “Kun wuce gona da iri! Dukan jama’an nan masu tsarki ne, kowannensu, Ubangiji kuma yana tare da su. Me ya sa kuke ɗaukan kanku fiye da taron jama’ar Ubangiji?”
And they assembled themselves against Moses, and against Aaron, and said unto them, Ye assume too much; for the whole of the congregation are all of them holy, and the Lord is among them; wherefore then will you lift yourselves up above the congregation of the Lord?
4 Da Musa ya ji haka, sai ya fāɗi rubda ciki ya yi addu’a
And when Moses heard it, he fell upon his face:
5 Sai ya ce wa Kora da dukan waɗannan da suke tare shi, “Da safe, Ubangiji zai nuna wane ne yake nasa, da kuma wane ne yake da tsarki. Zai kuma sa mutumin yă zo kusa da shi. Mutumin da ya zaɓa kuwa zai sa yă zo kusa da shi.
And he spoke unto Korach and unto all his company, saying, Tomorrow, —then will the Lord make known who is his, and who is holy, that he may cause them to come near unto him; and him whom he shall choose will he cause to come near unto him.
6 Kai Kora da ƙungiyarka, gobe, za ku ɗauki farantai,
This do ye: Take yourselves censers, Korach and all his company;
7 ku zuba wuta a ciki, ku kuma zuba musu turaren wuta a gaban Ubangiji. Sa’an nan wanda Ubangiji ya zaɓa a tsakaninmu sh ne mai tsarki. Ku Lawiyawa ku ne kuka wuce gona da iri!”
And put therein fire, and put upon them incense before the Lord, tomorrow; and it shall be that the man whom the Lord will choose, he shall be the holy one; you assume too much, ye sons of Levi.
8 Musa ya kuma ce wa Kora, “Yanzu ku saurara, ku Lawiyawa!
And Moses said unto Korach, Hear, I pray you, ye sons of Levi:
9 Ashe, bai ishe ku ba, cewa Allah na Isra’ila, ya keɓe ku daga sauran jama’ar Isra’ilawa, ya kuma kawo ku kusa da shi don ku yi aiki a tabanakul na Ubangiji, ku kuma tsaya a gaba jama’a don ku yi musu aiki?
It is too little for you, that the God of Israel hath separated you from the congregation of Israel, to bring you near unto himself, to do the service of the tabernacle of the Lord, and to stand before the congregation to minister for them?
10 Ya kawo ku da kuma dukan’yan’uwanku Lawiyawa kusa da shi, amma yanzu kuna ƙoƙari ku karɓi aikin firist.
And he hath brought thee near, and all thy brethren the sons of Levi with thee: and now will ye seek the priesthood also?
11 Kai da ƙungiyarka kun haɗa kai kuna yi wa Haruna gunaguni, amma wane ne Haruna? A zahiri tawaye ne kuke wa Ubangiji.”
For which cause [beware], thou and all thy company that are gathered together against the Lord; for Aaron, what is he, that ye should murmur against him:
12 Sai Musa ya aika a kira Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab maza, amma suka ce, “Ba za mu zo ba!
And Moses sent to call Dathan and Abiram, the sons of Eliab; but they said, We will not come up:
13 Bai isa ba ne da ka fitar da mu daga ƙasar mai zub da madara da zuma, ka kawo mu nan hamada don ka kashe mu? Yanzu kuma so kake ka mai da kanka sarki a bisanmu?
Is it too little that thou hast brought us up out of a land flowing with milk and honey, to kill us in the wilderness, that thou wilt assume to make thyself also a prince over us?
14 Ban da haka ma, ai, ba ka riga ka kai mu ƙasar mai zub da madara da zuma ba, ba ka ba mu gādon filaye da gonakin annabi ba, yanzu kuma kana so ka ruɗe mu. Mun ƙi, ba za mun zo ba!”
Moreover thou hast not brought us into a land flowing with milk and honey, and thou hast not given us inheritance of fields and vineyards: wilt thou bore out the eyes of these men? we will not come up.
15 Sai Musa ya husata ƙwarai, ya ce wa Ubangiji, “Kada ka karɓi hadayarsu. Ban ƙwace wani jakinsu ba, ban kuwa cuce waninsu ba.”
And this displeased Moses greatly, and he said unto the Lord, Have no respect unto their offering: I have not taken away an ass of any one of them, nor have I done wrong to any one of them.
16 Musa ya ce wa Kora, “Da kai da kuma dukan ƙungiyarka za ku bayyana a gaban Ubangiji gobe, kai da su. Haruna ma zai kasance a can.
And Moses said unto Korach, Thou and all thy company, be ye before the Lord, thou, and they, and Aaron, tomorrow:
17 Kowannenku zai ɗauki faranti yă zuba turare a ciki. Wato, farantai 250 ke nan, a kuma miƙa su a gaban Ubangiji. Kai da Haruna za ku miƙa farantanku, ku ma.”
And take ye every man his censer, and put incense upon them, and bring ye near before the Lord every man his censer, two hundred and fifty censers; thou also, and Aaron, each his censer.
18 Sai kowane mutum ya ɗauki farantinsa, ya sa wuta da kuma turare a ciki, suka tsaya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada.
And they took every man his censer, and put fire on them, and laid incense thereupon; and they stood at the door of the tabernacle of the congregation with Moses and Aaron.—
19 Sa’ad da Kora ya tara mabiyansa don su yi hamayya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan taron.
And Korach assembled against them all the congregation unto the door of the tabernacle of the congregation; and the glory of the Lord then appeared unto all the congregation.
20 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And the Lord spoke unto Moses and unto Aaron, saying,
21 “Ku ware kanku daga taron nan don in gama da su nan take.”
Separate yourselves from the midst of this congregation, and I will make an end of them in a moment.
22 Amma Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki suka tā da murya suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin dukan’yan adam, za ka husata da dukan taron ne, bayan mutum ɗaya ne ya yi zunubi?”
And they fell upon their faces, and said, O God, the God of the spirits of all flesh, this one man doth sin, and with all the congregation wouldst thou be wroth!
23 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke unto Moses, saying,
24 “Faɗa wa taron cewa, ‘Ku nisanci tentin Kora, da na Datan, da na Abiram.’”
Speak unto the congregation, saying, Get you away from about the dwelling of Korach, Dathan, and Abiram.
25 Musa ya tashi ya tafi wurin Datan da Abiram, dattawan Isra’ilawa kuwa suka bi shi.
And Moses rose up and went unto Dathan and Abiram; and there went after him the elders of Israel.
26 Ya gargaɗe taron ya ce, “Ku ƙaurace wa tentin waɗannan mugayen mutane! Kada ku taɓa kome da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.”
And he spoke unto the congregation, saying, Depart, I pray you, from the tents of these wicked men, and touch nothing which belongeth to them, lest ye be destroyed through all their sins.
27 Sai suka tashi daga inda tentin Kora, da Datan, da Abiram suke. Datan da Abiram kuwa suka fita suna tsaye tare da matansu da’ya’yansu da’yan ƙananansu a ƙofar tentinsu.
So they got away from the dwelling of Korach, Dathan, and Abiram, on every side: and Dathan and Abiram came out, standing [boldly] at the door of their tents, with their wives, and their sons, and their little ones.
28 Sai Musa ya ce musu, “Da haka za ku san cewa Ubangiji ne ya aiko ni, in yi dukan waɗannan abubuwa, ba da nufin kaina na yi su ba.
And Moses said, Through this shall ye know that the Lord hath sent me to do all these deeds; that [I have] not done them out of my own heart.
29 In waɗannan mutane sun mutu kamar yadda mutane suke mutuwa, in abin da yakan sami kowa shi ne ya same su, to, ba Ubangiji ne ya aiko ni ba.
If these men die as all men die, and if the visitation of all men be visited on them: then hath the Lord not sent me.
30 Amma in Ubangiji ya kawo wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara cikin kabari a raye, ta haka za ku sani mutanen nan sun rena Ubangiji.” (Sheol h7585)
But if the Lord do create a new thing, and the earth open her mouth, and swallow them up, with all that appertaineth unto them, and they go down alive into the pit: then shall ye understand that these men have provoked the Lord. (Sheol h7585)
31 Nan da nan da ya gama faɗi wannan, sai ƙasa ta tsage inda Datan da Abiram suke tsaye,
And it came to pass, when he had made an end of speaking all these words, that the ground that was under them was cloven asunder:
32 ta kuma buɗe bakinta, ta haɗiye su tare da mutanen gidansu da dukan mutanen Kora da dukan abin da yake mallakarsu.
And the earth opened her mouth, and swallowed them up, and their houses, and all the men that appertained unto Korach, and all their goods.
33 Suka gangara cikin kabari da rai, tare dukan mallakarsu; ƙasa ta rufe su, suka hallaka, suka rabu da jama’ar. (Sheol h7585)
And they went down, they, and all they that appertained to them, alive into the pit; and the earth closed over them, and they disappeared from the midst of the congregation. (Sheol h7585)
34 Da jin kukansu, dukan Isra’ilawa da suke kewaye da su suka gudu, suna ihu, “Ƙasa za tă haɗiye mu, mu ma!”
And all Israel that were round about them fled at their cry; for they said, Perhaps the earth may swallow us up [also].
35 Sai wuta ta fito daga wurin Ubangiji ta cinye mutane 250 da suke miƙa hadaya da turare.
And there came out a fire from the Lord, and consumed the two hundred and fifty men that had offered the incense.
36 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke unto Moses, saying,
37 “Ka gaya wa Eleyazar ɗan Haruna, firist, yă kawar da farantan ƙona turare daga wurin da wutar ta cinye, yă watsar da gawayin a wani wuri, gama farantan tsarkakakku ne,
Speak unto Elazar the son of Aaron the priest, that he lift up the censers out of the burning, and throw out the fire far away; for they have been hallowed:
38 gama an yi amfani da farantan don miƙa mini turare. Sai ka ɗauki farantan mutanen da suka yi zunubin da ya jawo musu mutuwa ka ƙera farantan, ka yi murfin bagade da su, gama an miƙa su a gaban Ubangiji, suka zama tsarkakakku. Bari su zama alama ga Isra’ilawa.”
The censers of these sinners against their own lives; and they shall make of them broad plates for a covering for the altar; for they brought them near before the Lord, and they have thus become hallowed; and they shall serve for a sign unto the children of Israel.
39 Haka Eleyazar, firist, ya tattara farantan tagulla waɗanda mutanen da aka hallaka suka kawo, ya ƙera murfin bagade da su,
And Elazar the priest took the copper censers, which they that were burnt had brought near; and they beat them out for a covering unto the altar:
40 yadda Ubangiji ya umarce shi, ta wurin Musa. Wannan ya zama abin tuni ga Isra’ilawa domin kada wani da ba firist ba, bai kuwa fito a cikin zuriyar Haruna ba, yă zo don yă ƙona turare a gaban Ubangiji, domin kada yă zama kamar Kora da mabiyansa.
As a memorial unto the children of Israel, in order that no stranger, who is not of the seed of Aaron, should come near to burn incense before the Lord; that he become not as Korach, and as his company; as the Lord had spoken to him by the hand of Moses.
41 Kashegari dukan taron Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna suka ce, “Kun kashe mutanen Ubangiji.”
And all the congregation of the children of Israel murmured against Moses and Aaron, on the morrow, saying, It is you who have caused the people of the Lord to die.
42 Bayan haka, sai dukan jama’a suka taru domin su nuna rashin yardansu da abin da suke zato Musa da Haruna ne suka aikata. Da suka fuskanci Tentin Sujada, nan take sai girgije ya rufe shi, ɗaukaka Ubangiji kuwa ta bayyana.
And it came to pass, when the congregation assembled against Moses and against Aaron, that they looked toward the tabernacle of the congregation, and, behold, the cloud covered it; and the glory of the Lord appeared.
43 Sai Musa da Haruna suka je gaban Tentin Sujada,
And Moses came with Aaron before the tabernacle of the congregation.
44 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
And the Lord spoke unto Moses, saying,
45 “Ku nisanci wannan taro, gama yanzu nan zan hallaka su.” Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki.
Remove yourselves from the midst of this congregation, that I may consume them in a moment. And they fell upon their faces.
46 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki farantinka ka sa turare a ciki, da wuta daga bagade, ka yi maza ka tafi wajen taron, ka yi kafara dominsu. Gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko; an kuma fara annoba.”
And Moses said unto Aaron, Take the censer, and put therein fire from off the altar, and put on incense, and carry [it] quickly unto the congregation, and make an atonement for them; for the wrath is gone forth from the Lord; the plague hath begun.
47 Saboda haka Haruna ya yi kamar yadda Musa ya faɗa, ya ruga a guje zuwa tsakiyar taron. An riga an fara annobar a cikin mutane, amma Haruna ya miƙa turaren ya kuma yi kafara dominsu.
And Aaron took as Moses had commanded, and he ran into the midst of the assembly; and, behold, the plague had begun among the people: and he put on the incense, and made an atonement for the people.
48 Ya tsaya tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.
And he stood between the dead and the living; and the plague was stayed.
49 Amma mutane 14,700 ne suka mutu a annobar, ban da waɗanda suka mutu a sanadin Kora.
And those who died in the plague were fourteen thousand and seven hundred, besides those that had died about the matter of Korach.
50 Sai Haruna ya komo wurin Musa a ƙofar Tentin Sujada, gama annobar ta ƙare.
And Aaron returned unto Moses, to the door of the tabernacle of the congregation, after the plague had been stayed.

< Ƙidaya 16 >