< Ƙidaya 16 >

1 Kora ɗan Izhar, wanda yake Balawe ne daga dangin Kohatawa, wata rana ya nemi Datan da Abiram’ya’yan Eliyab, da On ɗan Felet dukansu daga kabilar Ruben, suka haɗa kai
And Korah, the son of Izhar, the son of Kohath, the son of Levi, made bold, and [with him] Dathan and Abiram, the sons of Eliab, and On, the son of Peleth, the sons of Reuben;
2 suka tayar wa Musa. Sai suka nemi goyon bayan sanannun shugabannin Isra’ilawa da aka naɗa a majalisa su guda 250,
and they rose up against Moses, with two hundred and fifty men of the children of Israel, princes of the assembly, summoned to the council, men of renown;
3 tare kuwa suka zo wurin Musa da Haruna, suka ce musu, “Kun wuce gona da iri! Dukan jama’an nan masu tsarki ne, kowannensu, Ubangiji kuma yana tare da su. Me ya sa kuke ɗaukan kanku fiye da taron jama’ar Ubangiji?”
and they gathered themselves together against Moses and against Aaron, and said to them, It is enough; for all the assembly, all of them are holy, and Jehovah is among them; and why do ye lift up yourselves above the congregation of Jehovah?
4 Da Musa ya ji haka, sai ya fāɗi rubda ciki ya yi addu’a
When Moses heard this, he fell on his face.
5 Sai ya ce wa Kora da dukan waɗannan da suke tare shi, “Da safe, Ubangiji zai nuna wane ne yake nasa, da kuma wane ne yake da tsarki. Zai kuma sa mutumin yă zo kusa da shi. Mutumin da ya zaɓa kuwa zai sa yă zo kusa da shi.
And he spoke to Korah and to all his band, saying, Even to-morrow will Jehovah make known who is his, and who is holy; and he will cause him to come near to him; and him whom he has chosen, him will he cause to come near to him.
6 Kai Kora da ƙungiyarka, gobe, za ku ɗauki farantai,
This do: take you censers, Korah, and all his band,
7 ku zuba wuta a ciki, ku kuma zuba musu turaren wuta a gaban Ubangiji. Sa’an nan wanda Ubangiji ya zaɓa a tsakaninmu sh ne mai tsarki. Ku Lawiyawa ku ne kuka wuce gona da iri!”
and put fire therein, and lay incense thereon before Jehovah to-morrow; and it shall be that the man whom Jehovah doth choose, he shall be holy. It is enough, ye sons of Levi!
8 Musa ya kuma ce wa Kora, “Yanzu ku saurara, ku Lawiyawa!
And Moses said to Korah, Hear, I pray you, ye sons of Levi!
9 Ashe, bai ishe ku ba, cewa Allah na Isra’ila, ya keɓe ku daga sauran jama’ar Isra’ilawa, ya kuma kawo ku kusa da shi don ku yi aiki a tabanakul na Ubangiji, ku kuma tsaya a gaba jama’a don ku yi musu aiki?
Is it too little for you, that the God of Israel has separated you from the assembly of Israel, to bring you near to himself to do the work of the tabernacle of Jehovah, and to stand before the assembly to minister to them?
10 Ya kawo ku da kuma dukan’yan’uwanku Lawiyawa kusa da shi, amma yanzu kuna ƙoƙari ku karɓi aikin firist.
— that he has brought thee near, and all thy brethren the sons of Levi with thee; and seek ye now the priesthood also?
11 Kai da ƙungiyarka kun haɗa kai kuna yi wa Haruna gunaguni, amma wane ne Haruna? A zahiri tawaye ne kuke wa Ubangiji.”
For which cause thou and all thy band are banded together against Jehovah; and Aaron, who is he that ye murmur against him?
12 Sai Musa ya aika a kira Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab maza, amma suka ce, “Ba za mu zo ba!
And Moses sent to call Dathan and Abiram, the sons of Eliab; but they said, We will not come up!
13 Bai isa ba ne da ka fitar da mu daga ƙasar mai zub da madara da zuma, ka kawo mu nan hamada don ka kashe mu? Yanzu kuma so kake ka mai da kanka sarki a bisanmu?
Is it a small thing that thou hast brought us up out of a land flowing with milk and honey, to kill us in the wilderness, that thou must make thyself altogether a ruler over us?
14 Ban da haka ma, ai, ba ka riga ka kai mu ƙasar mai zub da madara da zuma ba, ba ka ba mu gādon filaye da gonakin annabi ba, yanzu kuma kana so ka ruɗe mu. Mun ƙi, ba za mun zo ba!”
Moreover, thou hast not brought us into a land flowing with milk and honey, or given us inheritance of fields and vineyards: wilt thou put out the eyes of these men? we will not come up!
15 Sai Musa ya husata ƙwarai, ya ce wa Ubangiji, “Kada ka karɓi hadayarsu. Ban ƙwace wani jakinsu ba, ban kuwa cuce waninsu ba.”
Then Moses was very wroth, and said to Jehovah, Have no regard to their oblation: not one ass have I taken from them, neither have I hurt one of them.
16 Musa ya ce wa Kora, “Da kai da kuma dukan ƙungiyarka za ku bayyana a gaban Ubangiji gobe, kai da su. Haruna ma zai kasance a can.
And Moses said to Korah, Be thou and all thy band before Jehovah, thou, and they, and Aaron, to-morrow.
17 Kowannenku zai ɗauki faranti yă zuba turare a ciki. Wato, farantai 250 ke nan, a kuma miƙa su a gaban Ubangiji. Kai da Haruna za ku miƙa farantanku, ku ma.”
And take each his censer, and put incense thereon, and present before Jehovah every man his censer, two hundred and fifty censers; and thou, and Aaron, each his censer.
18 Sai kowane mutum ya ɗauki farantinsa, ya sa wuta da kuma turare a ciki, suka tsaya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada.
And they took each his censer, and put fire on them, and laid incense thereon, and stood before the entrance to the tent of meeting, as well as Moses and Aaron.
19 Sa’ad da Kora ya tara mabiyansa don su yi hamayya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan taron.
And Korah gathered the whole assembly against them to the entrance of the tent of meeting. And the glory of Jehovah appeared to all the assembly.
20 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And Jehovah spoke to Moses and to Aaron, saying,
21 “Ku ware kanku daga taron nan don in gama da su nan take.”
Separate yourselves from the midst of this assembly, and I will consume them in a moment.
22 Amma Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki suka tā da murya suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin dukan’yan adam, za ka husata da dukan taron ne, bayan mutum ɗaya ne ya yi zunubi?”
And they fell on their faces, and said, O God, the God of the spirits of all flesh! shall one man sin, and wilt thou be wroth with the whole assembly?
23 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
24 “Faɗa wa taron cewa, ‘Ku nisanci tentin Kora, da na Datan, da na Abiram.’”
Speak unto the assembly, saying, Get you up from about the habitation of Korah, Dathan, and Abiram.
25 Musa ya tashi ya tafi wurin Datan da Abiram, dattawan Isra’ilawa kuwa suka bi shi.
And Moses rose up and went to Dathan and Abiram; and the elders of Israel followed him.
26 Ya gargaɗe taron ya ce, “Ku ƙaurace wa tentin waɗannan mugayen mutane! Kada ku taɓa kome da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.”
And he spoke to the assembly, saying, Depart, I pray you, from the tents of these wicked men, and touch nothing of theirs, lest ye perish in all their sins.
27 Sai suka tashi daga inda tentin Kora, da Datan, da Abiram suke. Datan da Abiram kuwa suka fita suna tsaye tare da matansu da’ya’yansu da’yan ƙananansu a ƙofar tentinsu.
And they got up from the habitation of Koran, Dathan, and Abiram, on every side. And Dathan and Abiram came out, and stood in the entrance of their tents, and their wives, and their sons, and their little ones.
28 Sai Musa ya ce musu, “Da haka za ku san cewa Ubangiji ne ya aiko ni, in yi dukan waɗannan abubuwa, ba da nufin kaina na yi su ba.
And Moses said, Hereby ye shall know that Jehovah has sent me to do all these deeds, for they are not out of my own heart:
29 In waɗannan mutane sun mutu kamar yadda mutane suke mutuwa, in abin da yakan sami kowa shi ne ya same su, to, ba Ubangiji ne ya aiko ni ba.
if these men die as all men die, and are visited with the visitation of all men, Jehovah has not sent me;
30 Amma in Ubangiji ya kawo wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara cikin kabari a raye, ta haka za ku sani mutanen nan sun rena Ubangiji.” (Sheol h7585)
but if Jehovah make a new thing, and the ground open its mouth, and swallow them up, and all that they have, and they go down alive into Sheol, then ye shall know that these men have despised Jehovah. (Sheol h7585)
31 Nan da nan da ya gama faɗi wannan, sai ƙasa ta tsage inda Datan da Abiram suke tsaye,
And it came to pass when he had ended speaking all these words, that the ground clave apart that was under them.
32 ta kuma buɗe bakinta, ta haɗiye su tare da mutanen gidansu da dukan mutanen Kora da dukan abin da yake mallakarsu.
And the earth opened its mouth, and swallowed them up, and their households, and all the men that belonged to Korah, and all their property.
33 Suka gangara cikin kabari da rai, tare dukan mallakarsu; ƙasa ta rufe su, suka hallaka, suka rabu da jama’ar. (Sheol h7585)
And they went down, they and all that they had, alive into Sheol, and the earth covered them; and they perished from among the congregation. (Sheol h7585)
34 Da jin kukansu, dukan Isra’ilawa da suke kewaye da su suka gudu, suna ihu, “Ƙasa za tă haɗiye mu, mu ma!”
And all Israel that were round about them fled at their cry; for they said, Lest the earth swallow us up!
35 Sai wuta ta fito daga wurin Ubangiji ta cinye mutane 250 da suke miƙa hadaya da turare.
And there came out a fire from Jehovah, and consumed the two hundred and fifty men that had presented incense.
36 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
37 “Ka gaya wa Eleyazar ɗan Haruna, firist, yă kawar da farantan ƙona turare daga wurin da wutar ta cinye, yă watsar da gawayin a wani wuri, gama farantan tsarkakakku ne,
Speak to Eleazar the son of Aaron the priest, that he take up the censers out of the burning; and scatter the fire afar; for they are hallowed,
38 gama an yi amfani da farantan don miƙa mini turare. Sai ka ɗauki farantan mutanen da suka yi zunubin da ya jawo musu mutuwa ka ƙera farantan, ka yi murfin bagade da su, gama an miƙa su a gaban Ubangiji, suka zama tsarkakakku. Bari su zama alama ga Isra’ilawa.”
the censers of these sinners who have forfeited their life; and they shall make them into broad plates for the covering of the altar; for they presented them before Jehovah, therefore they are hallowed; and they shall be a sign unto the children of Israel.
39 Haka Eleyazar, firist, ya tattara farantan tagulla waɗanda mutanen da aka hallaka suka kawo, ya ƙera murfin bagade da su,
And Eleazar the priest took the copper censers, which they that were burnt had presented; and they were made broad plates for a covering of the altar:
40 yadda Ubangiji ya umarce shi, ta wurin Musa. Wannan ya zama abin tuni ga Isra’ilawa domin kada wani da ba firist ba, bai kuwa fito a cikin zuriyar Haruna ba, yă zo don yă ƙona turare a gaban Ubangiji, domin kada yă zama kamar Kora da mabiyansa.
as a memorial to the children of Israel, that no stranger who is not of the seed of Aaron come near to burn incense before Jehovah, that he be not as Korah, and as his band, — as Jehovah had said to him through Moses.
41 Kashegari dukan taron Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna suka ce, “Kun kashe mutanen Ubangiji.”
And the whole assembly of the children of Israel murmured on the morrow against Moses and against Aaron, saying, Ye have killed the people of Jehovah.
42 Bayan haka, sai dukan jama’a suka taru domin su nuna rashin yardansu da abin da suke zato Musa da Haruna ne suka aikata. Da suka fuskanci Tentin Sujada, nan take sai girgije ya rufe shi, ɗaukaka Ubangiji kuwa ta bayyana.
And it came to pass, when the assembly was gathered together against Moses and against Aaron, that they looked toward the tent of meeting, and behold, the cloud covered it, and the glory of Jehovah appeared.
43 Sai Musa da Haruna suka je gaban Tentin Sujada,
And Moses and Aaron went before the tent of meeting.
44 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
45 “Ku nisanci wannan taro, gama yanzu nan zan hallaka su.” Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki.
Get you up from the midst of this assembly, and I will consume them in a moment. And they fell on their faces.
46 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki farantinka ka sa turare a ciki, da wuta daga bagade, ka yi maza ka tafi wajen taron, ka yi kafara dominsu. Gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko; an kuma fara annoba.”
And Moses said to Aaron, Take the censer, and put fire thereon from off the altar, and lay on incense, and carry it quickly to the assembly, and make atonement for them; for there is wrath gone out from Jehovah: the plague is begun.
47 Saboda haka Haruna ya yi kamar yadda Musa ya faɗa, ya ruga a guje zuwa tsakiyar taron. An riga an fara annobar a cikin mutane, amma Haruna ya miƙa turaren ya kuma yi kafara dominsu.
And Aaron took as Moses had said, and ran into the midst of the congregation; and behold, the plague had begun among the people; and he put on incense, and made atonement for the people.
48 Ya tsaya tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.
And he stood between the dead and the living; and the plague was stayed.
49 Amma mutane 14,700 ne suka mutu a annobar, ban da waɗanda suka mutu a sanadin Kora.
Now they that died in the plague were fourteen thousand seven hundred, besides them that had died because of the matter of Korah.
50 Sai Haruna ya komo wurin Musa a ƙofar Tentin Sujada, gama annobar ta ƙare.
And Aaron returned to Moses to the entrance of the tent of meeting; and the plague was stayed.

< Ƙidaya 16 >