< Ƙidaya 16 >
1 Kora ɗan Izhar, wanda yake Balawe ne daga dangin Kohatawa, wata rana ya nemi Datan da Abiram’ya’yan Eliyab, da On ɗan Felet dukansu daga kabilar Ruben, suka haɗa kai
Now Korah, the son of Izhar, the son of Kohath, the son of Levi, with Dathan and Abiram, the sons of Eliab, and On, the son of Peleth, sons of Reuben, took,
2 suka tayar wa Musa. Sai suka nemi goyon bayan sanannun shugabannin Isra’ilawa da aka naɗa a majalisa su guda 250,
and they rose up before Moses, with certain of the sons of Israel, two hundred and fifty rulers of the congregation, called to the assembly, men of renown,
3 tare kuwa suka zo wurin Musa da Haruna, suka ce musu, “Kun wuce gona da iri! Dukan jama’an nan masu tsarki ne, kowannensu, Ubangiji kuma yana tare da su. Me ya sa kuke ɗaukan kanku fiye da taron jama’ar Ubangiji?”
and they assembled themselves together against Moses and against Aaron, and said to them, Ye take too much upon you, since all the congregation are holy, every one of them, and Jehovah is among them. Why then do ye lift up yourselves above the assembly of Jehovah?
4 Da Musa ya ji haka, sai ya fāɗi rubda ciki ya yi addu’a
And when Moses heard it, he fell upon his face.
5 Sai ya ce wa Kora da dukan waɗannan da suke tare shi, “Da safe, Ubangiji zai nuna wane ne yake nasa, da kuma wane ne yake da tsarki. Zai kuma sa mutumin yă zo kusa da shi. Mutumin da ya zaɓa kuwa zai sa yă zo kusa da shi.
And he spoke to Korah and to all his company, saying, In the morning Jehovah will show who are his, and who is holy, and will cause him to come near to him, even him whom he shall choose will he cause to come near to him.
6 Kai Kora da ƙungiyarka, gobe, za ku ɗauki farantai,
This do: Take you censers, Korah, and all his company,
7 ku zuba wuta a ciki, ku kuma zuba musu turaren wuta a gaban Ubangiji. Sa’an nan wanda Ubangiji ya zaɓa a tsakaninmu sh ne mai tsarki. Ku Lawiyawa ku ne kuka wuce gona da iri!”
and put fire in them, and put incense upon them before Jehovah tomorrow. And it shall be that the man whom Jehovah chooses, he is holy. Ye take too much upon you, ye sons of Levi.
8 Musa ya kuma ce wa Kora, “Yanzu ku saurara, ku Lawiyawa!
And Moses said to Korah, Hear now, ye sons of Levi.
9 Ashe, bai ishe ku ba, cewa Allah na Isra’ila, ya keɓe ku daga sauran jama’ar Isra’ilawa, ya kuma kawo ku kusa da shi don ku yi aiki a tabanakul na Ubangiji, ku kuma tsaya a gaba jama’a don ku yi musu aiki?
Is it a small thing to you, that the God of Israel has separated you from the congregation of Israel, to bring you near to himself, to do the service of the tabernacle of Jehovah, and to stand before the congregation to minister to them,
10 Ya kawo ku da kuma dukan’yan’uwanku Lawiyawa kusa da shi, amma yanzu kuna ƙoƙari ku karɓi aikin firist.
and that he has brought thee near, and all thy brothers the sons of Levi with thee? And ye seek the priesthood also?
11 Kai da ƙungiyarka kun haɗa kai kuna yi wa Haruna gunaguni, amma wane ne Haruna? A zahiri tawaye ne kuke wa Ubangiji.”
Therefore thou and all thy company are gathered together against Jehovah. And Aaron, what is he that ye murmur against him?
12 Sai Musa ya aika a kira Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab maza, amma suka ce, “Ba za mu zo ba!
And Moses sent to call Dathan and Abiram, the sons of Eliab. And they said, We will not come up.
13 Bai isa ba ne da ka fitar da mu daga ƙasar mai zub da madara da zuma, ka kawo mu nan hamada don ka kashe mu? Yanzu kuma so kake ka mai da kanka sarki a bisanmu?
Is it a small thing that thou have brought us up out of a land flowing with milk and honey, to kill us in the wilderness, but thou must make thyself also a ruler over us?
14 Ban da haka ma, ai, ba ka riga ka kai mu ƙasar mai zub da madara da zuma ba, ba ka ba mu gādon filaye da gonakin annabi ba, yanzu kuma kana so ka ruɗe mu. Mun ƙi, ba za mun zo ba!”
Moreover thou have not brought us into a land flowing with milk and honey, nor given us inheritance of fields and vineyards. Will thou put out the eyes of these men? We will not come up.
15 Sai Musa ya husata ƙwarai, ya ce wa Ubangiji, “Kada ka karɓi hadayarsu. Ban ƙwace wani jakinsu ba, ban kuwa cuce waninsu ba.”
And Moses was very angry, and said to Jehovah, Do not respect thou their offering. I have not taken one donkey from them, neither have I hurt one of them.
16 Musa ya ce wa Kora, “Da kai da kuma dukan ƙungiyarka za ku bayyana a gaban Ubangiji gobe, kai da su. Haruna ma zai kasance a can.
And Moses said to Korah, Be thou and all thy company before Jehovah, thou, and they, and Aaron, tomorrow.
17 Kowannenku zai ɗauki faranti yă zuba turare a ciki. Wato, farantai 250 ke nan, a kuma miƙa su a gaban Ubangiji. Kai da Haruna za ku miƙa farantanku, ku ma.”
And take ye every man his censer, and put incense upon them, and bring ye before Jehovah every man his censer, two hundred and fifty censers, thou also, and Aaron, each his censer.
18 Sai kowane mutum ya ɗauki farantinsa, ya sa wuta da kuma turare a ciki, suka tsaya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada.
And they took every man his censer, and put fire in them, and laid incense on it, and stood at the door of the tent of meeting with Moses and Aaron.
19 Sa’ad da Kora ya tara mabiyansa don su yi hamayya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan taron.
And Korah assembled all the congregation against them to the door of the tent of meeting. And the glory of Jehovah appeared to all the congregation.
20 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And Jehovah spoke to Moses and to Aaron, saying,
21 “Ku ware kanku daga taron nan don in gama da su nan take.”
Separate yourselves from among this congregation, that I may consume them in a moment.
22 Amma Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki suka tā da murya suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin dukan’yan adam, za ka husata da dukan taron ne, bayan mutum ɗaya ne ya yi zunubi?”
And they fell upon their faces, and said, O God, the God of the spirits of all flesh, shall one man sin, and will thou be angry with all the congregation?
23 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
24 “Faɗa wa taron cewa, ‘Ku nisanci tentin Kora, da na Datan, da na Abiram.’”
Speak to the congregation, saying, Get you up from about the tabernacle of Korah, Dathan, and Abiram.
25 Musa ya tashi ya tafi wurin Datan da Abiram, dattawan Isra’ilawa kuwa suka bi shi.
And Moses rose up and went to Dathan and Abiram, and the elders of Israel followed him.
26 Ya gargaɗe taron ya ce, “Ku ƙaurace wa tentin waɗannan mugayen mutane! Kada ku taɓa kome da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.”
And he spoke to the congregation, saying, Depart, I pray you, from the tents of these wicked men, and touch nothing of theirs, lest ye be consumed in all their sins.
27 Sai suka tashi daga inda tentin Kora, da Datan, da Abiram suke. Datan da Abiram kuwa suka fita suna tsaye tare da matansu da’ya’yansu da’yan ƙananansu a ƙofar tentinsu.
So they got up from the tabernacle of Korah, Dathan, and Abiram, on every side. And Dathan and Abiram came out, and stood at the door of their tents, and their wives, and their sons, and their little ones.
28 Sai Musa ya ce musu, “Da haka za ku san cewa Ubangiji ne ya aiko ni, in yi dukan waɗannan abubuwa, ba da nufin kaina na yi su ba.
And Moses said, Hereby ye shall know that Jehovah has sent me to do all these works, for it is not of my own mind.
29 In waɗannan mutane sun mutu kamar yadda mutane suke mutuwa, in abin da yakan sami kowa shi ne ya same su, to, ba Ubangiji ne ya aiko ni ba.
If these men die the common death of all men, or if they be visited after the visitation of all men, then Jehovah has not sent me.
30 Amma in Ubangiji ya kawo wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara cikin kabari a raye, ta haka za ku sani mutanen nan sun rena Ubangiji.” (Sheol )
But if Jehovah makes a new thing, and the ground opens its mouth, and swallows them up, with all that pertains to them, and they go down alive into Sheol, then ye shall understand that these men have despised Jehovah. (Sheol )
31 Nan da nan da ya gama faɗi wannan, sai ƙasa ta tsage inda Datan da Abiram suke tsaye,
And it came to pass, as he made an end of speaking all these words, that the ground split asunder that was under them,
32 ta kuma buɗe bakinta, ta haɗiye su tare da mutanen gidansu da dukan mutanen Kora da dukan abin da yake mallakarsu.
and the earth opened its mouth, and swallowed them up, and their households, and all the men that pertained to Korah, and all their goods.
33 Suka gangara cikin kabari da rai, tare dukan mallakarsu; ƙasa ta rufe su, suka hallaka, suka rabu da jama’ar. (Sheol )
So they, and all that pertained to them, went down alive into Sheol. And the earth closed upon them, and they perished from among the assembly. (Sheol )
34 Da jin kukansu, dukan Isra’ilawa da suke kewaye da su suka gudu, suna ihu, “Ƙasa za tă haɗiye mu, mu ma!”
And all Israel that were round about them fled at the cry of them, for they said, Lest the earth swallow us up.
35 Sai wuta ta fito daga wurin Ubangiji ta cinye mutane 250 da suke miƙa hadaya da turare.
And fire came forth from Jehovah, and devoured the two hundred and fifty men who offered the incense.
36 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
37 “Ka gaya wa Eleyazar ɗan Haruna, firist, yă kawar da farantan ƙona turare daga wurin da wutar ta cinye, yă watsar da gawayin a wani wuri, gama farantan tsarkakakku ne,
Speak to Eleazar the son of Aaron the priest, that he take up the censers out of the burning, and scatter thou the fire yonder, for they are holy,
38 gama an yi amfani da farantan don miƙa mini turare. Sai ka ɗauki farantan mutanen da suka yi zunubin da ya jawo musu mutuwa ka ƙera farantan, ka yi murfin bagade da su, gama an miƙa su a gaban Ubangiji, suka zama tsarkakakku. Bari su zama alama ga Isra’ilawa.”
even the censers of these sinners against their own lives, and let them be made beaten plates for a covering of the altar, for they offered them before Jehovah, therefore they are holy, and they shall be a sign to the sons of Israel.
39 Haka Eleyazar, firist, ya tattara farantan tagulla waɗanda mutanen da aka hallaka suka kawo, ya ƙera murfin bagade da su,
And Eleazar the priest took the brazen censers, which those who were burnt had offered, and they beat them out for a covering of the altar,
40 yadda Ubangiji ya umarce shi, ta wurin Musa. Wannan ya zama abin tuni ga Isra’ilawa domin kada wani da ba firist ba, bai kuwa fito a cikin zuriyar Haruna ba, yă zo don yă ƙona turare a gaban Ubangiji, domin kada yă zama kamar Kora da mabiyansa.
to be a memorial to the sons of Israel, to the end that no stranger, who is not of the seed of Aaron, come near to burn incense before Jehovah, that he not be as Korah, and as his company, as Jehovah spoke to him by Moses.
41 Kashegari dukan taron Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna suka ce, “Kun kashe mutanen Ubangiji.”
But on the morrow all the congregation of the sons of Israel murmured against Moses and against Aaron, saying, Ye have killed the people of Jehovah.
42 Bayan haka, sai dukan jama’a suka taru domin su nuna rashin yardansu da abin da suke zato Musa da Haruna ne suka aikata. Da suka fuskanci Tentin Sujada, nan take sai girgije ya rufe shi, ɗaukaka Ubangiji kuwa ta bayyana.
And it came to pass, when the congregation was assembled against Moses and against Aaron, that they looked toward the tent of meeting, and, behold, the cloud covered it, and the glory of Jehovah appeared.
43 Sai Musa da Haruna suka je gaban Tentin Sujada,
And Moses and Aaron came to the front of the tent of meeting.
44 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
45 “Ku nisanci wannan taro, gama yanzu nan zan hallaka su.” Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki.
Get you up from among this congregation, that I may consume them in a moment. And they fell upon their faces.
46 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki farantinka ka sa turare a ciki, da wuta daga bagade, ka yi maza ka tafi wajen taron, ka yi kafara dominsu. Gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko; an kuma fara annoba.”
And Moses said to Aaron, Take thy censer, and put fire in it from off the altar, and lay incense on it, and carry it quickly to the congregation, and make atonement for them, for there is wrath gone out from Jehovah. The plague has begun.
47 Saboda haka Haruna ya yi kamar yadda Musa ya faɗa, ya ruga a guje zuwa tsakiyar taron. An riga an fara annobar a cikin mutane, amma Haruna ya miƙa turaren ya kuma yi kafara dominsu.
And Aaron took as Moses spoke, and ran into the midst of the assembly. And, behold, the plague had begun among the people. And he put on the incense, and made atonement for the people.
48 Ya tsaya tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.
And he stood between the dead and the living, and the plague was stopped.
49 Amma mutane 14,700 ne suka mutu a annobar, ban da waɗanda suka mutu a sanadin Kora.
Now those who died by the plague were fourteen thousand and seven hundred, besides those who died about the matter of Korah.
50 Sai Haruna ya komo wurin Musa a ƙofar Tentin Sujada, gama annobar ta ƙare.
And Aaron returned to Moses to the door of the tent of meeting, and the plague was stopped.