< Ƙidaya 16 >
1 Kora ɗan Izhar, wanda yake Balawe ne daga dangin Kohatawa, wata rana ya nemi Datan da Abiram’ya’yan Eliyab, da On ɗan Felet dukansu daga kabilar Ruben, suka haɗa kai
Chóre pak syn Izarův, syna Kahat z pokolení Léví, vytrhl se z jiných, tolikéž Dátan a Abiron, synové Eliabovi, také Hon, syn Feletův, z synů Rubenových,
2 suka tayar wa Musa. Sai suka nemi goyon bayan sanannun shugabannin Isra’ilawa da aka naɗa a majalisa su guda 250,
A povstali proti Mojžíšovi, i jiných mužů z synů Izraelských dvě stě a padesáte, knížata shromáždění, kteříž svoláváni byli do rady, muži slovoutní.
3 tare kuwa suka zo wurin Musa da Haruna, suka ce musu, “Kun wuce gona da iri! Dukan jama’an nan masu tsarki ne, kowannensu, Ubangiji kuma yana tare da su. Me ya sa kuke ɗaukan kanku fiye da taron jama’ar Ubangiji?”
A sebravše se proti Mojžíšovi a proti Aronovi, řekli jim: Příliště to již na vás; všecko zajisté množství toto, všickni tito svatí jsou, a u prostřed nich jest Hospodin. Pročež se tedy vyzdvihujete nad shromážděním Hospodinovým?
4 Da Musa ya ji haka, sai ya fāɗi rubda ciki ya yi addu’a
To když uslyšel Mojžíš, padl na tvář svou,
5 Sai ya ce wa Kora da dukan waɗannan da suke tare shi, “Da safe, Ubangiji zai nuna wane ne yake nasa, da kuma wane ne yake da tsarki. Zai kuma sa mutumin yă zo kusa da shi. Mutumin da ya zaɓa kuwa zai sa yă zo kusa da shi.
A mluvil k Chóre a ke vší rotě jeho, řka: Ráno ukáže Hospodin, kdo jsou jeho, a kdo jest svatý, i kdo před něj předstupovati má; nebo kohožkoli vyvolil, tomu rozkáže přistoupiti k sobě.
6 Kai Kora da ƙungiyarka, gobe, za ku ɗauki farantai,
Toto učiňte: Vezměte sobě kadidlnice, ty Chóre i všecko shromáždění tvé,
7 ku zuba wuta a ciki, ku kuma zuba musu turaren wuta a gaban Ubangiji. Sa’an nan wanda Ubangiji ya zaɓa a tsakaninmu sh ne mai tsarki. Ku Lawiyawa ku ne kuka wuce gona da iri!”
A naklaďte do nich uhlí, a vložte na ně kadidla před Hospodinem zítra; i stane se, že kohožkoli vyvolí Hospodin, ten bude svatý. Příliště to již na vás, synové Léví.
8 Musa ya kuma ce wa Kora, “Yanzu ku saurara, ku Lawiyawa!
I řekl Mojžíš k Chóre: Slyšte, prosím, synové Léví.
9 Ashe, bai ishe ku ba, cewa Allah na Isra’ila, ya keɓe ku daga sauran jama’ar Isra’ilawa, ya kuma kawo ku kusa da shi don ku yi aiki a tabanakul na Ubangiji, ku kuma tsaya a gaba jama’a don ku yi musu aiki?
Zdaliž málo vám to jest, že vás oddělil Bůh Izraelský ode všeho množství Izraelského, a rozkázal vám přistupovati k sobě, abyste vykonávali službu příbytku Hospodinova, a abyste stáli před shromážděním, a sloužili jim,
10 Ya kawo ku da kuma dukan’yan’uwanku Lawiyawa kusa da shi, amma yanzu kuna ƙoƙari ku karɓi aikin firist.
A vzal tě sobě, a všecky bratří tvé syny Léví s tebou, a že ještě přes to i kněžství hledáte?
11 Kai da ƙungiyarka kun haɗa kai kuna yi wa Haruna gunaguni, amma wane ne Haruna? A zahiri tawaye ne kuke wa Ubangiji.”
Protož věz, že ty a všickni tvoji jste ti, kteříž se rotíte proti Hospodinu; nebo Aron co jest, že jste reptali proti němu?
12 Sai Musa ya aika a kira Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab maza, amma suka ce, “Ba za mu zo ba!
Tedy poslal Mojžíš, aby zavolali Dátana a Abirona, synů Eliabových. Kteříž odpověděli: Nepůjdem.
13 Bai isa ba ne da ka fitar da mu daga ƙasar mai zub da madara da zuma, ka kawo mu nan hamada don ka kashe mu? Yanzu kuma so kake ka mai da kanka sarki a bisanmu?
Cožť se ještě málo zdá, že jsi vyvedl nás z země oplývající mlékem a strdí, abys nás zmořil na poušti, že také chceš i panovati nad námi, a rozkazovati nám?
14 Ban da haka ma, ai, ba ka riga ka kai mu ƙasar mai zub da madara da zuma ba, ba ka ba mu gādon filaye da gonakin annabi ba, yanzu kuma kana so ka ruɗe mu. Mun ƙi, ba za mun zo ba!”
A ještě jsi nás neuvedl do země oplývající mlékem a strdí, aniž jsi nám dal v dědictví rolí a vinic. Zdali oči mužům těmto vyloupiti chceš? Nepůjdeme.
15 Sai Musa ya husata ƙwarai, ya ce wa Ubangiji, “Kada ka karɓi hadayarsu. Ban ƙwace wani jakinsu ba, ban kuwa cuce waninsu ba.”
I rozhněval se Mojžíš velmi, a řekl k Hospodinu: Nepatřiž na oběti jejich. Ani jednoho osla od nich jsem nevzal, aniž jsem komu z nich co zlého učinil.
16 Musa ya ce wa Kora, “Da kai da kuma dukan ƙungiyarka za ku bayyana a gaban Ubangiji gobe, kai da su. Haruna ma zai kasance a can.
Potom řekl Mojžíš k Chóre: Ty a všickni tvoji, postavte se zítra před Hospodinem, ty i oni, též i Aron.
17 Kowannenku zai ɗauki faranti yă zuba turare a ciki. Wato, farantai 250 ke nan, a kuma miƙa su a gaban Ubangiji. Kai da Haruna za ku miƙa farantanku, ku ma.”
A vezmouce jeden každý kadidlnici svou, dáte do nich kadidla, a postavíte se před Hospodinem, jeden každý s kadidlnicí svou; dvě stě a padesáte kadidlnic bude, ty také i Aron, každý s kadidlnicí svou.
18 Sai kowane mutum ya ɗauki farantinsa, ya sa wuta da kuma turare a ciki, suka tsaya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada.
Tedy vzal jeden každý kadidlnici svou, a nabravše do nich uhlí, vložili na ně i kadidla, a stáli u dveří stánku úmluvy, i Mojžíši Aron.
19 Sa’ad da Kora ya tara mabiyansa don su yi hamayya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan taron.
Chóre pak již byl sebral proti nim všecko množství ke dveřím stánku úmluvy; i ukázala se sláva Hospodinova všemu množství.
20 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
I mluvil Hospodin k Mojžíšovi a k Aronovi, řka:
21 “Ku ware kanku daga taron nan don in gama da su nan take.”
Oddělte se z prostředku množství tohoto, ať je v okamžení zahladím.
22 Amma Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki suka tā da murya suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin dukan’yan adam, za ka husata da dukan taron ne, bayan mutum ɗaya ne ya yi zunubi?”
Kteřížto padše na tváři své, řekli: Bože silný, Bože duchů i všelikého těla, jediný tento člověk zhřešil, a což na všecko shromáždění hněvati se budeš?
23 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Tedy mluvil Hospodin k Mojžíšovi, řka:
24 “Faɗa wa taron cewa, ‘Ku nisanci tentin Kora, da na Datan, da na Abiram.’”
Mluv k množství a rci: Odstupte od příbytku Chóre, Dátana a Abirona.
25 Musa ya tashi ya tafi wurin Datan da Abiram, dattawan Isra’ilawa kuwa suka bi shi.
A vstav Mojžíš, šel k Dátanovi a Abironovi; i šli za ním starší Izraelští.
26 Ya gargaɗe taron ya ce, “Ku ƙaurace wa tentin waɗannan mugayen mutane! Kada ku taɓa kome da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.”
A mluvil k množství, řka: Odstupte, prosím, od stanů bezbožných mužů těchto, aniž se čeho dotýkejte, což jejich jest, abyste nebyli zachváceni ve všech hříších jejich.
27 Sai suka tashi daga inda tentin Kora, da Datan, da Abiram suke. Datan da Abiram kuwa suka fita suna tsaye tare da matansu da’ya’yansu da’yan ƙananansu a ƙofar tentinsu.
I odstoupili se všech stran od příbytku Chóre, Dátana a Abirona; ale Dátan a Abiron vyšedše, stáli u dveří stanů svých, i ženy jejich a synové jejich, i maličcí jejich.
28 Sai Musa ya ce musu, “Da haka za ku san cewa Ubangiji ne ya aiko ni, in yi dukan waɗannan abubuwa, ba da nufin kaina na yi su ba.
Tedy řekl Mojžíš: Po tomto poznáte, že Hospodin poslal mne, abych činil všecky skutky tyto, a že nic o své ujmě nečiním:
29 In waɗannan mutane sun mutu kamar yadda mutane suke mutuwa, in abin da yakan sami kowa shi ne ya same su, to, ba Ubangiji ne ya aiko ni ba.
Jestliže tak jako jiní lidé mrou, zemrou i tito, a navštívením obecným všechněm lidem jestliže navštíveni budou, neposlal mne Hospodin.
30 Amma in Ubangiji ya kawo wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara cikin kabari a raye, ta haka za ku sani mutanen nan sun rena Ubangiji.” (Sheol )
Pakliť něco nového učiní Hospodin, a země, otevra ústa svá, požře je se vším, což mají, a sstoupí-li za živa do pekla, tedy poznáte, že jsou popouzeli muži ti Hospodina. (Sheol )
31 Nan da nan da ya gama faɗi wannan, sai ƙasa ta tsage inda Datan da Abiram suke tsaye,
I stalo se, když přestal mluviti slov těch, že rozstoupila se země pod nimi.
32 ta kuma buɗe bakinta, ta haɗiye su tare da mutanen gidansu da dukan mutanen Kora da dukan abin da yake mallakarsu.
A otevřevši země ústa svá, požřela je i domy jejich i všecky lidi, kteříž byli s Chóre, i všecken statek jejich.
33 Suka gangara cikin kabari da rai, tare dukan mallakarsu; ƙasa ta rufe su, suka hallaka, suka rabu da jama’ar. (Sheol )
A tak sstoupili oni se vším, což měli, za živa do pekla, a přikryla je země; i zahynuli z prostředku shromáždění. (Sheol )
34 Da jin kukansu, dukan Isra’ilawa da suke kewaye da su suka gudu, suna ihu, “Ƙasa za tă haɗiye mu, mu ma!”
Všickni pak Izraelští, kteříž byli vůkol nich, utíkali, slyšíce křik jejich; nebo řekli: Utecme, aby i nás nesehltila země.
35 Sai wuta ta fito daga wurin Ubangiji ta cinye mutane 250 da suke miƙa hadaya da turare.
Vyšel také oheň od Hospodina, a spálil těch dvě stě a padesáte mužů, kteříž kadili.
36 Ubangiji ya ce wa Musa,
Tedy mluvil Hospodin k Mojžíšovi, řka:
37 “Ka gaya wa Eleyazar ɗan Haruna, firist, yă kawar da farantan ƙona turare daga wurin da wutar ta cinye, yă watsar da gawayin a wani wuri, gama farantan tsarkakakku ne,
Rci Eleazarovi, synu Arona kněze, ať sbéře kadidlnice z toho spáleniště, a uhlí z nich pryč rozmece, nebo posvěceny jsou,
38 gama an yi amfani da farantan don miƙa mini turare. Sai ka ɗauki farantan mutanen da suka yi zunubin da ya jawo musu mutuwa ka ƙera farantan, ka yi murfin bagade da su, gama an miƙa su a gaban Ubangiji, suka zama tsarkakakku. Bari su zama alama ga Isra’ilawa.”
Kadidlnice totiž těch, kteříž proti svým dušem hřešili, a ať je rozkuje na plechy k obložení oltáře; nebo kadili jimi před Hospodinem, protož posvěceny jsou, a budou na znamení synům Izraelským.
39 Haka Eleyazar, firist, ya tattara farantan tagulla waɗanda mutanen da aka hallaka suka kawo, ya ƙera murfin bagade da su,
I sebral Eleazar kněz kadidlnice měděné, jimiž kadili ti, kteříž spáleni jsou, a rozkovali je k obložení oltáře,
40 yadda Ubangiji ya umarce shi, ta wurin Musa. Wannan ya zama abin tuni ga Isra’ilawa domin kada wani da ba firist ba, bai kuwa fito a cikin zuriyar Haruna ba, yă zo don yă ƙona turare a gaban Ubangiji, domin kada yă zama kamar Kora da mabiyansa.
Pro budoucí pamět synům Izraelským, aby nepřistupoval žádný jiný, kdož by nebyl z rodu Aronova, k kadění před Hospodinem, aby se mu nestalo jako Chóre a jako rotě jeho, jakož byl mluvil jemu Hospodin skrze Mojžíše.
41 Kashegari dukan taron Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna suka ce, “Kun kashe mutanen Ubangiji.”
Nazejtří pak reptalo všecko množství synů Izraelských na Mojžíše a na Arona, řkouce: Vy jste příčinou smrti lidu Hospodinova.
42 Bayan haka, sai dukan jama’a suka taru domin su nuna rashin yardansu da abin da suke zato Musa da Haruna ne suka aikata. Da suka fuskanci Tentin Sujada, nan take sai girgije ya rufe shi, ɗaukaka Ubangiji kuwa ta bayyana.
I stalo se, když se opět sbíral lid proti Mojžíšovi a proti Aronovi, že se ohlédli k stánku úmluvy, a aj, přikryl jej oblak, a ukázala se sláva Hospodinova.
43 Sai Musa da Haruna suka je gaban Tentin Sujada,
Přišel také Mojžíš s Aronem před stánek úmluvy.
44 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
I mluvil Hospodin k Mojžíšovi, řka:
45 “Ku nisanci wannan taro, gama yanzu nan zan hallaka su.” Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki.
Vyjděte z prostředku množství tohoto, a zahladím je v okamžení. I padli na tváři své.
46 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki farantinka ka sa turare a ciki, da wuta daga bagade, ka yi maza ka tafi wajen taron, ka yi kafara dominsu. Gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko; an kuma fara annoba.”
Tedy řekl Mojžíš Aronovi: Vezma kadidlnici, dej do ní uhlí z oltáře, a vlož kadidla, a běž rychle k množství a očisť je; nebo vyšla prchlivost od tváři Hospodinovy, a již rána se začala.
47 Saboda haka Haruna ya yi kamar yadda Musa ya faɗa, ya ruga a guje zuwa tsakiyar taron. An riga an fara annobar a cikin mutane, amma Haruna ya miƙa turaren ya kuma yi kafara dominsu.
I vzav Aron kadidlnici, jakž rozkázal Mojžíš, běžel do prostřed shromáždění, (a aj, rána již se byla začala v lidu, ) a zakadiv, očistil lid.
48 Ya tsaya tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.
A stál mezi mrtvými a živými; i zastavena jest rána.
49 Amma mutane 14,700 ne suka mutu a annobar, ban da waɗanda suka mutu a sanadin Kora.
Bylo pak těch, kteříž od té rány zemřeli, čtrnácte tisíců a sedm set, kromě těch, jenž zemřeli příčinou Chóre.
50 Sai Haruna ya komo wurin Musa a ƙofar Tentin Sujada, gama annobar ta ƙare.
I navrátil se Aron k Mojžíšovi, ke dveřím stánku úmluvy, když ta rána přetržena byla.