< Ƙidaya 15 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yavé habló a Moisés:
2 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Bayan kun shiga ƙasar da nake ba ku a matsayin gida,
Habla a los hijos de Israel: Cuando entren en la tierra en la cual van a vivir y que Yo les doy,
3 kuka yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji, daga cikin shanu, ko tumaki, abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa, ko hadayu don alkawura na musamman, ko hadayar yardar rai, ko kuma hadaya ta biki,
y ofrezcan sacrificio quemado a Yavé del ganado vacuno o del rebaño, holocausto, sacrificio por voto especial, por su voluntad, o en sus fiestas solemnes para ofrecer olor que apacigua a Yavé,
4 sai shi wanda ya kawo hadayar yă miƙa wa Ubangiji hadaya ta gari mai laushi mai kyau, kashi ɗaya bisa goma na efa wanda aka kwaɓa da kwalaba ɗaya na mai.
el que presente su ofrenda a Yavé llevará como ofrenda vegetal 2,2 litros de flor de harina, amasada con 0,9 litros de aceite.
5 Da kowane ɗan rago don hadaya ta ƙonawa, a shirya kwalaba ɗaya na ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha.
Presentarás vino para la libación, 0,9 litros con el holocausto o para el sacrificio por cada cordero.
6 “‘In da rago ne za a miƙa, to, sai a shirya hadaya ta gari mai laushi, garin yă zama kashi biyu bisa goma na efa. A kwaɓa shi da kashi ɗaya bisa uku na garwan mai,
Por un carnero presentarás como ofrenda vegetal 4,4 litros de flor de harina, amasada con 1,2 litros de aceite,
7 da kashi ɗaya bisa uku na garwan ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha. A miƙa ta abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
y de vino para la libación, 1,2 litros, el cual ofrecerás como olor que apacigua a Yavé.
8 “‘Sa’ad da kuka shirya rago don hadaya ta ƙonawa saboda alkawari na musamman, ko hadaya ta salama ga Ubangiji,
Pero si deseas sacrificar un buey en holocausto o sacrificio en cumplimiento de un voto, o como sacrificio de paz a Yavé,
9 sai ku kawo hadaya ta gari tare da bijimi, kashi ɗaya bisa uku na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da rabin garwan mai.
ofrecerá además del buey, una ofrenda vegetal de 6,6 litros de flor de harina, amasada con 1,8 litros de aceite.
10 A kuma kawo rabin garwan ruwan inabi na hadaya ta sha. Za tă zama hadayar da aka yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
Para la libación ofrecerás 1,8 litros de vino, en sacrificio quemado de olor que apacigua a Yavé.
11 Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru.
Así hará con cada buey, carnero, cría de ovejas o de cabras
12 Haka za a yi da kowannensu bisa ga abin da aka shirya.
según el número [de sacrificios] que ofrezcan. Así ofrecerán según la cantidad de ellos.
13 “‘Duk wanda yake ɗan ƙasa, ta haka ne dole zai aikata waɗannan abubuwa sa’ad da ya kawo hadaya da akan yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
Todos ustedes, los de la congregación, harán estas cosas así para ofrecer el sacrificio quemado en olor que apacigua a Yavé.
14 Idan baƙon da yake baƙunci a cikinku, ko kowane ne da yake tare da ku a dukan zamananku, yana so yă ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, dole yă yi kamar yadda kuke yi.
Cuando un extranjero resida entre ustedes, o alguien viva en medio de ustedes en sus sucesivas generaciones, y desee ofrecer un sacrificio quemado de olor que apacigua a Yavé, lo hará como ustedes lo hacen.
15 Ƙa’ida ɗaya ce ga jama’a da kuma baƙin da suke zama a cikinku, wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a dukan tsararraki masu zuwa. Da ku, da baƙi, za ku zama ɗaya a gaban Ubangiji.
Tendrán un mismo estatuto tanto para ustedes, los de la congregación, como para el extranjero que está con ustedes. Habrá un estatuto perpetuo delante de Yavé en sus generaciones, tanto para ustedes como para el extranjero.
16 Doka ɗaya da ƙa’ida ɗaya za a yi aiki da ita a kan ku da kuma baƙin da suke zama a cikinku.’”
Una sola Ley y un solo decreto tendrán tanto para ustedes como para el extranjero que está con ustedes.
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yavé habló a Moisés:
18 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da ina kai ku,
Habla a los hijos de Israel: Cuando entren en la tierra a la cual Yo los llevo,
19 kuka ci abincin ƙasar, ku miƙa wani sashe na amfanin ƙasar a matsayin hadaya ga Ubangiji.
sucederá que cuando coman el alimento de la tierra, presentarán una ofrenda alzada ante Yavé.
20 Ku kawo waina daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku, ku kuma miƙa shi a matsayin hadaya daga masussuka.
De lo primero que amasen, ofrecerán una torta como ofrenda alzada. La ofrecerán como ofrenda alzada de la era.
21 A duk tsararraki masu zuwa, za ku miƙa wannan hadaya daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku ga Ubangiji.
Así que, de las primicias de lo que amasen, ofrecerán una ofrenda alzada a Yavé en sus generaciones.
22 “‘To, in ku a matsayin jama’a, da gangan kuka ƙi kiyaye waɗannan ƙa’idodi da Ubangiji ya ba wa Musa ba,
Cuando fallen y no cumplan todos estos Mandamientos que Yavé habló a Moisés,
23 ko wani daga cikin umarnan da Ubangiji ya ba ku ta wurinsa, daga ranar da Ubangiji ya ba da su, har zuwa tsararraki masu zuwa,
todas las cosas que Yavé les ordenó por medio de Moisés desde el día cuando Yavé lo mandó y en adelante en sus generaciones,
24 in kuwa aka yi haka ba da gangan ba, kuma da rashin sani, sai duk jama’a su miƙa ɗan bijimi don hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, tare da ƙayyadadden hadaya ta gari, da hadaya ta sha, da kuma bunsuru na hadaya don zunubi.
si el pecado fue cometido por error con ignorancia de la congregación, toda la asamblea ofrecerá un buey como holocausto en olor que apacigua a Yavé, con su ofrenda vegetal y su libación conforme a la ordenanza, juntamente con un macho cabrío en sacrificio por el pecado.
25 Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuma gafarta musu, gama ba da gangan ba ne suka aikata, kuma sun kawo wa Ubangiji hadayar da akan yi da wuta da kuma hadaya don zunubi saboda laifinsu.
El sacerdote hará sacrificio que apacigua a favor de toda la congregación de los hijos de Israel, y les será perdonado, pues fue error. Traerán su ofrenda: un sacrificio quemado a Yavé y su sacrificio que apacigua por su pecado.
26 Za a gafarta wa dukan jama’ar Isra’ilawa, da baƙin da suke zama a cikinsu, gama duk laifin da aka yi da rashin sani, yakan shafi dukan mutane.
Le será perdonado a toda la congregación de los hijos de Israel y al extranjero que reside entre ustedes, porque fue error de todo el pueblo.
27 “‘Amma in mutum ɗaya ne kaɗai ya yi laifi ba da gangan ba, dole yă kawo akuya domin hadaya don zunubi.
Si una persona peca por error, ofrecerá una cabra de un año en sacrificio que apacigua por el pecado,
28 Firist zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin nan da ya aikata laifi ba da gangan ba, in kuwa an yi kafara saboda shi, za a gafarta masa.
y el sacerdote hará sacrificio que apacigua a favor de la persona que pecó por error ante Yavé. Al hacer sacrificio que apacigua a su favor, le será perdonado.
29 Ƙa’ida dai za tă zama ɗaya ga duk wanda ya yi laifi ba da gangan ba, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙon da yake zama a cikinku.
Una misma Ley tendrán para el que cometa error por ignorancia, tanto para el nativo entre los hijos de Israel como para el extranjero que está entre ustedes.
30 “‘Amma duk wanda ya yi zunubi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko baƙo, ya saɓi Ubangiji, dole a ware wannan mutum daga mutanensa,
Pero la persona que haga algo con altivez, sea de la congregación o extranjero, blasfema ante Yavé. Esa persona será cortada de en medio de su pueblo,
31 gama ya rena maganar Ubangiji, ya kuma karya umarninsa. Tabbatacce za a kashe wannan mutum, alhakinsa laifinsa kuwa yana wuyansa.’”
porque despreció la Palabra de Yavé y quebrantó su Mandamiento. Esa persona será cortada de en medio de su pueblo. Su iniquidad caerá sobre ella.
32 Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
Mientras los hijos de Israel estaban en el desierto, sorprendieron a un hombre que recogía leña en sábado.
33 Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
Los que lo sorprendieron mientras recogía leña lo presentaron ante Moisés y Aarón y toda la asamblea,
34 sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
y lo pondrán bajo custodia porque aún no se había declarado lo que se le debía hacer.
35 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
Entonces Yavé dijo a Moisés: Ese hombre ciertamente debe morir. Que toda la congregación lo apedree fuera del campamento.
36 Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Entonces la congregación lo sacó del campamento y lo apedrearon, y murió, como Yavé ordenó a Moisés.
37 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yavé habló a Moisés:
38 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘A dukan tsararraki masu zuwa, za ku sa tuntaye a gefen rigunarku, su sa zare mai ruwan shuɗi a bisan kowane tuntu.
Habla a los hijos de Israel y diles que a través de sus generaciones se hagan flecos en los bordes de sus ropas, y que en cada fleco de los bordes pongan un cordón azul.
39 Tuntayen za su zama muku abin dubawa don ku riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji, don kada ku bi son zuciyarku, da sha’awar idanunku yadda kuka taɓa yi.
Estos flecos les servirán para que, cuando los vean, se acuerden de todos los Mandamientos de Yavé y los cumplan, y no sigan el impulso de su corazón ni de sus ojos, tras el cual se prostituyen,
40 Sa’an nan za ku riƙa tuna, ku kuma aikata dukan umarnaina ku zama tsarkaka ga Allahnku.
a fin de que recuerden y cumplan todos mis Mandamientos y estén consagrados a su ʼElohim.
41 Ni ne Ubangiji Allahnku, da ya fitar da ku daga Masar, don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Yo, Yavé su ʼElohim, Quien los sacó de la tierra de Egipto para ser su ʼElohim. ¡Yo, Yavé su ʼElohim!