< Ƙidaya 15 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Entonces el Señor le dijo a Moisés:
2 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Bayan kun shiga ƙasar da nake ba ku a matsayin gida,
“Dile a los israelitas, ‘Estas son la instrucciones sobre lo que deben hacer una vez que lleguen al país que les doy para vivir:
3 kuka yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji, daga cikin shanu, ko tumaki, abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa, ko hadayu don alkawura na musamman, ko hadayar yardar rai, ko kuma hadaya ta biki,
Cuando traiga una ofrenda al Señor de tu ganado o rebaño (ya sea un holocausto, un sacrificio para cumplir una promesa que hiciste, o una ofrenda de libre albedrío o de fiesta) que sea aceptable para el Señor,
4 sai shi wanda ya kawo hadayar yă miƙa wa Ubangiji hadaya ta gari mai laushi mai kyau, kashi ɗaya bisa goma na efa wanda aka kwaɓa da kwalaba ɗaya na mai.
entonces también presentarás una ofrenda de grano de una décima parte de un efa de la mejor harina mezclada con un cuarto de hin de aceite de oliva.
5 Da kowane ɗan rago don hadaya ta ƙonawa, a shirya kwalaba ɗaya na ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha.
Añade un cuarto de hin de vino como ofrenda de bebida al holocausto o al sacrificio de un cordero.
6 “‘In da rago ne za a miƙa, to, sai a shirya hadaya ta gari mai laushi, garin yă zama kashi biyu bisa goma na efa. A kwaɓa shi da kashi ɗaya bisa uku na garwan mai,
“Cuando se trate de un carnero, presenta una ofrenda de grano de dos décimas de efa de la mejor harina mezclada con un tercio de hin de aceite de oliva,
7 da kashi ɗaya bisa uku na garwan ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha. A miƙa ta abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
junto con un tercio de hin de vino como ofrenda de bebida, todo ello para ser aceptable al Señor.
8 “‘Sa’ad da kuka shirya rago don hadaya ta ƙonawa saboda alkawari na musamman, ko hadaya ta salama ga Ubangiji,
“Cuando traigas un novillo como holocausto o sacrificio para cumplir una promesa que hiciste o como ofrenda de paz al Señor,
9 sai ku kawo hadaya ta gari tare da bijimi, kashi ɗaya bisa uku na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da rabin garwan mai.
también llevarás con el novillo una ofrenda de grano de tres décimas de efa de la mejor harina mezclada con medio hin de aceite de oliva.
10 A kuma kawo rabin garwan ruwan inabi na hadaya ta sha. Za tă zama hadayar da aka yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
Añade medio hin de vino como ofrenda de bebida. Todo esto es una ofrenda para ser aceptable al Señor.
11 Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru.
“Esto debe hacerse por cada toro, carnero, cordero o cabra que se traiga como ofrenda.
12 Haka za a yi da kowannensu bisa ga abin da aka shirya.
Esto es lo que tienes que hacer para cada uno, sin importar cuántos sean.
13 “‘Duk wanda yake ɗan ƙasa, ta haka ne dole zai aikata waɗannan abubuwa sa’ad da ya kawo hadaya da akan yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
Todo israelita debe seguir estas instrucciones cuando presente una ofrenda que sea aceptable para el Señor.
14 Idan baƙon da yake baƙunci a cikinku, ko kowane ne da yake tare da ku a dukan zamananku, yana so yă ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, dole yă yi kamar yadda kuke yi.
Esto también se aplica a todas las generaciones futuras que si un extranjero que vive entre ustedes o cualquier otra persona entre ustedes desea presentar una ofrenda aceptable para el Señor: deben hacer exactamente lo que ustedes hacen.
15 Ƙa’ida ɗaya ce ga jama’a da kuma baƙin da suke zama a cikinku, wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a dukan tsararraki masu zuwa. Da ku, da baƙi, za ku zama ɗaya a gaban Ubangiji.
Toda la congregación debe tener las mismas reglas para ustedes y para el extranjero que vive entre ustedes. Esta es una ley permanente para todas las generaciones futuras. Tú y el extranjero deben ser tratados de la misma manera ante la ley.
16 Doka ɗaya da ƙa’ida ɗaya za a yi aiki da ita a kan ku da kuma baƙin da suke zama a cikinku.’”
Las mismas reglas y normas se aplican a ustedes y al extranjero que vive entre ustedes’”.
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
El Señor le dijo a Moisés:
18 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da ina kai ku,
“Diles a los israelitas: ‘Cuando lleguen al país al que yo los llevo
19 kuka ci abincin ƙasar, ku miƙa wani sashe na amfanin ƙasar a matsayin hadaya ga Ubangiji.
y cománde los alimentos que allí se producen, darán parte de ellos como ofrenda al Señor.
20 Ku kawo waina daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku, ku kuma miƙa shi a matsayin hadaya daga masussuka.
Darán como ofrenda una parte de la harina que usen para hacer los panes, y la presentarás como una ofrenda de la era.
21 A duk tsararraki masu zuwa, za ku miƙa wannan hadaya daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku ga Ubangiji.
Para todas las generaciones futuras, darás al Señor una ofrenda de la primera de tus harinas.
22 “‘To, in ku a matsayin jama’a, da gangan kuka ƙi kiyaye waɗannan ƙa’idodi da Ubangiji ya ba wa Musa ba,
“Ahora bien, si pecan colectivamente sin querer y no siguen todas estas instrucciones que el Señor ha dado a Moisés,
23 ko wani daga cikin umarnan da Ubangiji ya ba ku ta wurinsa, daga ranar da Ubangiji ya ba da su, har zuwa tsararraki masu zuwa,
s decir, todo lo que el Señor les ha ordenado hacer a través de Moisés desde el momento en que el Señor les dio y para todas las generaciones futuras,
24 in kuwa aka yi haka ba da gangan ba, kuma da rashin sani, sai duk jama’a su miƙa ɗan bijimi don hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, tare da ƙayyadadden hadaya ta gari, da hadaya ta sha, da kuma bunsuru na hadaya don zunubi.
y si se hizo sin querer y sin que todos lo supieran, entonces toda la congregación debe presentar un novillo como holocausto para ser aceptado por el Señor, junto con su ofrenda de grano y su libación presentada según las reglas, así como un macho cabrío como ofrenda por el pecado.
25 Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuma gafarta musu, gama ba da gangan ba ne suka aikata, kuma sun kawo wa Ubangiji hadayar da akan yi da wuta da kuma hadaya don zunubi saboda laifinsu.
De esta manera el sacerdote debe hacer que toda la congregación de Israel esté bien con el Señor para que puedan ser perdonados, porque el pecado fue involuntario y han presentado al Señor un holocausto y una ofrenda por el pecado, ofrecida ante el Señor por su pecado involuntario.
26 Za a gafarta wa dukan jama’ar Isra’ilawa, da baƙin da suke zama a cikinsu, gama duk laifin da aka yi da rashin sani, yakan shafi dukan mutane.
Entonces toda la congregación de Israel y los extranjeros que viven entre ellos serán perdonados, porque el pueblo pecó sin intención.
27 “‘Amma in mutum ɗaya ne kaɗai ya yi laifi ba da gangan ba, dole yă kawo akuya domin hadaya don zunubi.
“En el caso de un individuo que peca sin intención, deben presentar una cabra hembra de un año como ofrenda por el pecado.
28 Firist zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin nan da ya aikata laifi ba da gangan ba, in kuwa an yi kafara saboda shi, za a gafarta masa.
El sacerdote hará que la persona que pecó sin querer esté en su derecho ante el Señor. Una vez que hayan sido expiados, serán perdonados.
29 Ƙa’ida dai za tă zama ɗaya ga duk wanda ya yi laifi ba da gangan ba, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙon da yake zama a cikinku.
Aplicarás la misma ley para el que peca por error a un israelita o a un extranjero que viva entre ustedes.
30 “‘Amma duk wanda ya yi zunubi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko baƙo, ya saɓi Ubangiji, dole a ware wannan mutum daga mutanensa,
“Pero la persona que peca a manera de desafío, ya sea un israelita o un extranjero, está blasfemando al Señor. Serán expulsados de su pueblo.
31 gama ya rena maganar Ubangiji, ya kuma karya umarninsa. Tabbatacce za a kashe wannan mutum, alhakinsa laifinsa kuwa yana wuyansa.’”
Deben ser expulsados, porque han tratado la palabra del Señor con desprecio y han quebrantado su mandamiento. Son responsables de las consecuencias de su propia culpa’”.
32 Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
Durante el tiempo en que los israelitas vagaban por el desierto, un hombre fue sorprendido recogiendo leña en el día Sábado.
33 Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
Las personas que lo encontraron recogiendo leña lo llevaron ante Moisés, Aarón y el resto de los israelitas.
34 sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
Lo pusieron bajo vigilancia porque no estaba claro qué le iba a pasar.
35 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
El Señor le dijo a Moisés: “Este hombre tiene que ser ejecutado. Todos los israelitas deben apedrearlo fuera del campamento”.
36 Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Así que todos tomaron al hombre fuera del campamento y lo apedrearon hasta la muerte como el Señor había ordenado a Moisés.
37 Ubangiji ya ce wa Musa,
Poco después el Señor le dijo a Moisés:
38 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘A dukan tsararraki masu zuwa, za ku sa tuntaye a gefen rigunarku, su sa zare mai ruwan shuɗi a bisan kowane tuntu.
“Diles a los israelitas que para todas las generaciones futuras harán borlas para los dobladillos de tu ropa y deberán atarlas con un cordón azul.
39 Tuntayen za su zama muku abin dubawa don ku riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji, don kada ku bi son zuciyarku, da sha’awar idanunku yadda kuka taɓa yi.
Cuando miren estas borlas recordarán que deben guardar todos los mandamientos del Señor y que no sean infieles, siguiendo sus propios pensamientos y deseos.
40 Sa’an nan za ku riƙa tuna, ku kuma aikata dukan umarnaina ku zama tsarkaka ga Allahnku.
De esta manera serecordarán que deben guardar todos mis mandamientos y serán santos para Dios. Yo soy el Señor su Dios que los sacó de Egipto para ser su Dios.
41 Ni ne Ubangiji Allahnku, da ya fitar da ku daga Masar, don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
¡Yo soy el Señor su Dios!”