< Ƙidaya 15 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
L’Éternel parla à Moïse en ces termes:
2 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Bayan kun shiga ƙasar da nake ba ku a matsayin gida,
"Parle aux enfants d’Israël et dis-leur: Quand vous serez arrivés dans le pays que je vous destine pour votre établissement,
3 kuka yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji, daga cikin shanu, ko tumaki, abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa, ko hadayu don alkawura na musamman, ko hadayar yardar rai, ko kuma hadaya ta biki,
et que vous ferez un sacrifice à l’Éternel, holocauste ou autre victime, à l’occasion d’un vœu spécial ou d’un don spontané, ou lors de vos solennités, voulant offrir, en odeur agréable au Seigneur, une pièce de gros ou de menu bétail,
4 sai shi wanda ya kawo hadayar yă miƙa wa Ubangiji hadaya ta gari mai laushi mai kyau, kashi ɗaya bisa goma na efa wanda aka kwaɓa da kwalaba ɗaya na mai.
celui qui offrira ce sacrifice à l’Éternel y joindra, comme oblation, un dixième de fleur de farine, pétrie avec un quart de hîn d’huile;
5 Da kowane ɗan rago don hadaya ta ƙonawa, a shirya kwalaba ɗaya na ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha.
plus, du vin, comme libation, un quart de hîn, que tu joindras à l’holocauste ou au sacrifice, pour chaque agneau.
6 “‘In da rago ne za a miƙa, to, sai a shirya hadaya ta gari mai laushi, garin yă zama kashi biyu bisa goma na efa. A kwaɓa shi da kashi ɗaya bisa uku na garwan mai,
Si c’est un bélier, tu offriras comme oblation deux dixièmes de fleur de farine, pétrie avec un tiers de hîn d’huile;
7 da kashi ɗaya bisa uku na garwan ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha. A miƙa ta abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
plus, du vin pour libation, un tiers de hîn, que tu offriras, comme odeur délectable, au Seigneur.
8 “‘Sa’ad da kuka shirya rago don hadaya ta ƙonawa saboda alkawari na musamman, ko hadaya ta salama ga Ubangiji,
Et si c’est une pièce de gros bétail que tu offres comme holocauste ou autre sacrifice, à l’occasion d’un vœu particulier ou comme rémunératoire au Seigneur,
9 sai ku kawo hadaya ta gari tare da bijimi, kashi ɗaya bisa uku na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da rabin garwan mai.
on ajoutera à cette victime, comme oblation, trois dixièmes de fleur de farine, pétrie avec un demi-hîn d’huile;
10 A kuma kawo rabin garwan ruwan inabi na hadaya ta sha. Za tă zama hadayar da aka yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
et tu offriras, comme libation, un demi-hîn de vin: sacrifice d’odeur agréable à l’Éternel.
11 Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru.
C’Est ainsi qu’on en usera pour chaque taureau, pour chaque bélier, pour chaque animal de l’espèce des brebis ou des chèvres;
12 Haka za a yi da kowannensu bisa ga abin da aka shirya.
selon le nombre des victimes que vous offrirez, vous suivrez ces prescriptions pour chacune, en nombre égal.
13 “‘Duk wanda yake ɗan ƙasa, ta haka ne dole zai aikata waɗannan abubuwa sa’ad da ya kawo hadaya da akan yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
Tout indigène pratiquera ainsi ces rites, lorsqu’il offrira un sacrifice d’odeur agréable au Seigneur.
14 Idan baƙon da yake baƙunci a cikinku, ko kowane ne da yake tare da ku a dukan zamananku, yana so yă ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, dole yă yi kamar yadda kuke yi.
Et si un étranger émigre chez vous ou se trouve parmi vous, dans les âges ultérieurs, et qu’il offre à l’Éternel un sacrifice d’odeur agréable, comme vous procéderez, ainsi procédera-t-il.
15 Ƙa’ida ɗaya ce ga jama’a da kuma baƙin da suke zama a cikinku, wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a dukan tsararraki masu zuwa. Da ku, da baƙi, za ku zama ɗaya a gaban Ubangiji.
Peuple, une même loi vous régira, vous et l’étranger domicilié. Règle absolue pour vos générations: vous et l’étranger, vous serez égaux devant l’Éternel.
16 Doka ɗaya da ƙa’ida ɗaya za a yi aiki da ita a kan ku da kuma baƙin da suke zama a cikinku.’”
Même loi et même droit existeront pour vous et pour l’étranger habitant parmi vous."
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
L’Éternel parla à Moïse en ces termes:
18 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da ina kai ku,
"Parle aux enfants d’Israël et dis-leur: A votre arrivée dans le pays où je vous conduirai,
19 kuka ci abincin ƙasar, ku miƙa wani sashe na amfanin ƙasar a matsayin hadaya ga Ubangiji.
lorsque vous mangerez du pain de la contrée, vous en prélèverez un tribut au Seigneur.
20 Ku kawo waina daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku, ku kuma miƙa shi a matsayin hadaya daga masussuka.
Comme prémices de votre pâte, vous prélèverez un gâteau en tribut; à l’instar du tribut de la grange, ainsi vous le prélèverez.
21 A duk tsararraki masu zuwa, za ku miƙa wannan hadaya daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku ga Ubangiji.
Des prémices de votre pâte vous ferez hommage à l’Éternel dans vos générations futures.
22 “‘To, in ku a matsayin jama’a, da gangan kuka ƙi kiyaye waɗannan ƙa’idodi da Ubangiji ya ba wa Musa ba,
Si, par suite d’une erreur, vous n’observez pas tous ces commandements que l’Éternel a communiqués à Moïse,
23 ko wani daga cikin umarnan da Ubangiji ya ba ku ta wurinsa, daga ranar da Ubangiji ya ba da su, har zuwa tsararraki masu zuwa,
tout ce que l’Éternel a prescrit à votre intention par l’organe de Moïse, et cela depuis l’époque où l’Éternel l’a prescrit jusqu’à vos générations ultérieures;
24 in kuwa aka yi haka ba da gangan ba, kuma da rashin sani, sai duk jama’a su miƙa ɗan bijimi don hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, tare da ƙayyadadden hadaya ta gari, da hadaya ta sha, da kuma bunsuru na hadaya don zunubi.
si c’est par l’inadvertance de la communauté qu’a eu lieu cette erreur, la communauté entière offrira un jeune taureau comme holocauste, en odeur agréable à l’Éternel, avec son oblation et sa libation selon la règle; plus un bouc, comme expiatoire.
25 Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuma gafarta musu, gama ba da gangan ba ne suka aikata, kuma sun kawo wa Ubangiji hadayar da akan yi da wuta da kuma hadaya don zunubi saboda laifinsu.
Le pontife effacera la faute de toute la communauté des enfants d’Israël, et elle leur sera remise, parce que c’était une erreur, et qu’ils ont apporté devant Dieu leur offrande, un sacrifice destiné au feu pour le Seigneur, ainsi que leur expiatoire, pour réparer cette erreur.
26 Za a gafarta wa dukan jama’ar Isra’ilawa, da baƙin da suke zama a cikinsu, gama duk laifin da aka yi da rashin sani, yakan shafi dukan mutane.
Et il sera pardonné à toute la communauté des enfants d’Israël et à l’étranger qui séjourne parmi eux; car l’erreur a été commune à tout le peuple.
27 “‘Amma in mutum ɗaya ne kaɗai ya yi laifi ba da gangan ba, dole yă kawo akuya domin hadaya don zunubi.
Que si c’est une seule personne qui a péché par erreur, elle offrira une chèvre, âgée d’un an pour expiatoire.
28 Firist zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin nan da ya aikata laifi ba da gangan ba, in kuwa an yi kafara saboda shi, za a gafarta masa.
Le pontife fera expiation pour la personne imprudente (car elle n’a péché que par imprudence) devant le Seigneur; afin qu’étant expiée, sa faute lui soit remise.
29 Ƙa’ida dai za tă zama ɗaya ga duk wanda ya yi laifi ba da gangan ba, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙon da yake zama a cikinku.
Indigène entre les enfants d’Israël ou étranger résidant parmi eux, une même règle sera la vôtre, si l’on a agi par erreur.
30 “‘Amma duk wanda ya yi zunubi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko baƙo, ya saɓi Ubangiji, dole a ware wannan mutum daga mutanensa,
Mais celui qui aurait agi ainsi de propos délibéré, parmi les nationaux ou parmi les étrangers, celui-là outrage le Seigneur! Cette personne sera retranchée du milieu de son peuple.
31 gama ya rena maganar Ubangiji, ya kuma karya umarninsa. Tabbatacce za a kashe wannan mutum, alhakinsa laifinsa kuwa yana wuyansa.’”
Pour avoir méprisé la parole du Seigneur, pour avoir violé sa loi, cette personne sera certainement retranchée: elle est coupable!"
32 Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
Pendant leur séjour au désert, les enfants d’Israël trouvèrent un homme ramassant du bois le jour du Sabbat.
33 Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
Ceux qui l’avaient trouvé ramassant du bois le conduisirent devant Moïse et Aaron, et devant toute la communauté.
34 sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
On le mit en lieu sûr, parce qu’il n’avait pas été expliqué comment il fallait agir à son égard.
35 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
Alors l’Éternel dit à Moïse: "Cet homme doit être mis à mort; que toute la communauté le lapide hors du camp."
36 Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Et toute la communauté l’emmena hors du camp, et on le fit mourir à coups de pierres, comme l’Éternel l’avait ordonné à Moïse.
37 Ubangiji ya ce wa Musa,
L’Éternel parla à Moïse en ces termes:
38 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘A dukan tsararraki masu zuwa, za ku sa tuntaye a gefen rigunarku, su sa zare mai ruwan shuɗi a bisan kowane tuntu.
"Parle aux enfants d’Israël, et dis-leur de se faire des franges aux coins de leurs vêtements, dans toutes leurs générations, et d’ajouter à la frange de chaque coin un cordon d’azur.
39 Tuntayen za su zama muku abin dubawa don ku riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji, don kada ku bi son zuciyarku, da sha’awar idanunku yadda kuka taɓa yi.
Cela formera pour vous des franges dont la vue vous rappellera tous les commandements de l’Éternel, afin que vous les exécutiez et ne vous égariez pas à la suite de votre cœur et de vos yeux, qui vous entraînent à l’infidélité.
40 Sa’an nan za ku riƙa tuna, ku kuma aikata dukan umarnaina ku zama tsarkaka ga Allahnku.
Vous vous rappellerez ainsi et vous accomplirez tous mes commandements, et vous serez saints pour votre Dieu.
41 Ni ne Ubangiji Allahnku, da ya fitar da ku daga Masar, don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Je suis l’Éternel votre Dieu, qui vous ai fait sortir du pays d’Egypte pour devenir votre Dieu, moi, l’Éternel votre Dieu!"

< Ƙidaya 15 >