< Ƙidaya 15 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Then Yahweh spoke to Moses. He said,
2 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Bayan kun shiga ƙasar da nake ba ku a matsayin gida,
“Speak to the people of Israel and say to them, 'When you go into the land where you will live, which Yahweh will give to you,
3 kuka yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji, daga cikin shanu, ko tumaki, abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa, ko hadayu don alkawura na musamman, ko hadayar yardar rai, ko kuma hadaya ta biki,
you are to prepare an offering by fire to Yahweh, either a burnt offering or a sacrifice to fulfill a vow or a freewill offering, or an offering at your feasts, to produce a pleasing aroma for Yahweh from the herd or the flock.
4 sai shi wanda ya kawo hadayar yă miƙa wa Ubangiji hadaya ta gari mai laushi mai kyau, kashi ɗaya bisa goma na efa wanda aka kwaɓa da kwalaba ɗaya na mai.
You must offer to Yahweh a burnt offering as well as a grain offering of a tenth of an ephah of fine flour mixed with one-fourth of a hin of oil.
5 Da kowane ɗan rago don hadaya ta ƙonawa, a shirya kwalaba ɗaya na ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha.
You must also offer with the burnt offering, or for the sacrifice, one-fourth of a hin of wine for the drink offering for each lamb.
6 “‘In da rago ne za a miƙa, to, sai a shirya hadaya ta gari mai laushi, garin yă zama kashi biyu bisa goma na efa. A kwaɓa shi da kashi ɗaya bisa uku na garwan mai,
If you are offering a ram, you must prepare as a grain offering two-tenths of an ephah of fine flour mixed with a third of a hin of oil.
7 da kashi ɗaya bisa uku na garwan ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha. A miƙa ta abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
For the drink offering, you must offer a third of a hin of wine. It will produce a sweet aroma for Yahweh.
8 “‘Sa’ad da kuka shirya rago don hadaya ta ƙonawa saboda alkawari na musamman, ko hadaya ta salama ga Ubangiji,
When you prepare a bull as a burnt offering or as a sacrifice to fulfill a vow, or as a fellowship offering to Yahweh,
9 sai ku kawo hadaya ta gari tare da bijimi, kashi ɗaya bisa uku na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da rabin garwan mai.
then you must offer with the bull a grain offering of three-tenths of an ephah of fine flour mixed with half a hin of oil.
10 A kuma kawo rabin garwan ruwan inabi na hadaya ta sha. Za tă zama hadayar da aka yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
You must offer as the drink offering half a hin of wine, as an offering made by fire, to produce a sweet aroma for Yahweh.
11 Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru.
It must be done this way for each bull, for each ram, and for each of the male lambs or young goats.
12 Haka za a yi da kowannensu bisa ga abin da aka shirya.
Every sacrifice that you prepare and offer must be done as described here.
13 “‘Duk wanda yake ɗan ƙasa, ta haka ne dole zai aikata waɗannan abubuwa sa’ad da ya kawo hadaya da akan yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
All who are native-born Israelites must do these things in this way, when anyone brings an offering made by fire, to produce an aroma that is pleasing to Yahweh.
14 Idan baƙon da yake baƙunci a cikinku, ko kowane ne da yake tare da ku a dukan zamananku, yana so yă ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, dole yă yi kamar yadda kuke yi.
If a foreigner is staying with you, or whoever may live among you throughout your people's generations, he must make an offering made by fire, to produce a sweet aroma for Yahweh. He must act as you act.
15 Ƙa’ida ɗaya ce ga jama’a da kuma baƙin da suke zama a cikinku, wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a dukan tsararraki masu zuwa. Da ku, da baƙi, za ku zama ɗaya a gaban Ubangiji.
There must be the same law for the community and for the foreigner who stays with you, a permanent law throughout your people's generations. As you are, so also must be the traveler staying with you. He must act as you act before Yahweh.
16 Doka ɗaya da ƙa’ida ɗaya za a yi aiki da ita a kan ku da kuma baƙin da suke zama a cikinku.’”
The same law and decree must apply to you and to the foreigner who is staying with you.'”
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
Again Yahweh spoke to Moses. He said,
18 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da ina kai ku,
“Speak to the people of Israel and say to them, 'When you come into the land where I will take you,
19 kuka ci abincin ƙasar, ku miƙa wani sashe na amfanin ƙasar a matsayin hadaya ga Ubangiji.
when you eat the food produced in the land, you must offer an offering and present it to me.
20 Ku kawo waina daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku, ku kuma miƙa shi a matsayin hadaya daga masussuka.
From the first of your dough you must offer a loaf to raise it up as a raised offering from the threshing floor. You must raise it up in this way.
21 A duk tsararraki masu zuwa, za ku miƙa wannan hadaya daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku ga Ubangiji.
You must give to me a raised offering throughout your people's generations from the first of your dough.
22 “‘To, in ku a matsayin jama’a, da gangan kuka ƙi kiyaye waɗannan ƙa’idodi da Ubangiji ya ba wa Musa ba,
You will sometimes sin without intending to do so, when you do not obey all these commands that I have spoken to Moses—
23 ko wani daga cikin umarnan da Ubangiji ya ba ku ta wurinsa, daga ranar da Ubangiji ya ba da su, har zuwa tsararraki masu zuwa,
everything that I have commanded you through Moses from the day that I began to give you commands and onward throughout your people's generations.
24 in kuwa aka yi haka ba da gangan ba, kuma da rashin sani, sai duk jama’a su miƙa ɗan bijimi don hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, tare da ƙayyadadden hadaya ta gari, da hadaya ta sha, da kuma bunsuru na hadaya don zunubi.
In the case of unintentional sin without the community's knowledge, then all the community must offer one young bull as a burnt offering to produce a sweet aroma for Yahweh. Along with this must be made a grain offering and drink offering, as commanded by the decree, and one male goat as a sin offering.
25 Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuma gafarta musu, gama ba da gangan ba ne suka aikata, kuma sun kawo wa Ubangiji hadayar da akan yi da wuta da kuma hadaya don zunubi saboda laifinsu.
The priest must make atonement for all the community of the people of Israel. They will be forgiven because the sin was an error. They have brought their sacrifice, an offering made by fire to me. They have brought their sin offering before me for their error.
26 Za a gafarta wa dukan jama’ar Isra’ilawa, da baƙin da suke zama a cikinsu, gama duk laifin da aka yi da rashin sani, yakan shafi dukan mutane.
Then all the community of the people of Israel will be forgiven, and also the foreigners who are staying with them, because all the people committed the sin unintentionally.
27 “‘Amma in mutum ɗaya ne kaɗai ya yi laifi ba da gangan ba, dole yă kawo akuya domin hadaya don zunubi.
If a person sins unintentionally, then he must offer a female goat a year old as a sin offering.
28 Firist zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin nan da ya aikata laifi ba da gangan ba, in kuwa an yi kafara saboda shi, za a gafarta masa.
The priest must make atonement before Yahweh for the person who sins unintentionally. That person will be forgiven when atonement has been made.
29 Ƙa’ida dai za tă zama ɗaya ga duk wanda ya yi laifi ba da gangan ba, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙon da yake zama a cikinku.
You must have the same law for the one who does anything unintentionally, the same law for the one who is native born among the people of Israel and for the foreigners who are staying among them.
30 “‘Amma duk wanda ya yi zunubi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko baƙo, ya saɓi Ubangiji, dole a ware wannan mutum daga mutanensa,
But the person who does anything in defiance, whether he is native born or a foreigner, blasphemes me. That person must be cut off from among his people.
31 gama ya rena maganar Ubangiji, ya kuma karya umarninsa. Tabbatacce za a kashe wannan mutum, alhakinsa laifinsa kuwa yana wuyansa.’”
Because he has despised my word and has broken my commandment, that person must be cut off completely. His sin will be on him.'”
32 Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
While the people of Israel were in the wilderness, they found a man gathering wood on the Sabbath day.
33 Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
Those who found him brought him to Moses, Aaron, and all the community.
34 sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
They kept him in custody because it had not been declared what should be done with him.
35 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
Then Yahweh said to Moses, “The man must surely be put to death. All the community must stone him with stones outside the camp.”
36 Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
So all the community brought him outside the camp and stoned him to death as Yahweh had commanded Moses.
37 Ubangiji ya ce wa Musa,
Again Yahweh spoke to Moses. He said,
38 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘A dukan tsararraki masu zuwa, za ku sa tuntaye a gefen rigunarku, su sa zare mai ruwan shuɗi a bisan kowane tuntu.
“Speak to the descendants of Israel and command them to make for themselves tassels to hang from the borders of their garments, to hang them from each border by a blue cord. They must do this throughout their people's generations.
39 Tuntayen za su zama muku abin dubawa don ku riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji, don kada ku bi son zuciyarku, da sha’awar idanunku yadda kuka taɓa yi.
It will be a special reminder to you, when you may look at it, of all my commandments, to carry them out so that you do not look to your own heart and your own eyes and prostitute yourselves to them.
40 Sa’an nan za ku riƙa tuna, ku kuma aikata dukan umarnaina ku zama tsarkaka ga Allahnku.
Do this so that you may call to mind and obey all my commandments, and so that you may be holy, reserved for me, your God.
41 Ni ne Ubangiji Allahnku, da ya fitar da ku daga Masar, don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
I am Yahweh your God, who brought you out of the land of Egypt, to become your God. I am Yahweh your God.”