< Ƙidaya 15 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke unto Moses, saying,
2 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Bayan kun shiga ƙasar da nake ba ku a matsayin gida,
Speak unto the children of Israel and say unto them, When ye shall have come into the land of your habitations, which I give unto you,
3 kuka yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji, daga cikin shanu, ko tumaki, abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa, ko hadayu don alkawura na musamman, ko hadayar yardar rai, ko kuma hadaya ta biki,
And ye will prepare a fire-offering unto the Lord, a burnt-offering, or a sacrifice, in performing a pronounced vow, or as a freewill-offering, or on your solemn feasts, to prepare a sweet savor unto the Lord, of the herds of the flocks:
4 sai shi wanda ya kawo hadayar yă miƙa wa Ubangiji hadaya ta gari mai laushi mai kyau, kashi ɗaya bisa goma na efa wanda aka kwaɓa da kwalaba ɗaya na mai.
Then shall he that bringeth his offering unto the Lord, bring as a meat-offering a tenth part of fine flour mingled with the fourth of a hin of oil.
5 Da kowane ɗan rago don hadaya ta ƙonawa, a shirya kwalaba ɗaya na ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha.
And wine for a drink-offering, the fourth of a hin, shalt thou prepare with the burnt-offering or sacrifice, for each one sheep.
6 “‘In da rago ne za a miƙa, to, sai a shirya hadaya ta gari mai laushi, garin yă zama kashi biyu bisa goma na efa. A kwaɓa shi da kashi ɗaya bisa uku na garwan mai,
But for a ram, shalt thou prepare as a meat-offering two tenth parts of fine flour mingled with the third of a hin of oil.
7 da kashi ɗaya bisa uku na garwan ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha. A miƙa ta abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
And wine for the drink-offering, the third of a hin, shalt thou bring, for a sweet savor unto the Lord.
8 “‘Sa’ad da kuka shirya rago don hadaya ta ƙonawa saboda alkawari na musamman, ko hadaya ta salama ga Ubangiji,
And when thou preparest a bullock for a burnt-offering, or for a sacrifice, in performing a pronounced vow, or a peace-offering unto the Lord:
9 sai ku kawo hadaya ta gari tare da bijimi, kashi ɗaya bisa uku na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da rabin garwan mai.
Then shall he bring with the bullock as a meat-offering, three tenth parts of fine flour mingled with half a hin of oil.
10 A kuma kawo rabin garwan ruwan inabi na hadaya ta sha. Za tă zama hadayar da aka yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
And wine shalt thou bring for a drink-offering, half a hin, as a fire-offering of a sweet savor unto the Lord.
11 Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru.
Thus shall it be done for each one bullock, or for each one ram, or for a lamb, be it of the sheep or of the goats.
12 Haka za a yi da kowannensu bisa ga abin da aka shirya.
According to the number that ye may prepare, so shall ye do to every one according to their number.
13 “‘Duk wanda yake ɗan ƙasa, ta haka ne dole zai aikata waɗannan abubuwa sa’ad da ya kawo hadaya da akan yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
All that are born in the country shall do these things after this manner, in offering a fire-offering of a sweet savor unto the Lord.
14 Idan baƙon da yake baƙunci a cikinku, ko kowane ne da yake tare da ku a dukan zamananku, yana so yă ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, dole yă yi kamar yadda kuke yi.
And if a stranger sojourn with you, or whosoever may be among you in your generations, and will make an offering made by fire, of a sweet savor unto the Lord: as ye do, so shall he do.
15 Ƙa’ida ɗaya ce ga jama’a da kuma baƙin da suke zama a cikinku, wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a dukan tsararraki masu zuwa. Da ku, da baƙi, za ku zama ɗaya a gaban Ubangiji.
Congregation! one statute shall be for you, and for the stranger that sojourneth: a statute for ever in your generations; as ye are, so shall the stranger be before the Lord.
16 Doka ɗaya da ƙa’ida ɗaya za a yi aiki da ita a kan ku da kuma baƙin da suke zama a cikinku.’”
One law and one code shall be for you, and for the stranger that sojourneth with you.
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke unto Moses, saying,
18 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da ina kai ku,
Speak unto the children of Israel, and say unto them, When ye come into the land whither I bring you:
19 kuka ci abincin ƙasar, ku miƙa wani sashe na amfanin ƙasar a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Then shall it be, that, when ye eat of the bread of the land, ye shall set aside a heave-offering unto the Lord.
20 Ku kawo waina daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku, ku kuma miƙa shi a matsayin hadaya daga masussuka.
As the first of your doughs shall ye set aside a cake for a heave-offering; like the heave-offering of the threshing-floor, so shall ye set this aside.
21 A duk tsararraki masu zuwa, za ku miƙa wannan hadaya daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku ga Ubangiji.
Of the first of your doughs shall ye give unto the Lord a heave-offering, in your generations.
22 “‘To, in ku a matsayin jama’a, da gangan kuka ƙi kiyaye waɗannan ƙa’idodi da Ubangiji ya ba wa Musa ba,
And if ye err, and do not observe all these commandments, which the Lord hath spoken unto Moses,
23 ko wani daga cikin umarnan da Ubangiji ya ba ku ta wurinsa, daga ranar da Ubangiji ya ba da su, har zuwa tsararraki masu zuwa,
All that the Lord hath commanded you by the hand of Moses, from the day that the Lord commanded [the same] and thenceforward, among your generations:
24 in kuwa aka yi haka ba da gangan ba, kuma da rashin sani, sai duk jama’a su miƙa ɗan bijimi don hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, tare da ƙayyadadden hadaya ta gari, da hadaya ta sha, da kuma bunsuru na hadaya don zunubi.
Then shall it be, if, through inadvertence of the congregation, it was committed by ignorance, that all the congregation shall prepare one young bullock for a burnt-offering, for a sweet savor unto the Lord, with his meat-offering, and his drink-offering, according to the prescribed manner, and one he-goat for a sin-offering.
25 Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuma gafarta musu, gama ba da gangan ba ne suka aikata, kuma sun kawo wa Ubangiji hadayar da akan yi da wuta da kuma hadaya don zunubi saboda laifinsu.
And the priest shall make an atonement for all the congregation of the children of Israel, and it shall be forgiven unto them; for it is [a sin of] ignorance; and they have brought their offering, a sacrifice made by fire unto the Lord, and their sin-offering before the Lord, for their [sin of] ignorance:
26 Za a gafarta wa dukan jama’ar Isra’ilawa, da baƙin da suke zama a cikinsu, gama duk laifin da aka yi da rashin sani, yakan shafi dukan mutane.
And it shall be forgiven unto all the congregation of the children of Israel, and unto the stranger that sojourneth among them; for by all the people [was it done] in ignorance.
27 “‘Amma in mutum ɗaya ne kaɗai ya yi laifi ba da gangan ba, dole yă kawo akuya domin hadaya don zunubi.
And if any person sin through ignorance, then shall he bring a she-goat of the first year for a sin-offering.
28 Firist zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin nan da ya aikata laifi ba da gangan ba, in kuwa an yi kafara saboda shi, za a gafarta masa.
And the priest shall make an atonement for the person that hath erred, in his sinning through ignorance before the Lord; to make an atonement for him, that it may be forgiven unto him.
29 Ƙa’ida dai za tă zama ɗaya ga duk wanda ya yi laifi ba da gangan ba, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙon da yake zama a cikinku.
For the native born among the children of Israel, and for the stranger that sojourneth among them: —one law shall be for you, for him that acteth through ignorance.
30 “‘Amma duk wanda ya yi zunubi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko baƙo, ya saɓi Ubangiji, dole a ware wannan mutum daga mutanensa,
But the person that doth aught with a high hand, be he one born in the land, or a stranger, the same dishonoreth the Lord; and that person shall be cut off from among his people.
31 gama ya rena maganar Ubangiji, ya kuma karya umarninsa. Tabbatacce za a kashe wannan mutum, alhakinsa laifinsa kuwa yana wuyansa.’”
Because the word of the Lord hath he despised, and his commandment hath he broken; that person shall be cut off, his iniquity is upon him.
32 Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
And while the children of Israel were in the wilderness, they found a man gathering sticks upon the sabbath-day.
33 Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
And they that found him gathering sticks brought him for judgment unto Moses and Aaron, and unto all the congregation.
34 sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
And they put him in ward; because it had not been declared what should be done to him.
35 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
And the Lord said unto Moses, The man shall be put to death: all the congregation shall stone him with stones without the camp.
36 Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And all the congregation brought him forth to without the camp, and they stoned him with stones, and he died; as the Lord had commanded Moses.
37 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord said unto Moses, as followeth,
38 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘A dukan tsararraki masu zuwa, za ku sa tuntaye a gefen rigunarku, su sa zare mai ruwan shuɗi a bisan kowane tuntu.
Speak unto the children of Israel, and say to them, that they shall make themselves fringes on the corners of their garments throughout their generations, and that they shall put upon the fringe of the corner a thread of blue:
39 Tuntayen za su zama muku abin dubawa don ku riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji, don kada ku bi son zuciyarku, da sha’awar idanunku yadda kuka taɓa yi.
And it shall be unto you for a fringe, that ye may look upon it, and remember all the commandments of the Lord, and do them; and that ye seek not after [the inclination of] your own heart and [the delight of] your eyes, in pursuit of which ye have been led astray.
40 Sa’an nan za ku riƙa tuna, ku kuma aikata dukan umarnaina ku zama tsarkaka ga Allahnku.
In order that ye may remember, and do all my commandments, and be holy unto your God.
41 Ni ne Ubangiji Allahnku, da ya fitar da ku daga Masar, don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
I am the Lord your God, who brought you out of the land of Egypt, to be your God: I am the Lord your God.

< Ƙidaya 15 >