< Ƙidaya 14 >

1 A daren nan, sai dukan jama’ar suka tā da murya, suka yi kuka da ƙarfi.
Toda a congregação levantou sua voz, e chorou; e o povo chorou naquela noite.
2 Dukan Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, dukan taron kuwa suka ce musu, “Da ma mun mutu a Masar! Ko kuma a wannan hamada ma!
Todas as crianças de Israel murmuraram contra Moisés e contra Arão. Toda a congregação lhes disse: “Desejamos que tivéssemos morrido na terra do Egito, ou que tivéssemos morrido neste deserto!
3 Don me Ubangiji yana kawo mu wannan ƙasa yă bar mu kawai mu mutu da takobi? A kuma kwashe matanmu da’ya’yanmu ganima. Ashe, bai fi mana mu koma Masar ba?”
Por que Iavé nos traz a esta terra, para cair à espada? Nossas esposas e nossos pequenos serão capturados ou mortos! Não seria melhor para nós voltarmos ao Egito?”
4 Sai suka ce wa junansu, “Mu naɗa wa kanmu shugaba, mu koma Masar.”
Disseram um ao outro: “Vamos escolher um líder, e vamos voltar ao Egito”.
5 Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki a gaban jama’ar Isra’ilawa da suka taru a can.
Então Moisés e Arão caíram de rosto caído diante de toda a assembléia da congregação dos filhos de Israel.
6 Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne waɗanda suke tare da masu leƙo asirin ƙasar, suka yayyage tufafinsu
Josué, filho de Nun e Caleb, filho de Jephunneh, que eram dos que espiaram a terra, rasgaram suas roupas.
7 suka ce wa dukan taron Isra’ilawa, “Ƙasar da muka ratsa, muka kuma leƙi asirinta, tana da kyau sosai.
Eles falaram a toda a congregação dos filhos de Israel, dizendo: “A terra, pela qual passamos para espioná-la, é uma terra extremamente boa”.
8 In Ubangiji ya ji daɗinmu, zai kai mu ƙasan nan, ƙasar da take zub da madara da zuma, yă kuwa ba mu ita.
Se Yahweh se deleita conosco, então ele nos trará para esta terra, e nos dará: uma terra que flui com leite e mel.
9 Sai dai kada ku tayar wa Ubangiji. Kada kuma ku ji tsoron mutane ƙasar, domin za mu gama da su. Kāriyarsu ta gama, amma Ubangiji yana nan tare da mu. Kada ku ji tsoronsu.”
Somente não se revolte contra Iavé, nem tema o povo da terra; pois eles são pão para nós. Sua defesa é retirada de cima deles, e Yahweh está conosco. Não tenha medo deles”.
10 Amma taron jama’a suka ce za su jajjefe su da duwatsu. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana a Tentin Sujada ga dukan Isra’ilawa.
Mas toda a congregação ameaçou apedrejá-los com pedras. A glória de Yahweh apareceu na Tenda de Reunião para todas as crianças de Israel.
11 Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe mutanen nan za su rena ni? Har yaushe za su ƙi gaskata da ni, duk da yawan mu’ujizan da nake yi a cikinsu?
Yahweh disse a Moisés: “Quanto tempo este povo vai me desprezar? Por quanto tempo eles não acreditarão em mim, por todos os sinais que tenho trabalhado entre eles?
12 Zan buge su duka da annoba, in hallaka su, amma zan mai da kai al’umma mai girma, da kuma ƙarfi fiye da su.”
Vou atacá-los com a peste e deserdá-los, e farei de vocês uma nação maior e mais poderosa do que eles”.
13 Sai Musa ya ce wa Ubangiji, “Ai, Masarawa za su ji game da wannan! Da ikonka ka fitar da mutanen nan daga cikinsu.
Moisés disse a Iavé: “Então os egípcios o ouvirão; pois você educou este povo em seu poder de entre eles”.
14 Za su kuwa gaya wa mutanen wannan ƙasa. Sun riga sun ji cewa kai, ya Ubangiji, kana tare da waɗannan mutane, kuma cewa kai, ya Ubangiji, an gan ka fuska da fuska, cewa girgijenka ya tsaya bisansu, cewa kana tafiya a gabansu cikin ginshiƙin girgije da rana, da ginshiƙin wuta kuma da dare.
Eles o dirão aos habitantes desta terra”. Eles ouviram dizer que você, Javé, está entre este povo; pois você, Javé, é visto face a face, e sua nuvem está sobre eles, e você vai diante deles, num pilar de nuvem de dia, e num pilar de fogo de noite.
15 In ka kashe dukan mutanen nan gaba ɗaya, al’ummai da suka ji wannan labari game da kai za su ce,
Agora, se você matou este povo como um só homem, então as nações que ouviram a fama de você falarão, dizendo:
16 ‘Ubangiji ya kāsa kai waɗannan mutane a ƙasar da ya yi alkawari da rantsuwa ne, shi ya sa ya kashe su a hamada.’
'Porque Javé não foi capaz de trazer este povo para a terra que ele lhes jurou, por isso ele os matou no deserto'.
17 “Yanzu bari Ubangiji yă nuna ikonsa, kamar dai yadda ka furta.
Agora, por favor, deixai que o poder do Senhor seja grande, conforme falastes, dizendo:
18 ‘Ubangiji mai jinkiri fushi ne, mai yawan ƙauna, mai gafarta zunubi da tawaye. Duk da haka ba ya ƙyale mai laifi, babu horo. Yana horin’ya’ya saboda zunubin iyayensu har tsara ta uku, da ta huɗu.’
'Yahweh é lento na ira, e abundante na bondade amorosa, perdoando a iniqüidade e a desobediência; e ele de modo algum limpará os culpados, visitando a iniqüidade dos pais sobre os filhos, sobre a terceira e a quarta geração'.
19 Bisa ga ƙaunarka mai girma, ka gafarta zunubin mutanen nan, kamar dai yadda ka gafarta musu daga lokacin da suka bar Masar har zuwa yanzu.”
Por favor, perdoe a iniqüidade deste povo de acordo com a grandeza de sua bondade amorosa, e assim como você perdoou este povo, desde o Egito até agora”.
20 Ubangiji ya amsa ya ce, “Na gafarta musu, yadda ka roƙa.
Yahweh disse: “Perdoei de acordo com a sua palavra;
21 Duk da haka, muddin ina raye, kuma muddin ɗaukakar Ubangiji ta cika dukan duniya,
mas em toda a ação - como eu vivo, e como toda a terra será cheia da glória de Yahweh -
22 ko ɗaya daga cikinsu da suka ga ɗaukakata da mu’ujizai da na yi a Masar, da kuma a cikin hamada, da suka ƙi yin mini biyayya, suka kuma gwada ni har sau goma,
porque todos aqueles homens que viram minha glória e meus sinais, que eu trabalhei no Egito e no deserto, mas me tentaram estas dez vezes, e não escutaram minha voz;
23 ba ko ɗayansu da zai gan ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa zan ba wa kakanninsu. Ba ko ɗaya da ya rena ni, da zai taɓa ganinta.
certamente não verão a terra que eu jurei a seus pais, nem nenhum daqueles que me desprezaram a verão.
24 Amma domin Kaleb bawana ya kasance da ruhu dabam, ya kuma bi ni da zuciya ɗaya, zan kai shi cikin ƙasar da ya je, zuriyarsa kuwa za su gāje ta.
Mas meu servo Caleb, porque tinha outro espírito com ele, e me seguiu plenamente, eu o trarei para a terra para onde ele foi. Sua descendência a possuirá.
25 Da yake Amalekawa da Kan’aniyawa suna zama a kwarin, gobe sai ka koma baya, ka nufi wajen hamada ta hanyar Jan Teku.”
Since os amalequitas e os cananeus habitam no vale, amanhã viram e vão para o deserto pelo caminho do Mar Vermelho”.
26 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
Yahweh falou a Moisés e a Arão, dizendo:
27 “Har yaushe wannan muguwar al’umma za tă yi gunaguni a kaina? Na ji koke-koken waɗannan Isra’ilawa masu gunaguni.
“Por quanto tempo vou suportar esta má congregação que se queixa contra mim? Ouvi as queixas dos filhos de Israel, que se queixam contra mim.
28 Saboda haka ka gaya musu cewa, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji, zan yi muku daidai da abin da na ji kuke faɗa.
Diga-lhes: “Como eu vivo, diz Javé, certamente como vocês falaram aos meus ouvidos, assim eu farei a vocês”.
29 A cikin wannan hamadan, jikunanku za su fāɗi, kowanne a cikinku mai shekara ashirin ko fiye, wanda aka ƙirga shi cikin ƙidaya, wanda kuma ya yi gunaguni a kaina, da zai shiga wannan ƙasa.
Seus cadáveres cairão neste deserto; e todos os que foram contados de vocês, de acordo com seu número inteiro, a partir de vinte anos de idade, que reclamaram contra mim,
30 Ba ko ɗaya daga cikinku da zai shiga ƙasar da na ɗaga hannu na rantse, za tă zama gidanku, sai dai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
certamente não entrarão na terra a respeito da qual jurei que os faria habitar, exceto Calebe, filho de Jefoné, e Josué, filho de Freira.
31 Amma game da’ya’yanku da kuka ce za a kwashe ganima, zan kawo su cikin ƙasar, su ji daɗin ƙasar wadda kuka ƙi.
Mas eu trarei seus pequenos que você disse que deveriam ser capturados ou mortos, e eles conhecerão a terra que você rejeitou.
32 Amma ku, jikunanku za su fāɗi a wannan hamada.
Mas quanto a vocês, seus cadáveres cairão neste deserto.
33 ’Ya’yanku za su zama makiyaya a nan, shekaru arba’in suna shan wahala domin rashin amincinku, har sai mutum na ƙarshe a cikinku ya kwanta a hamada.
Seus filhos serão errantes no deserto durante quarenta anos, e suportarão sua prostituição, até que seus cadáveres sejam consumidos no deserto.
34 Shekaru arba’in, shekara ɗaya a madadi kwana ɗaya cikin kwanakin arba’in da kuka ɗauka kuka leƙi asirin ƙasa, za ku sha wahala saboda zunubanku, ku kuma san abin da ake nufi da sa ni in yi gāba da ku.’
Após o número de dias em que vocês espiaram a terra, mesmo quarenta dias, por cada dia do ano, vocês suportarão suas iniquidades, mesmo quarenta anos, e conhecerão minha alienação'.
35 Ni, Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata waɗannan abubuwa a kan dukan muguwar jama’an nan da suka haɗa kai, suka tayar mini. Za su sadu da ƙarshensu a wannan hamada; a nan za su mutu.”
Eu, Yahweh, falei. Certamente farei isto a toda esta congregação maligna que está reunida contra mim. Neste deserto eles serão consumidos, e ali morrerão”.
36 Saboda haka mutanen da Musa ya aika, su leƙo asirin ƙasar, waɗanda suka komo, suka sa taron jama’a su yi gunaguni a kansa saboda sun kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar,
Os homens que Moisés enviou para espionar a terra, que voltaram e fizeram toda a congregação murmurar contra ele, trazendo um relatório maligno contra a terra,
37 waɗannan mutanen da suka kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, annoba ta buge su, suka kuwa mutu a gaban Ubangiji.
mesmo aqueles homens que trouxeram um relatório maligno sobre a terra, morreram pela peste antes de Yahweh.
38 Daga cikin mutanen da suka leƙo asirin ƙasar, Yoshuwa ɗan Nun, da Kaleb ɗan Yefunne ne, kaɗai suka rayu.
Mas Josué, filho de Nun, e Calebe, filho de Jefoné, permaneceram vivos daqueles homens que foram espionar a terra.
39 Da Musa ya gaya wa dukan Isra’ilawa wannan labari, sai suka yi baƙin ciki ƙwarai.
Moisés disse estas palavras a todas as crianças de Israel, e o povo lamentou muito.
40 Kashegari da sassafe suka haura ta wajen ƙasa mai tudu suka ce, “Mun yi zunubi, za mu tafi inda Ubangiji ya yi alkawari.”
Eles se levantaram de manhã cedo e subiram ao topo da montanha, dizendo: “Eis que estamos aqui, e iremos ao lugar que Javé prometeu; pois pecamos”.
41 Amma Musa ya ce, “Don me kuke rashin biyayya da umarnin Ubangiji? Wannan ba zai yiwu ba!
Moisés disse: “Por que agora você desobedece ao mandamento de Iavé, já que ele não prosperará?
42 Kada ku haura, domin Ubangiji, ba ya tare da ku. Magabtanku za su ci nasara a kanku,
Não suba, pois Yahweh não está entre vocês; assim não será derrubado diante de seus inimigos.
43 gama Amalekawa da Kan’aniyawa za su kara da ku a can. Domin kun juya daga Ubangiji, ba zai kasance da ku ba, za a kuma karkashe ku da takobi.”
Pois ali os amalequitas e os cananeus estão diante de vocês, e vocês cairão pela espada porque voltaram a seguir a Iavé; portanto Iavé não estará com vocês”.
44 Duk da haka, suka yi tsammani ba zai zama haka ba, sai suka haura ta wajen ƙasa mai tudu, Musa da akwatin alkawarin Ubangiji dai ba su gusa daga sansanin ba.
Mas eles presumiram subir até o topo da montanha. No entanto, a arca do pacto de Iavé e Moisés não saíram do acampamento.
45 Sai Amalekawa da Kan’aniyawa mazaunan ƙasar tudu, suka gangaro suka auka musu, suka bubbuge su suka kokkore su har Horma.
Então os amalequitas desceram, e os cananeus que viviam naquela montanha, e os atingiram e bateram até mesmo em Hormah.

< Ƙidaya 14 >