< Ƙidaya 14 >
1 A daren nan, sai dukan jama’ar suka tā da murya, suka yi kuka da ƙarfi.
Ainsi toute la multitude vociférant, pleura cette nuit-là.
2 Dukan Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, dukan taron kuwa suka ce musu, “Da ma mun mutu a Masar! Ko kuma a wannan hamada ma!
Et tous les enfants d’Israël murmurèrent contre Moïse et Aaron, disant:
3 Don me Ubangiji yana kawo mu wannan ƙasa yă bar mu kawai mu mutu da takobi? A kuma kwashe matanmu da’ya’yanmu ganima. Ashe, bai fi mana mu koma Masar ba?”
Plût Dieu que nous fussions morts en Egypte! et plût à Dieu que nous périssions dans cette vaste solitude, et que le Seigneur ne nous conduise pas dans cette terre, afin que nous ne tombions point sous le glaive, et que nos femmes et nos enfants ne soient pas amenés captifs! Ne vaut-il pas mieux retourner en Egypte?
4 Sai suka ce wa junansu, “Mu naɗa wa kanmu shugaba, mu koma Masar.”
Et ils se dirent l’un à l’autre: Etablissons-nous un chef, et retournons en Egypte.
5 Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki a gaban jama’ar Isra’ilawa da suka taru a can.
Ce qu’ayant entendu. Moïse et Aaron tombèrent inclinés vers la terre devant toute la multitude des enfants d’Israël.
6 Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne waɗanda suke tare da masu leƙo asirin ƙasar, suka yayyage tufafinsu
Mais Josué, fils de Nun, et Caleb, fils de Jéphoné, qui avaient aussi eux-mêmes parcouru la terre, déchirèrent leurs vêtements,
7 suka ce wa dukan taron Isra’ilawa, “Ƙasar da muka ratsa, muka kuma leƙi asirinta, tana da kyau sosai.
Et dirent à toute la multitude des enfants d’Israël: La terre dont nous avons fait le tour est très bonne.
8 In Ubangiji ya ji daɗinmu, zai kai mu ƙasan nan, ƙasar da take zub da madara da zuma, yă kuwa ba mu ita.
Si le Seigneur est propice, il nous y conduira et nous donnera ce sol où coulent du lait et du miel.
9 Sai dai kada ku tayar wa Ubangiji. Kada kuma ku ji tsoron mutane ƙasar, domin za mu gama da su. Kāriyarsu ta gama, amma Ubangiji yana nan tare da mu. Kada ku ji tsoronsu.”
Ne soyez point rebelles contre le Seigneur, et ne craignez point le peuple de cette terre, parce que nous pouvons les dévorer comme du pain: tout secours les a abandonnés: le Seigneur est avec nous; ne craignez point.
10 Amma taron jama’a suka ce za su jajjefe su da duwatsu. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana a Tentin Sujada ga dukan Isra’ilawa.
Et, comme toute la multitude criait et voulait les lapider, la gloire du Seigneur apparut sur le toit d’alliance à tous les enfants d’Israël.
11 Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe mutanen nan za su rena ni? Har yaushe za su ƙi gaskata da ni, duk da yawan mu’ujizan da nake yi a cikinsu?
Et le Seigneur dit à Moïse: Jusqu’à quand ce peuple m’outragera-t-il? Jusqu’à quand ne me croiront-ils pas, après tous les miracles que j’ai faits devant eux?
12 Zan buge su duka da annoba, in hallaka su, amma zan mai da kai al’umma mai girma, da kuma ƙarfi fiye da su.”
Je les frapperai donc de la peste, et je les détruirai entièrement: et pour toi, je te ferai prince sur une nation grande, et plus forte que n’est celle-ci.
13 Sai Musa ya ce wa Ubangiji, “Ai, Masarawa za su ji game da wannan! Da ikonka ka fitar da mutanen nan daga cikinsu.
Et Moïse répondit au Seigneur: C’est donc pour que les Egyptiens du milieu desquels vous avez retiré ce peuple, apprennent, eux
14 Za su kuwa gaya wa mutanen wannan ƙasa. Sun riga sun ji cewa kai, ya Ubangiji, kana tare da waɗannan mutane, kuma cewa kai, ya Ubangiji, an gan ka fuska da fuska, cewa girgijenka ya tsaya bisansu, cewa kana tafiya a gabansu cikin ginshiƙin girgije da rana, da ginshiƙin wuta kuma da dare.
Et les habitants de cette terre (qui ont ouï dire que vous, Seigneur, vous êtes au milieu de ce peuple, que vous y êtes vu face à face, que votre nuée les couvre, que vous les précédez dans une colonne de nuée pendant le jour, et dans une colonne de feu pendant la nuit),
15 In ka kashe dukan mutanen nan gaba ɗaya, al’ummai da suka ji wannan labari game da kai za su ce,
Que vous avez fait mourir une si grande multitude comme un seul homme, et qu’ils disent:
16 ‘Ubangiji ya kāsa kai waɗannan mutane a ƙasar da ya yi alkawari da rantsuwa ne, shi ya sa ya kashe su a hamada.’
Il ne pouvait pas introduire ce peuple dans la terre au sujet de laquelle il avait juré. C’est pourquoi il les a fait mourir dans le désert.
17 “Yanzu bari Ubangiji yă nuna ikonsa, kamar dai yadda ka furta.
Que la force du Seigneur soit donc glorifiée, comme vous l’avez juré, disant:
18 ‘Ubangiji mai jinkiri fushi ne, mai yawan ƙauna, mai gafarta zunubi da tawaye. Duk da haka ba ya ƙyale mai laifi, babu horo. Yana horin’ya’ya saboda zunubin iyayensu har tsara ta uku, da ta huɗu.’
Le Seigneur est patient et d’une abondante miséricorde, effaçant l’iniquité et les crimes, et ne délaissant aucun innocent; vous qui visitez les péchés des pères dans les fils jusqu’à la troisième et quatrième génération,
19 Bisa ga ƙaunarka mai girma, ka gafarta zunubin mutanen nan, kamar dai yadda ka gafarta musu daga lokacin da suka bar Masar har zuwa yanzu.”
Remettez, je vous conjure, le péché de ce peuple, selon la grandeur de votre miséricorde, comme vous leur avez été propice depuis qu’ils sortirent de l’Egypte jusqu’en ce lieu.
20 Ubangiji ya amsa ya ce, “Na gafarta musu, yadda ka roƙa.
Et le Seigneur reprit: Je l’ai remis selon ta parole.
21 Duk da haka, muddin ina raye, kuma muddin ɗaukakar Ubangiji ta cika dukan duniya,
Je vis, moi: et toute la terre sera remplie de la gloire du Seigneur.
22 ko ɗaya daga cikinsu da suka ga ɗaukakata da mu’ujizai da na yi a Masar, da kuma a cikin hamada, da suka ƙi yin mini biyayya, suka kuma gwada ni har sau goma,
Mais cependant tous les hommes qui ont vu ma majesté et les miracles que j’ai faits en Egypte et dans le désert, qui m’ont déjà tenté par dix fois, et n’ont pas obéi à ma voix,
23 ba ko ɗayansu da zai gan ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa zan ba wa kakanninsu. Ba ko ɗaya da ya rena ni, da zai taɓa ganinta.
Ne verront pas la terre au sujet de laquelle j’ai juré à leurs pères, et qui que ce soit d’entre eux qui m’a outragé ne la verra pas.
24 Amma domin Kaleb bawana ya kasance da ruhu dabam, ya kuma bi ni da zuciya ɗaya, zan kai shi cikin ƙasar da ya je, zuriyarsa kuwa za su gāje ta.
Quant à mon serviteur Caleb, qui, plein d’un autre esprit, m’a suivi, je l’introduirai dans cette terre dont il a fait le tour; et sa postérité la possédera.
25 Da yake Amalekawa da Kan’aniyawa suna zama a kwarin, gobe sai ka koma baya, ka nufi wajen hamada ta hanyar Jan Teku.”
Parce que l’Amalécite et le Chananéen habitent dans les vallées, demain levez le camp et retournez au désert par le chemin de la mer Rouge.
26 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
Le Seigneur parla encore à Moïse et à Aaron, disant:
27 “Har yaushe wannan muguwar al’umma za tă yi gunaguni a kaina? Na ji koke-koken waɗannan Isra’ilawa masu gunaguni.
Jusqu’à quand cette multitude très méchante murmurera-t-elle contre moi? j’ai ouï les plaintes des enfants d’Israël.
28 Saboda haka ka gaya musu cewa, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji, zan yi muku daidai da abin da na ji kuke faɗa.
Dis leur donc: Je vis, moi, dit le Seigneur: Comme vous avez parlé, moi l’entendant, ainsi je vous ferai.
29 A cikin wannan hamadan, jikunanku za su fāɗi, kowanne a cikinku mai shekara ashirin ko fiye, wanda aka ƙirga shi cikin ƙidaya, wanda kuma ya yi gunaguni a kaina, da zai shiga wannan ƙasa.
C’est dans cette solitude que gésiront vos cadavres. Vous tous qui avez été dénombrés depuis vingt ans et au-dessus, et qui avez murmuré contre moi,
30 Ba ko ɗaya daga cikinku da zai shiga ƙasar da na ɗaga hannu na rantse, za tă zama gidanku, sai dai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
Vous n’entrerez point dans la terre sur laquelle j’ai levé ma main, que je vous la ferais habiter, excepté Caleb, fils de Jéphoné et Josué, fils de Nun.
31 Amma game da’ya’yanku da kuka ce za a kwashe ganima, zan kawo su cikin ƙasar, su ji daɗin ƙasar wadda kuka ƙi.
Mais vos petits-enfants dont vous avez dit qu’ils seraient en proie aux ennemis, je les y introduirai, afin qu’ils voient la terre qui vous a déplu.
32 Amma ku, jikunanku za su fāɗi a wannan hamada.
Vos cadavres gésiront dans cette solitude.
33 ’Ya’yanku za su zama makiyaya a nan, shekaru arba’in suna shan wahala domin rashin amincinku, har sai mutum na ƙarshe a cikinku ya kwanta a hamada.
Vos enfants seront errants dans le désert pendant quarante ans, ils porteront votre fornication, jusqu’à ce que soient consumés les cadavres de leurs pères dans le désert,
34 Shekaru arba’in, shekara ɗaya a madadi kwana ɗaya cikin kwanakin arba’in da kuka ɗauka kuka leƙi asirin ƙasa, za ku sha wahala saboda zunubanku, ku kuma san abin da ake nufi da sa ni in yi gāba da ku.’
Selon le nombre des quarante jours pendant lesquels vous avez considéré la terre: un an sera compté pour un jour. Et pendant quarante ans vous recevrez la peine de vos iniquités, et vous saurez ma vengeance;
35 Ni, Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata waɗannan abubuwa a kan dukan muguwar jama’an nan da suka haɗa kai, suka tayar mini. Za su sadu da ƙarshensu a wannan hamada; a nan za su mutu.”
Parce que, comme j’ai parlé, ainsi je ferai à toute cette multitude très méchante, qui s’est élevée contre moi: elle défaillira dans cette solitude et elle mourra.
36 Saboda haka mutanen da Musa ya aika, su leƙo asirin ƙasar, waɗanda suka komo, suka sa taron jama’a su yi gunaguni a kansa saboda sun kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar,
Ainsi, tous les hommes qu’avait envoyés Moïse pour considérer la terre et qui, revenus, avaient fait murmurer contre lui toute la multitude, décriant la terre comme si elle était mauvaise,
37 waɗannan mutanen da suka kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, annoba ta buge su, suka kuwa mutu a gaban Ubangiji.
Moururent, ayant été frappés en la présence du Seigneur.
38 Daga cikin mutanen da suka leƙo asirin ƙasar, Yoshuwa ɗan Nun, da Kaleb ɗan Yefunne ne, kaɗai suka rayu.
Mais Josué, fils de Nun, et Caleb, fils de Jéphoné, vécurent seuls de tous ceux qui étaient allés pour considérer la terre.
39 Da Musa ya gaya wa dukan Isra’ilawa wannan labari, sai suka yi baƙin ciki ƙwarai.
Or Moïse dit toutes ces paroles à tous les enfants d’Israël, et le peuple se lamenta beaucoup.
40 Kashegari da sassafe suka haura ta wajen ƙasa mai tudu suka ce, “Mun yi zunubi, za mu tafi inda Ubangiji ya yi alkawari.”
Et voilà que, se levant de grand matin, ils montèrent sur le sommet de la montagne, et dirent: Nous sommes prêts à monter au lieu dont le Seigneur a parlé, parce que nous avons péché.
41 Amma Musa ya ce, “Don me kuke rashin biyayya da umarnin Ubangiji? Wannan ba zai yiwu ba!
Pourquoi, leur dit Moïse, transgressez-vous la parole du Seigneur, ce qui ne vous tournera pas à bien?
42 Kada ku haura, domin Ubangiji, ba ya tare da ku. Magabtanku za su ci nasara a kanku,
Ne montez point (car le Seigneur n’est point avec vous), de peur que vous ne succombiez devant vos ennemis.
43 gama Amalekawa da Kan’aniyawa za su kara da ku a can. Domin kun juya daga Ubangiji, ba zai kasance da ku ba, za a kuma karkashe ku da takobi.”
L’Amalécite et le Chananéen sont devant vous; vous succomberez sous leur glaive, parce que vous n’avez pas voulu obéir au Seigneur, et le Seigneur ne sera pas avec vous.
44 Duk da haka, suka yi tsammani ba zai zama haka ba, sai suka haura ta wajen ƙasa mai tudu, Musa da akwatin alkawarin Ubangiji dai ba su gusa daga sansanin ba.
Mais eux, couverts de ténèbres, montèrent sur le sommet de la montagne. Mais l’arche d’alliance du Seigneur et Moïse ne sortirent point du camp.
45 Sai Amalekawa da Kan’aniyawa mazaunan ƙasar tudu, suka gangaro suka auka musu, suka bubbuge su suka kokkore su har Horma.
Alors descendirent l’Amalécite et le Chananéen, qui habitaient sur la montagne, et les frappant et les taillant en pièces, ils les poursuivirent jusqu’à Horma.