< Ƙidaya 13 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talte til Moses og sa:
2 “Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
Send avsted menn for å utspeide Kana'ans land, som jeg nu vil gi Israels barn! En mann for hver fedrenestamme skal I sende; hver av dem skal være en høvding blandt folket.
3 Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
Da sendte Moses dem fra ørkenen Paran efter Herrens ord; alle var de overhoder for Israels barn.
4 Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
Og dette var deres navn: For Rubens stamme Sammua, Sakkurs sønn,
5 Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
for Simeons stamme Safat, Horis sønn,
6 Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
for Juda stamme Kaleb, Jefunnes sønn,
7 Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
for Issakars stamme Jigeal, Josefs sønn,
8 Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
for Efra'ims stamme Hosea, Nuns sønn,
9 daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
for Benjamins stamme Palti, Rafus sønn,
10 Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
for Sebulons stamme Gaddiel, Sodis sønn,
11 Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
for Josefs stamme, for Manasse stamme Gaddi, Susis sønn,
12 Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
for Dans stamme Ammiel, Gemallis sønn,
13 Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
for Asers stamme Setur, Mikaels sønn,
14 Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
for Naftali stamme Nahbi, Vofsis sønn,
15 Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
for Gads stamme Ge'uel, Makis sønn.
16 Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
Dette var navnene på de menn som Moses sendte for å utspeide landet; men Moses gav Hosea, Nuns sønn, navnet Josva.
17 Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
Og Moses sendte dem for å utspeide Kana'ans land, og han sa til dem: Dra op her til sydlandet og stig op i fjellene
18 Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
og se hvordan landet er, og om folket som bor der, er sterkt eller svakt, om det er lite eller stort,
19 Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
og hvordan det land er som det bor i, om det er godt eller dårlig, og hvordan de byer er som det bor i, om det bor i leire eller i festninger,
20 Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
og hvordan jorden er, om den er fet eller mager, om det er trær der eller ikke! Vær ved godt mot og ta med eder av landets frukt! Det var nettop på den tid de første druer blev modne.
21 Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
Så drog de da op og utspeidet landet fra ørkenen Sin til Rehob, bortimot Hamat.
22 Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
De drog op til sydlandet og kom til Hebron; der bodde Akiman, Sesai og Talmai, Anaks barn - Hebron var bygget syv år før Soan i Egypten.
23 Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
Så kom de til Eskol-dalen; der skar de av en vinranke med en drueklase, og den bar to mann mellem sig på en stang; likeledes tok de granatepler og fikener.
24 Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
Dette sted blev kalt Eskol-dalen efter den drueklase som Israels barn skar av der.
25 A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
Da firti dager var til ende, vendte de tilbake efter å ha utspeidet landet.
26 Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
De gikk avsted og fant Moses og Aron og hele Israels barns menighet i ørkenen Paran, i Kades, og gav dem og hele menigheten beskjed om hvad de hadde sett, og viste dem landets frukt.
27 Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
De fortalte ham og sa: Vi kom til det land du sendte oss til, og det flyter virkelig med melk og honning, og her er dets frukt.
28 Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
Men det folk som bor i landet, er sterkt, og byene er som festninger og meget store; der så vi også Anaks barn.
29 Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
Amalekittene bor i sydlandet, og hetittene og jebusittene og amorittene bor i fjellbygdene, og kana'anittene bor ute ved havet og langsmed Jordan.
30 Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
Men da folket knurret mot Moses, søkte Kaleb å stagge dem og sa: Vi vil dra op og ta landet i eie; vi skal nok få det i vår makt.
31 Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
Men de menn som hadde vært med ham der op, sa: Vi makter ikke å dra op mot det folk; for det er sterkere enn vi.
32 Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
Og de talte ille blandt Israels barn om det land de hadde utspeidet, og sa: Det land vi drog igjennem for å utspeide det, er et land som fortærer sine innbyggere, og alle de vi så der, var høivoksne folk;
33 Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”
der så vi kjempene, Anaks barn av kjempeætten, og mot dem var vi i våre egne øine som gresshopper, og det syntes også de at vi var.

< Ƙidaya 13 >