< Ƙidaya 13 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
INkosi yasikhuluma kuMozisi isithi:
2 “Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
Zithumele amadoda ukuthi ahlole ilizwe leKhanani engibapha lona abantwana bakoIsrayeli; uthume indoda eyodwa yaleso lalesosizwe saboyise, yonke eyinduna phakathi kwabo.
3 Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
UMozisi wawathuma-ke esuka enkangala yeParani, ngokomlayo weNkosi; wonke lawomadoda ayezinhloko zabantwana bakoIsrayeli.
4 Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
Lala ngamabizo awo; owesizwe sakoRubeni, uShamuwa indodana kaZakuri.
5 Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
Owesizwe sakoSimeyoni, uShafati indodana kaHori.
6 Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
Owesizwe sakoJuda, uKalebi indodana kaJefune.
7 Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
Owesizwe sakoIsakari, uIgali indodana kaJosefa.
8 Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
Owesizwe sakoEfrayimi, uHoseya indodana kaNuni.
9 daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
Owesizwe sakoBhenjamini, uPaliti indodana kaRafu.
10 Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
Owesizwe sakoZebuluni, uGadiyeli indodana kaSodi.
11 Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
Owesizwe sakoJosefa, owesizwe sakoManase, uGadi indodana kaSusi.
12 Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
Owesizwe sakoDani, uAmiyeli indodana kaGemali.
13 Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
Owesizwe sakoAsheri, uSethuri indodana kaMikayeli.
14 Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
Owesizwe sakoNafithali, uNabi indodana kaVofisi.
15 Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
Owesizwe sakoGadi, uGewuweli indodana kaMaki.
16 Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
La ngamabizo amadoda uMozisi awathumayo ukuhlola ilizwe. UMozisi wasembiza uHoseya indodana kaNuni ngokuthi nguJoshuwa.
17 Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
UMozisi wasewathuma ukuhlola ilizwe leKhanani, wathi kuwo: Yenyukani lapha liye eningizimu, lenyukele entabeni,
18 Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
libone ilizwe ukuthi linjani, labantu abakhileyo kulo ukuthi balamandla kumbe babuthakathaka, balutshwana kumbe banengi yini,
19 Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
lokuthi linjani ilizwe abahlala kulo, loba lihle loba libi, lokuthi injani imizi abahlala kiyo, loba izinkamba loba izinqaba,
20 Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
lokuthi ilizwe linjani, loba livundile loba lilugwadule, lokuthi lilezihlahla loba hayi. Manini isibindi, lithathe okwesithelo selizwe. Lalesisikhathi kwakuyisikhathi sezithelo zokuqala zevini.
21 Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
Basebesenyuka, balihlola ilizwe kusukela enkangala yeZini kuze kube seRehobi, ekungeneni eHamathi.
22 Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
Benyuka-ke ngeningizimu bafika eHebroni, lapho kwakulaboAhimani, uSheshayi, loTalimayi, abantwana bakaAnaki. IHebroni lakhiwa-ke iminyaka eyisikhombisa kungakabi leZowani eGibhithe.
23 Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
Basebefika esihotsheni seEshikoli; baquma khona ugatsha olulehlukuzo elilodwa lezithelo zevini, baluthwalisana ngesigodo ngababili, lokwamapomegranati lokwemikhiwa.
24 Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
Leyondawo kwathiwa yisihotsha seEshikoli, ngenxa yehlukuzo abantwana bakoIsrayeli abaliqumayo lapho.
25 A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
Basebebuya bevela ekuhloleni ilizwe ekupheleni kwensuku ezingamatshumi amane.
26 Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
Basebehamba bafika kuMozisi lakuAroni lakunhlangano yonke yabantwana bakoIsrayeli enkangala yeParani, eKadeshi; basebebuyisela umbiko kubo lakunhlangano yonke, basebebatshengisa isithelo selizwe.
27 Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
Basebembikela bathi: Safika elizweni owasithuma kulo; njalo ngeqiniso, ligeleza uchago loluju; lalesi yisithelo salo.
28 Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
Kodwa-ke abantu abahlala elizweni balamandla, lemizi ibiyelwe ngemithangala, mikhulu kakhulu; njalo-ke sibone khona inzalo kaAnaki.
29 Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
AmaAmaleki akhile elizweni leningizimu; lamaHethi lamaJebusi lamaAmori akhile entabeni; lamaKhanani akhile elwandle leceleni kweJordani.
30 Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
UKalebi wasethulisa abantu phambi kukaMozisi, wathi: Asenyukeni lokwenyuka, sidle ilifa lalo, ngoba silamandla okulinqoba.
31 Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
Kodwa amadoda ayenyuke laye athi: Kasilamandla okwenyukela kulabobantu, ngoba balamandla kulathi.
32 Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
Basebeveza umbiko omubi ngelizwe ababelihlolile ebantwaneni bakoIsrayeli besithi: Ilizwe esidabule kulo ukulihlola yilizwe elidla abantu abahlala kulo; labantu bonke esababona phakathi kwalo bangamadoda amade kakhulu.
33 Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”
Lalapho sibone iziqhwaga, amadodana kaAnaki, avela eziqhwageni. Lemehlweni ethu sasinjengentethe, sasinjalo lemehlweni azo.

< Ƙidaya 13 >