< Ƙidaya 13 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Et là, le Seigneur parla à Moïse, disant:
2 “Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
Envoie d’entre les princes, un par chaque tribu, des hommes, qui considèrent la terre de Chanaan que je dois donner aux enfants d’Israël.
3 Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
Moïse fit ce que le Seigneur avait commandé, envoyant du désert de Pharan des hommes d’entre les princes dont voici les noms:
4 Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
De la tribu de Ruben, Sammua, fils de Zéchur;
5 Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
De la tribu de Siméon, Saphat, fils d’Huri;
6 Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
De la tribu de Juda, Caleb, fils de Jéphoné;
7 Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
Delà tribu d’Issachar, Igal, fils de Joseph;
8 Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
De la tribu d’Ephraïm, Osée, fils de Nun;
9 daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
De la tribu de Benjamin, Phalti, fils de Raphu;
10 Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
De la tribu de Zabulon, Geddiel, fils de Sodi;
11 Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
De la tribu de Joseph, du sceptre de Manassé, Gaddi, fils de Susi;
12 Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
De la tribu de Dan, Ammiel, fils de Gémalli;
13 Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
De la tribu d’Aser, Sthur, fils de Michaël;
14 Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
De la tribu de Nephthali, Nahabi, fils de Vapsi;
15 Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
De la tribu de Gad, Guel, fils de Machi.
16 Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
Ce sont là les noms des hommes qu’envoya Moïse, pour considérer la terre; et il donna à Osée, fils de Nun, le nom de Josué.
17 Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
Moïse les envoya donc pour considérer la terre de Chanaan, et il leur dit: Montez par le côté méridional. Or, lorsque vous serez arrivés aux montagnes,
18 Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
Considérez la terre, ce qu’elle est, et le peuple qui l’habite, s’il est fort ou faible, s’il est en petit nombre, ou nombreux;
19 Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
Si la terre elle-même est bonne ou mauvaise, ce que sont les villes, si elles sont murées ou sans murs.
20 Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
Si le sol est gras ou stérile, bien boisé ou sans arbres. Fortifiez-vous, et apportez-nous des fruits de la terre. Or, c’était le temps auquel les raisins précoces peuvent être mangés.
21 Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
Lors donc qu’ils furent montés, ils explorèrent la terre depuis le désert de Sin, jusqu’à Rohob, en entrant à Emath.
22 Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
Et ils montèrent vers le midi, et ils vinrent à Hébron, où étaient Achiman, Sisaï et Tholmaï, les fils d’Enac; car Hébron fut fondée sept ans avant Tanim, ville d’Egypte.
23 Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
Et avançant jusqu’au Torrent de la grappe de raisin, ils coupèrent une branche de vigne avec son raisin, que deux hommes portèrent sur un levier. Ils portèrent aussi des grenades et des figues de ce lieu,
24 Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
Qui fut appelé Néhélescol, c’est-à-dire, le Torrent de la grappe de raisin, parce que les enfants d’Israël avaient emporté de là une grappe de raisin.
25 A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
Or, les explorateurs de la terre, étant retournés après quarante jours, toute la contrée parcourue,
26 Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
Vinrent vers Moïse, Aaron et toute l’assemblée des enfants d’Israël dans le désert de Pharan qui est en Cadès; et leur ayant parlé ainsi qu’à toute la multitude, ils montrèrent les fruits de la terre;
27 Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
Et ils racontèrent, disant: Nous sommes allés dans la terre vers laquelle vous nous avez envoyés, où coulent, en effet, du lait et du miel, comme on peut le connaître par ces fruits;
28 Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
Mais elle a des habitants très forts, et des villes grandes et murées. Nous avons vu là la race d’Enac.
29 Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
Amalec habite au midi, l’Héthéen, le Jébuséen et l’Amorrhéen dans les montagnes; mais le Chananéen demeure le long de la mer, et près des courants du Jourdain.
30 Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
Cependant Caleb, pour apaiser le murmure du peuple, qui s’élevait contre Moïse, dit: Montons, et possédons la terre, parce que nous pouvons nous en emparer.
31 Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
Mais les autres qui avaient été avec lui, disaient: Nous ne pouvons nullement monter vers ce peuple, parce qu’il est plus fort que nous.
32 Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
Et ils décrièrent, parmi les enfants d’Israël, la terre qu’ils avaient examinée, disant: La terre que nous avons parcourue dévore ses habitants: le peuple que nous avons considéré est d’une haute stature.
33 Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”
Là nous avons vu certains monstres des enfants d’Enac, de la race gigantesque: comparés à eux, nous paraissions comme des sauterelles.

< Ƙidaya 13 >