< Ƙidaya 13 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Et l'Éternel parla à Moïse, en disant:
2 “Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
Envoie des hommes pour explorer le pays de Canaan, que je donne aux enfants d'Israël. Vous enverrez un homme pour chacune des tribus de leurs pères, tous des principaux d'entre eux.
3 Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
Moïse les envoya donc du désert de Paran, selon le commandement de l'Éternel; tous ces hommes étaient chefs des enfants d'Israël.
4 Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
Et voici leurs noms: Pour la tribu de Ruben, Shammua, fils de Zaccur;
5 Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
Pour la tribu de Siméon, Shaphath, fils de Hori;
6 Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
Pour la tribu de Juda, Caleb, fils de Jephunné;
7 Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
Pour la tribu d'Issacar, Jigal, fils de Joseph;
8 Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
Pour la tribu d'Éphraïm, Hosée, fils de Nun;
9 daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
Pour la tribu de Benjamin, Palthi, fils de Raphu;
10 Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
Pour la tribu de Zabulon, Gaddiel, fils de Sodi;
11 Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
Pour la tribu de Joseph, c'est-à-dire, pour la tribu de Manassé, Gaddi, fils de Susi;
12 Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
Pour la tribu de Dan, Ammiel, fils de Guemalli;
13 Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
Pour la tribu d'Asser, Sethur, fils de Micaël;
14 Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
Pour la tribu de Nephthali, Nachbi, fils de Vophsi;
15 Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
Pour la tribu de Gad, Gueuel, fils de Maki.
16 Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
Tels sont les noms des hommes que Moïse envoya pour explorer le pays. Or Moïse nomma Hosée, fils de Nun, Josué.
17 Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
Moïse les envoya donc pour explorer le pays de Canaan, et il leur dit: Montez ici par le Midi, et vous monterez sur la montagne,
18 Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
Et vous verrez le pays, quel il est, le peuple qui y habite, s'il est fort ou faible, s'il est en petit ou en grand nombre;
19 Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
Et ce qu'est le pays où il habite, s'il est bon ou mauvais; ce que sont les villes dans lesquelles il habite, si c'est dans des camps ou dans des forteresses;
20 Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
Ce qu'est la terre, si elle est grasse ou maigre; s'il y a des arbres ou non. Et ayez bon courage, et prenez du fruit du pays. C'était alors le temps des premiers raisins.
21 Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
Ils montèrent donc et explorèrent le pays, depuis le désert de Tsin jusqu'à Rehob, en allant vers Hamath.
22 Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
Ils montèrent par le Midi, et vinrent jusqu'à Hébron, où étaient Ahiman, Sheshaï, et Talmaï, enfants d'Anak. Or Hébron avait été bâtie sept ans avant Tsoan d'Égypte.
23 Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
Et ils vinrent jusqu'au torrent d'Eshcol, et y coupèrent un sarment avec une grappe de raisins, et ils la portèrent à deux avec une perche, ainsi que des grenades et des figues.
24 Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
On appela ce lieu Torrent d'Eshcol (Torrent de la grappe), à cause de la grappe que les enfants d'Israël y coupèrent.
25 A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
Or ils revinrent d'explorer le pays au bout de quarante jours.
26 Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
Et étant arrivés, ils vinrent vers Moïse et vers Aaron, et vers toute l'assemblée des enfants d'Israël, au désert de Paran, à Kadès, et ils leur rendirent compte, ainsi qu'à toute l'assemblée, et leur montrèrent du fruit du pays.
27 Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
Ils lui firent donc leur rapport, et dirent: Nous sommes allés au pays où tu nous avais envoyés; et vraiment c'est un pays où coulent le lait et le miel, et voici de son fruit.
28 Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
Seulement le peuple qui habite dans ce pays est robuste, et les villes sont closes et très grandes; nous y avons vu aussi des enfants d'Anak.
29 Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
Les Amalécites habitent la contrée du Midi; et les Héthiens, les Jébusiens et les Amoréens habitent dans la montagne; et les Cananéens habitent près de la mer et le long du Jourdain.
30 Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
Alors Caleb fit taire le peuple devant Moïse, et dit: Montons, et emparons-nous-en; car nous pouvons les vaincre.
31 Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
Mais les hommes qui étaient montés avec lui, dirent: Nous ne pourrons monter contre ce peuple, car il est plus fort que nous.
32 Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
Et ils décrièrent devant les enfants d'Israël le pays qu'ils avaient exploré, en disant: Le pays que nous avons parcouru pour l'explorer, est un pays qui dévore ses habitants, et tous ceux que nous y avons vus, sont des gens de haute stature.
33 Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”
Et nous y avons vu les géants, enfants d'Anak, de la race des géants; et nous étions à nos yeux comme des sauterelles, et nous l'étions aussi à leurs yeux.

< Ƙidaya 13 >