< Ƙidaya 13 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And there, the Lord spoke to Moses, saying:
2 “Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
“Send men, who may examine the land of Canaan, which I will give to the sons of Israel, one from the rulers of each tribe.”
3 Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
Moses did what the Lord had commanded, sending, from the desert of Paran, leading men, whose names are these:
4 Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
from the tribe of Ruben, Shammua the son of Zaccur;
5 Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
from the tribe of Simeon, Shaphat the son of Hori;
6 Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
from the tribe of Judah, Caleb the son of Jephunneh;
7 Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
from the tribe of Issachar, Igal the son of Joseph;
8 Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
from the tribe of Ephraim, Hosea the son of Nun;
9 daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
from the tribe of Benjamin, Palti the son of Raphu;
10 Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
from the tribe of Zebulon, Gaddiel the son of Sodi;
11 Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
from the tribe of Joseph, of the scepter of Manasseh, Gaddi the son of Susi;
12 Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
from the tribe of Dan, Ammiel the son of Gemalli;
13 Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
from the tribe of Asher, Sethur the son of Michael;
14 Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
from the tribe of Naphtali, Nahbi the son of Vophsi;
15 Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
from the tribe of Gad, Guel the son of Machi.
16 Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
These are the names of the men, whom Moses sent to examine the land. And he called Hosea, the son of Nun, Joshua.
17 Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
And so, Moses sent them to examine the land of Canaan, and he said to them: “Ascend by the south side. And when you arrive at the mountains,
18 Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
consider the land, as to what kind it may be, and the people, who are its inhabitants, whether they may be strong or weak, whether they may be few in number or many,
19 Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
and the land itself, whether it is good or bad, what kind of cities, walled or without walls,
20 Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
the soil, rich or barren, forested or without trees. Be strong, and bring us some of the fruits of the land.” Now it was the time when the first ripe grapes were ready to be eaten.
21 Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
And when they had ascended, they explored the land from the desert of Sin, all the way to Rehob, as one enters into Hamath.
22 Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
And they ascended by the south side. And they arrived at Hebron, where there were Ahiman and Shishai and Talmai, the sons of Anak. For Hebron was founded seven years before Tanis, the city of Egypt.
23 Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
And continuing on as far as the Torrent of the Cluster of Grapes, they cut off a vine with its grapes, which two men carried on a board. Likewise, they took from the pomegranates and the figs of that place,
24 Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
which was called Nehel Eshcol, that is, the Torrent of the Cluster of Grapes, because the sons of Israel had carried a cluster of grapes from there.
25 A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
And those exploring the land returned after forty days, having circulated through the entire region.
26 Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
And they went to Moses and Aaron, and to the entire assembly of the sons of Israel in the desert of Paran, which is in Kadesh. And speaking to them, and to the entire multitude, they showed them the fruits of the land.
27 Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
And they explained, saying: “We went into the land, to which you sent us, which, it is true, flows with milk and honey, as one can know by these fruits.
28 Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
But it has very strong occupants, and the cities are great and also walled. We saw the race of Anak there.
29 Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
Amalek lives in the south. The Hethite, and the Jebusite, and the Amorite live in the mountains. And truly, the Canaanite stays near the sea and around the streams of the Jordan.”
30 Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
During these events, Caleb, to restrain the murmuring of the people who rose up against Moses, said, “Let us ascend and possess the land, for we will be able to obtain it.”
31 Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
Yet truly, the others, who had been with him, were saying, “By no means are we able to ascend to this people, because they are stronger than we are.”
32 Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
And before the sons of Israel they disparaged the land, which they had inspected, saying: “The land, which we viewed, devours its inhabitants. The people, upon whom we gazed, were of lofty stature.
33 Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”
There, we saw some monsters among the sons of Anak, of the race of giants; by comparison with them, we seemed like locusts.”

< Ƙidaya 13 >