< Ƙidaya 12 >

1 Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
Miriam e Arão falaram contra Moisés por causa da mulher cuchita com quem ele havia casado; pois ele havia casado com uma mulher cuchita.
2 Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
Eles disseram: “Será que Yahweh realmente falou somente com Moisés? Ele não falou também conosco?”. E Yahweh ouviu.
3 (Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
Agora o homem Moisés era muito humilde, mais do que todos os homens que estavam na superfície da terra.
4 Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
Yahweh falou subitamente a Moisés, a Arão e a Miriam: “Vocês três venham para a Tenda da Reunião”! Os três saíram.
5 Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
Yahweh desceu em uma coluna de nuvem, e ficou na porta da Tenda, e chamou Aaron e Miriam; e ambos se apresentaram.
6 sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
Ele disse: “Agora ouçam minhas palavras. Se houver um profeta entre vocês, eu, Yahweh, me farei conhecer a ele numa visão. Falarei com ele em um sonho.
7 Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
Meu servo Moisés não é assim. Ele é fiel em toda a minha casa.
8 Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
Com ele, falarei boca a boca, mesmo claramente, e não por enigmas; e ele verá a forma de Javé. Por que então não teve medo de falar contra meu servo, contra Moisés”?
9 Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
A raiva de Javé queimou contra eles; e ele partiu.
10 Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
A nuvem partiu de cima da Tenda; e eis que Miriam era leprosa, tão branca como a neve. Aaron olhou para Miriam, e eis que ela era leprosa.
11 sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
Arão disse a Moisés: “Oh, meu senhor, por favor não conte este pecado contra nós, no qual fizemos tolices, e no qual pecamos.
12 Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
Que ela não seja, oro, como um morto, de quem a carne é meio consumida quando ele sai do ventre de sua mãe”.
13 Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
Moisés gritou a Javé, dizendo: “Cura-a, Deus, eu te imploro”!
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
Yahweh disse a Moisés: “Se seu pai só tivesse cuspido na cara dela, ela não deveria ter vergonha de sete dias? Que ela fique fechada fora do acampamento sete dias, e depois disso ela será trazida novamente”.
15 Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
Miriam foi fechada fora do acampamento por sete dias, e as pessoas não viajaram até que Miriam fosse trazida novamente.
16 Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.
Depois disso, o povo viajou de Hazeroth, e acamparam no deserto de Paran.

< Ƙidaya 12 >