< Ƙidaya 12 >

1 Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
Or Marie et Aaron parlèrent contre Moïse à cause de sa femme l’Éthiopienne,
2 Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
Et dirent: Est-ce par le seul Moïse qu’a parlé le Seigneur? Ne nous a-t-il pas également parlé? Ce qu’ayant entendu le Seigneur,
3 (Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
(Car Moïse était l’homme le plus doux de tous les hommes qui demeuraient sur la terre)
4 Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
Il dit aussitôt à Moïse, à Aaron et à Marie: Sortez, vous trois seulement, pour aller au tabernacle d’alliance. Et lorsqu’ils furent sortis,
5 Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
Le Seigneur descendit dans une colonne de nuée, et se tint à l’entrée du tabernacle, appelant Aaron et Marie. Lorsqu’ils furent venus,
6 sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
Il leur dit: Ecoutez mes paroles: Si quelqu’un parmi vous est prophète du Seigneur, je lui apparaîtrai dans la vision, ou je lui parlerai en songe.
7 Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
Mais tel n’est pas mon serviteur Moïse, qui est très fidèle dans toute ma maison;
8 Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
Car c’est bouche à bouche que je lui parle, et c’est clairement et non en énigmes et en figures qu’il voit le Seigneur. Pourquoi donc n’avez-vous pas craint de décrier mon serviteur Moïse?
9 Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
Et, irrité contre eux, il s’en alla.
10 Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
La nuée aussi qui était sur le tabernacle se retira: et voilà que Marie parut blanche de lèpre comme la neige. Or Aaron l’ayant regardée, et l’ayant vue couverte de lèpre,
11 sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
Dit à Moïse: Je vous conjure, mon seigneur, ne nous imposez point un péché que nous avons commis follement;
12 Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
Que celle-ci ne devienne pas comme morte, et comme l’avorton qui est rejeté du sein de sa mère; voilà que déjà la moitié de sa chair a été dévorée par la lèpre.
13 Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
Moïse donc cria au Seigneur, disant: Dieu, je vous conjure, guérissez-la.
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
Le Seigneur lui répondit: Si son père eût craché sur sa face, n’eût-elle pas dû être au moins pendant sept jours couverte de honte? Qu’elle soit séparée durant sept jours hors du camp, et après cela elle sera rappelée.
15 Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
C’est pourquoi Marie fut exclue du camp durant sept jours; et le peuple ne sortit pas de ce lieu, jusqu’à ce que Marie fut rappelée.
16 Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.
Après cela le peuple partit d’Haséroth, et planta ses tentes dans le désert de Pharan.

< Ƙidaya 12 >