< Ƙidaya 12 >
1 Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
And she spoke Miriam and Aaron against Moses on [the] causes of the woman Cushite whom he had taken for a woman Cushite he had taken.
2 Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
And they said ¿ only only by Moses has he spoken Yahweh ¿ not also by us has he spoken and he heard Yahweh.
3 (Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
And the man Moses ([was] humble *Q(K)*) very more than every person who [was] on [the] surface of the ground.
4 Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
And he said Yahweh suddenly to Moses and to Aaron and to Miriam come out O [the] three of you to [the] tent of meeting and they went out [the] three of them.
5 Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
And he came down Yahweh in a pillar of cloud and he stood [the] entrance of the tent and he summoned Aaron and Miriam and they went out both of them.
6 sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
And he said hear please words my if he is prophet of your Yahweh by vision to him I make myself known by a dream I speak with him.
7 Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
Not thus servant my Moses in all house my [is] faithful he.
8 Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
Mouth to mouth I speak with him and a vision and not by riddles and [the] form of Yahweh he sees and why? not were you afraid to speak against servant my against Moses.
9 Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
And it burned [the] anger of Yahweh on them and he went.
10 Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
And the cloud it departed from over the tent and there! Miriam [was] leprous like snow and he turned Aaron to Miriam and there! leprous.
11 sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
And he said Aaron to Moses pardon me O lord my do not please may put on us [the] sin which we have acted foolishly and which we have sinned.
12 Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
May not please she be like dead [person] whom when came forth he from [the] womb of mother his and it was eaten half of flesh his.
13 Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
And he cried out Moses to Yahweh saying O God please heal please her.
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
And he said Yahweh to Moses and father her certainly he had spat in face her ¿ not will she be put to shame seven days she will be shut up seven days from [the] outside of the camp and after she will be received.
15 Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
And she was shut up Miriam from [the] outside of the camp seven days and the people not it set out until was received Miriam.
16 Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.
And after they set out the people from Hazeroth and they encamped in [the] wilderness of Paran.